< Judges 21 >

1 The sons of Israel had also taken an oath at Mizpah, and they said, “None of us shall give his daughters as a wife to the sons of Benjamin.”
Mutanen Isra’ila sun riga sun yi rantsuwa a Mizfa cewa, “Ba ɗayanmu da zai ba da’yarsa aure ga mutumin Benyamin.”
2 And they all went to the house of God at Shiloh. And sitting in his sight until evening, they lifted up their voice, and they began to weep, with a great wailing, saying,
Sai mutanen suka tafi Betel, inda suka zauna a gaban Allah har yamma, suna tā da muryoyinsu suna kuka mai zafi.
3 “Why, O Lord, God of Israel, has this evil happened among your people, so that this day one tribe would be taken away from us?”
Suka ce, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, “Me ya sa wannan abu ya faru da Isra’ila? Don me kabila ɗaya daga Isra’ila za tă ɓace a yau?”
4 Then, rising at first light on the next day, they built an altar. And they offered holocausts and victims of peace offerings there, and they said,
Kashegari da sassafe mutane suka gina bagade suka miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.
5 “Who, out of all the tribes of Israel, did not ascend with the army of the Lord?” For they had bound themselves with a great oath, when they were at Mizpah, that whoever was not present would be slain.
Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji ba?” Gama an yi rantsuwa cewa duk wanda ya kāsa zuwa taro a gaban Ubangiji a Mizfa lalle a kashe shi.
6 And the sons of Israel, having been led to repentance over their brother Benjamin, began to say: “One tribe has been taken away from Israel.
To, Isra’ilawa suka yi juyayin’yan’uwansu, mutanen Benyamin. “Yau an hallaka kabila daga cikin Isra’ila.
7 From where shall they receive wives? For we have all sworn in common that we will not give our daughters to them.”
Yaya za mu ba wa waɗanda suka rage mata, da yake mun riga mun yi rantsuwa a gaban Ubangiji, ba za mu ba su ɗaya daga’ya’yanmu su aura ba?”
8 For this reason, they said, “Who is there, out of all the tribes of Israel, that did not ascend to the Lord at Mizpah?” And behold, the inhabitants of Jabesh-Gilead were found not to have been among that army.
Sa’an nan suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji a Mizfa ba?” Sai su gane cewa babu wani daga Yabesh Gileyad da ya zo sansani don taron.
9 (Likewise, in the time when they had been at Shiloh, not one of them was found to be there.)
Gama da aka yi ƙidaya mutane, sai aka gane cewa babu wani daga mutanen Yabesh Gileyad da yake a can.
10 And so they sent ten thousand very robust men, and they instructed them, saying, “Go and strike down the inhabitants of Jabesh-Gilead with the edge of the sword, including their wives and little ones.”
Saboda haka sai taron ya umarci jarumai dubu goma sha biyu su je Yabesh Gileyad su karkashe waɗanda suke zaune a can, duk da mata da yara.
11 And this shall be what you ought to do: “Every one of the male gender, as well as all the women who have known men, shall be put to death. But the virgins you shall reserve.”
Suka ce musu, “Ga abin da za ku yi. Ku karkashe duk namiji da kowace macen da ta riga ta san namiji.”
12 And four hundred virgins, who had not known the bed of a man, were found from Jabesh-Gilead. And they brought them to the camp at Shiloh, in the land of Canaan.
Suka samu a cikin mutanen da suke zaune a Yabesh Gileyad mata ɗari huɗu da ba su taɓa kwana da namiji ba, suka kwashe su zuwa sansani a Shilo a Kan’ana.
13 And they sent messengers to the sons of Benjamin, who were at the rock of Rimmon, and they instructed them, so that they would receive them in peace.
Sa’an nan dukan taro suka aika wa mutanen Benyamin da suke a Dutsen Rimmon cewa yaƙi ya ƙare, yanzu sai salama.
