< Judges 16 >

1 He also went into Gaza. And there he saw a harlot woman, and he entered to her.
Wata rana Samson ya tafi Gaza, inda ya ga wata karuwa. Ya shiga wurinta ya kwana.
2 And when the Philistines had heard of this, and it had become well known among them, that Samson had entered the city, they surrounded him, placing guards at the gate of the city. And there they were keeping watch all night in silence, so that, in the morning, they might kill him as he was going out.
Aka gaya wa mutanen Gaza, “Ai, Samson yana a nan!” Saboda haka suka zo suka kewaye wurin suka yi kwanto dukan dare a bakin ƙofar birni. A daren nan ba su motsa nan da can ba, suna cewa, “Gari yana wayewa za mu kashe shi.”
3 But Samson slept until the middle of the night, and rising up from there, he took both doors from the gate, with their posts and bars. And laying them upon his shoulders, he carried them to the top of the hill that looks toward Hebron.
Amma Samson ya yi kwanciyarsa har tsakiyar dare. Sa’an nan ya tashi ya kama ƙofofin birnin, tare da madogarai biyunsu, ya tumɓuke, ya aza su a kafaɗarsa, ya kai su kan dutsen da yake a fuskantar Hebron.
4 After these things, he loved a woman who was living in the valley of Sorek. And she was called Delilah.
Bayan ɗan lokaci, sai ya shiga ƙaunar wata mace, mai suna Delila a Kwarin Sorek.
5 And the leaders of the Philistines went to her, and they said: “Deceive him, and learn from him wherein lies his great strength, and how we may be able to overcome him and to impose restraints on him. And if you will do this, each one of us will give you one thousand one hundred silver coins.”
Sai shugabannin Filistiyawa suka tafi wurinta suka ce, “Ki yi ƙoƙari ki ga ko za ki rarrashe shi yă nuna miki asirin ƙarfinsa da yadda za mu iya shan ƙarfinsa don mu ɗaura shi mu yi nasara a kansa. Kowannenmu zai ba ki shekel dubu ɗari ɗaya na azurfa.”
6 Therefore, Delilah said to Samson, “Tell me, I beg you, wherein lies your very great strength, and with what might you be bound, so that you could not break free?”
Saboda haka Delila ta ce wa Samson, “Ka faɗa miki asirin ƙarfinka da yadda za a ɗaura ka a yi nasara a kanka.”
7 And Samson answered her, “If I will be bound with seven cords, made of sinews not yet dry, but still damp, I will be weak like other men.”
Samson ya ce mata, “In wani ya ɗaura ni da sababbin igiyoyin da ba su bushe ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
8 And the princes of the Philistines brought to her seven cords, such as he had described. And she bound him with these.
Sa’an nan shugabannin Filistiyawa suka kawo mata sababbin igiyoyi guda bakwai da ba su bushe ba, sai ta daure shi da su.
9 And so, those hiding in ambush with her, in the bedroom, were expecting the end of the matter. And she cried out to him, “The Philistines are upon you, Samson!” And he broke the cords, as one would break a thread of flax, twisted for cutting and singed by fire. And so it was not known wherein lay his strength.
Da mutane a ɓoye a cikin ɗaki tare da ita, sai ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Da jin haka sai ya tsintsinke igiyoyin kamar zaren da ya yi kusa da harshen wuta. Saboda haka asirin ƙarfinsa bai tonu ba.
10 And Delilah said to him: “Behold, you have mocked me, and you have spoken a falsehood. But at least now, tell me with what you may be bound.”
Sa’an nan Delila ta ce wa Samson, “Ka mai da ni wawiya; ka ruɗe ni. Yanzu, ka gaya mini yadda za a daure ka.”
11 And he answered her, “If I will be bound with new cords, which have never been used, I will be weak and like other men.”
Ya ce, “In wani ya ɗaura ni sosai da sababbin igiyoyin da ba a taɓa amfani da su ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
12 Again, Delilah tied him with these, and she cried out, “The Philistines are upon you, Samson!” For an ambush had been prepared in the bedroom. But he broke the bindings like the filaments of a web.
Saboda haka Delila ta ɗauki sababbin igiyoyi ta ɗaura shi da su. Sa’an nan, tare da mutane a ɓoye a ɗakin, ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Amma sai ya tsintsinke su kamar zare.
13 And Delilah spoke to him again: “How long will you deceive me and tell me falsehoods? Reveal with what you ought to be bound.” And Samson responded to her, “If you weave the seven locks of my head with a loom, and if you tie these around a spike and fix it to the ground, I will be weak.”
