< Exodus 33 >

1 And the Lord spoke to Moses, saying: “Go forth, ascend from this place, you and your people, whom you led away from the land of Egypt, into the land that I swore to Abraham, Isaac, and Jacob, saying: To your offspring, I will give it.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka bar wannan wuri, kai da mutanen da ka fito da su daga Masar, ka haura zuwa ƙasar da na alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub cewa, ‘Zan ba zuriyarka.’
2 And I will send an Angel to precede you, so that I may cast out the Canaanite, and the Amorite, and the Hittite, and the Perizzite, and the Hivite, and the Jebusite,
Zan aika da mala’ika a gabanka in kuma kori Kan’aniyawa, Amoriyawa, Hittiyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa.
3 and so that you may enter into a land flowing with milk and honey. For I will not go up with you, since you are a stiff-necked people, lest perhaps I may destroy you on the way.”
Ka haura zuwa ƙasar da take zub da madara da zuma. Amma ba zan tafi tare da ku ba, saboda ku mutane ne masu taurinkai domin mai yiwuwa in hallaka ku a hanya.”
4 And upon hearing this very bad news, the people mourned; and no one put on his finery according to custom.
Da mutane suka ji wannan mugun magana, sai suka fara makoki. Ba kuma wanda ya sa kayan ado.
5 And the Lord said to Moses: “Say to the sons of Israel: You are a stiff-necked people. I should at once go up into your midst and destroy you. Now immediately put aside your ornaments, so that I may know what to do to you.”
Gama Ubangiji ya riga ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Ku mutane ne masu taurinkai. In na yi tafiya da ku ko na ɗan lokaci, mai yiwuwa in hallaka ku. Yanzu sai ku tuɓe kayan adonku, zan kuwa yanke shawara a kan abin da zan yi da ku.’”
6 Therefore, the sons of Israel put aside their ornaments before Mount Horeb.
Saboda haka Isra’ilawa suka tuttuɓe kayan adonsu a Dutsen Horeb.
7 Also, Moses took the tabernacle and pitched it beyond the camp at a distance, and he called its name: ‘Tabernacle of the Covenant.’ And all the people, who had any kind of question, went out to the Tabernacle of the Covenant, beyond the camp.
Musa fa ya saba ɗaukan tenti yă kafa shi a bayan sansani da ɗan nisa, yana kiransa “Tentin Sujada.” Duk wanda yake neman wani abu daga wurin Ubangiji sai yă tafi Tentin Sujada a bayan sansani.
8 And when Moses went out to the tabernacle, all the people rose up, and each one stood at the door of his pavilion, and they beheld the back of Moses until he entered the tent.
A sa’ad da kuma Musa ya fita zuwa Tentin, dukan mutanen sukan tashi su tsaya a ƙofofin tentinsu, suna kallon Musa, sai ya shiga tentin.
9 And when he had gone into the Tabernacle of the Covenant, the pillar of cloud descended and stood at the door, and he spoke with Moses.
Yayinda Musa ya shiga cikin tentin, sai al’amudin girgije yă sauko, yă tsaya a ƙofar yayinda Ubangiji yana magana da Musa.
10 And all discerned that the pillar of cloud stood at the door of the Tabernacle. And they stood and worshipped at the doors of their tents.
Lokacin da mutane suka ga al’amudin girgije a tsaye a ƙofar tentin, sai duk su miƙe tsaye su yi sujada, kowa a ƙofar tentinsa.
11 But the Lord spoke to Moses face to face, just as a man is used to speaking to his friend. And when he returned to the camp, his minister Joshua, the son of Nun, a young man, did not withdraw from the Tabernacle.
Ubangiji yakan yi magana da Musa fuska da fuska, kamar yadda mutum yake magana da abokinsa. Sa’an nan Musa yă koma sansani, amma saurayin nan Yoshuwa ɗan Nun mai taimakonsa ba ya barin tentin.
12 Then Moses said to the Lord: “You instruct me to lead this people away, and you do not reveal to me whom you will send with me, particularly since you have said: ‘I know you by name, and you have found favor before me.’
Musa ya ce wa Ubangiji, “Kana ta faɗa mini cewa, ‘Ka jagoranci mutane nan,’ amma ba ka faɗa mini wanda zai tafi tare da ni ba. Ga shi ka ƙara ce mini, ‘Na san ka, na san sunanka, ka kuma sami tagomashi a wurina.’
13 If, therefore, I have found favor in your sight, show your face to me, so that I may know you and may find grace before your eyes. Look favorably on your people, this nation.”
In ka ji daɗina, ka koya mini hanyarka don in san ka, in kuma ci gaba da samun tagomashi daga gare ka. Ka tuna cewa wannan al’umma mutanenka ne.”
14 And the Lord said, “My face will precede you, and I will give you rest.”
Ubangiji ya amsa ya ce, “Zan tafi tare da kai, zan kuma rage maka nauyin kaya.”
15 And Moses said: “If you will not yourself precede us, then do not lead us away from this place.
Musa kuwa ya ce masa, “In ba za tă tafi tare da mu ba, to, kada ka ɗaga mu daga nan.
16 For how will we be able to know, I and your people, that we have found grace in your sight, unless you walk with us, so that we may be glorified out of all the people who live upon the earth?”
Yaya wani zai sani ko ka ji daɗina da kuma mutanenka, in ba ka tafi tare da mu ba? Mene ne kuma zai bambanta ni da mutanenka daga sauran jama’ar da suke a duniya?”
17 Then the Lord said to Moses: “This word also, which you have spoken, I will do. For you have found grace before me, and I have known you by name.”
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan yi yadda ka faɗa, gama ka sami tagomashi a wurina, na san ka, na kuma san sunanka.”
18 And he said, “Show me your glory.”
Musa kuwa ya ce, “To, ka nuna mini ɗaukakarka.”
19 He responded: “I will show you all that is good, and I will call out with the name of the Lord before you. And I will take pity on whomever I will, and I will be lenient to whomever it will please me.”
Sai Ubangiji ya ce, “Zan wuce a gabanka, Ni Ubangiji zan yi shelar sunana a gabanka. Zan yi alheri ga duk wanda na so in yi masa alheri, zan nuna jinƙai ga duk wanda na so in yi masa jinƙai.
20 And again he said: “You are not able to see my face. For man shall not see me and live.”
Amma ya ce, ba za ka ga fuskata ba, don ba mutumin da zai gan ni yă rayu.”
21 And again, he said: “Behold, there is a place with me, and you shall stand upon the rock.
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ga wani wuri kusa da ni inda za ka tsaya bisa dutsen.
22 And when my glory will cross over, I will set you in a cleft of the rock, and I will protect you with my right hand, until I pass by.
A sa’ad da ɗaukakata tana wucewa, zan sa ka a cikin tsaguwar dutsen, in rufe ka da hannuna har sai na wuce.
23 And I will take away my hand, and you shall see my back. But my face you are not able to see.”
Sa’an nan zan ɗauke hannuna, ka kuwa ga bayana; amma fuskata, ba za ka gani ba.”

< Exodus 33 >