14 And the sons of Benjamin went, at that time, and wives were given to them from the daughters of Jabesh-Gilead. But others were not found, whom they might give in a similar manner.
Saboda haka mutanen Benyamin suka komo a lokacin aka kuma ba su matan Yabesh Gileyad nan da aka bari da rai. Amma matan ba su ishe su duka ba.
15 And all of Israel was very saddened, and they did penance for destroying one tribe out of Israel.
Mutanen kuwa suka yi juyayi saboda mutanen Benyamin, domin Ubangiji ya yi gibi a cikin kabilan Isra’ila.
16 And those greater by birth said: “What shall we do with the remainder, those who have not received wives? For all the females of Benjamin have been cut down,
Shugabannin taron suka ce, “Da matan Benyamin da aka hallaka, yaya za mu yi da mazan da suka ragu da ba su sami mata ba?”
17 and we must take great care, and make provision with a very great diligence, so that one tribe may not be wiped away from Israel.
Suka ce, “Dole mutanen Benyamin da suka ragu su sami gādo, domin kada wata kabila a Isra’ila ta ɓace.
18 As for our own daughters, we are not able to give them, being bound by an oath and a curse, when we said, ‘Accursed is he who will give any of his daughters to Benjamin as a wife.’”
Ba za mu iya ba su’yan matanmu su zama matansu ba, da yake mu Isra’ilawa mun riga mun yi wannan rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne wanda ya ba da’yarsa aure ga mutum Benyamin.’
19 And they took counsel, and they said, “Behold, there is a yearly solemnity of the Lord at Shiloh, which is situated to the north of the city of Bethel, and on the eastern side of the way that one takes from Bethel to Shechem, and to the south of the town of Lebonah.”
Sai suka tuna, akwai bikin Ubangiji da sukan yi shekara-shekara a Shilo ya yi kusa. Shilo yana arewancin Betel, kudu da Lebona, gabas da hanyar da take tsakanin Betel da Shekem.”
20 And they instructed the sons of Benjamin, and they said: “Go, and hide in the vineyards.
Saboda haka suka cewa mutanen Benyamin, “Ku je ku ɓuya a gonakin inabi
21 And when you will have seen daughters of Shiloh being led out to dance, according to custom, go forth suddenly from the vineyards, and let each one seize one wife from among them, and travel into the land of Benjamin.
ku lura. Sa’ad da’yan matan Shilo suka fito waje don su yi rawa, ku fito a guje daga gonakin inabi, kowannenku yă kama wa kansa mata daga cikin’yan matan Shilo, ku tafi ƙasar Benyamin.
22 And when their fathers and brothers arrive, and they begin to complain against you and to argue, we will say to them: ‘Take pity on them. For they have not seized them by right of war or conquest. Instead, begging to receive them, you did not give them, and so the sin was on your part.’”
Sa’ad da iyayensu maza ko’yan’uwansu suka kawo mana ƙara, za mu ce musu, ‘Ku yi mana alheri ku bar su, domin ba mu samo musu mata ba lokacin yaƙi, ku kuma marasa laifi ne, tun da yake ba ku ba da’ya’yan matanku gare su ba.’”
23 And so the sons of Benjamin did just as they had been ordered. And according to their number, they seized for themselves one wife each, out of those who were led out dancing. And they went into their own possession, and they built up their cities, and they lived in them.
Haka mutanen Benyamin suka yi. Yayinda’yan matan suke rawa, kowane mutum ya kama ɗaya ya yi gaba da ita ta zama matarsa. Sa’an nan suka komo ƙasar gādonsu suka sāke giggina garuruwan suka kuwa zauna a cikinsu.
24 The sons of Israel also returned, according to their tribes and families, to their tents.
A lokacin, Isra’ilawa sun bar wurin suka tafi gida zuwa ga kabilansu da zuriyoyinsu, kowane zuwa gādonsa.
25 In those days, there was no king in Israel. Instead, each one did what seemed right to himself.
A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa ya yi abin da ya ga dama.

< Judges 21 >