Sa’an nan Delila ta ce, “Har yanzu, ka mai da shashasha, kana mai da ni wawiya kana kuma yin mini ƙarya. Ka gaya mini yadda za a daure ka mana.” Ya ce mata, “In kin yi kitson gashin kaina guda bakwai kika ɗaura su da zare kika buga su da akwasha, zan rasa ƙarfi in zama kamar kowa.” Saboda haka yayinda yake barci, sai Delila ta yi kitson gashin kansa guda bakwai ta ɗinka su da zare,
14 And when Delilah had done this, she said to him, “The Philistines are upon you, Samson.” And arising from sleep, he withdrew the spike with the hairs and the weaving.
ta kuma ɗaura su da akwasha. Ta sāke yin ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka.” Ya tashi daga barcinsa ya tumɓuke akwashan tare da zaren da aka ɗaura gashin kansa da su.
15 And Delilah said to him: “How can you say that you love me, when your soul is not with me? You have lied to me on three occasions, and you are not willing to reveal wherein lies your very great strength.”
Sa’an nan ta ce masa, “Yaya kake cewa kana sona alhali ba ka yarda da ni ba? Wannan shi ne sau na uku kana mai da ni wawiya kuma ba ka nuna mini asirin ƙarfinka ba.”
16 And when she had been very troublesome to him, and over many days had continually stayed nearby, giving him no time to rest, his soul was faint, and he was weary, even unto death.
Da irin wannan fitina ta tsokane shi kwana da kwanaki har sai da ya gaji kamar zai mutu.
17 Then disclosing the truth of the matter, he said to her: “Iron has never been drawn across my head, for I am a Nazirite, that is, I have been consecrated to God from my mother’s womb. If my head will be shaven, my strength will depart from me, and I will be faint and will be like other men.”
Saboda haka sai ya faɗa mata kome ya ce, “Ba a taɓa sa reza a kaina ba, domin ni Naziri ne keɓaɓɓe ga Allah tun haihuwa. In kuwa an aske kaina, ƙarfina zai rabu da ni, sai in zama kamar kowa.”
18 Then, seeing that he had confessed to her his whole soul, she sent to the leaders of the Philistines and ordered: “Come up just once more. For now he has opened his heart to me.” And they went up, taking with them the money that they had promised.
Da Delila ta gane ya gaya mata kome yanzu, sai ta aika saƙo zuwa ga shugabannin Filistiyawa ta ce, “Ku ƙara zuwa sau ɗayan nan, ai, ya gaya mini kome.” Saboda haka shugabannin Filistiyawa suka dawo tare da azurfa a hannuwansu.
19 But she made him sleep upon her knees, and recline his head upon her bosom. And she called a barber, and he shaved his seven locks of hair. And she began to push him away, and to repel him from herself. For immediately his strength departed from him.
Bayan ta sa shi ya yi barci a cinyarta, sai ta kira wani ya zo ya aske kitso guda bakwai nan a kansa, aka fara rinjayensa. Ƙarfinsa kuwa ya rabu da shi.
20 And she said, “The Philistines are upon you, Samson!” And awaking from sleep, he said in his mind, “I will break away and shake myself free, just as I did before.” For he did not know that the Lord had withdrawn from him.
Sa’an nan ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Sai ya farka daga barci yana tsammani cewa, “Zan fita kamar dā in miƙe jikina.” Amma bai san cewa Ubangiji ya rabu da shi ba.
21 And when the Philistines had seized him, they immediately plucked out his eyes. And they led him, bound in chains, to Gaza. And enclosing him in a prison, they made him work a millstone.
Sa’an nan Filistiyawa suka fizge shi, suka ƙwaƙule idanunsa suka gangara da shi zuwa Gaza. Da suka daure shi da sarƙoƙin tagulla, sai aka sa shi yana niƙa a kurkuku.
22 And now his hair began to grow back.
Amma gashi kansa ya fara tohuwa kuma bayan an aske shi.
23 And the leaders of the Philistines convened as one, so that they might offer great sacrifices to Dagon, their god. And they feasted, saying, “Our god has delivered our enemy, Samson, into our hands.”
To, sai Filistiyawa suka taru don su miƙa hadaya ga Dagon allahnsu su kuma yi biki cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu Samson a hannuwanmu.”
24 Then, too, the people, seeing this, praised their god, and they said the same, “Our god has delivered our adversary into our hands: the one who destroyed our land and who killed very many.”
Sa’ad da mutane suka gan shi, sai suka yabi allahnsu, suna cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu a hannunmu, wanda ya lalace ƙasarmu ya kuma raɓanya kisan mutanenmu.”
25 And rejoicing in their celebration, having now taken food, they instructed that Samson be called, and that he be mocked before them. And having been brought from prison, he was mocked before them. And they caused him to stand between two pillars.
Yayinda suke cikin farin ciki, sai suka yi ihu, suka ce, “Fito mana da Samson yă yi mana wasa.” Saboda haka aka zo da Samson daga kurkuku, shi kuwa ya yi wasa a gabansu. Sa’ad da suka tsai da shi a tsakanin ginshiƙai,
26 And he said to the boy who was guiding his steps, “Permit me to touch the pillars, which support the entire house, and to lean against them, so that I may rest a little.”
sai Samson ya ce wa bawan da ya riƙe hannunsa, “Ka kai ni inda zan taɓa ginshiƙan da suke ɗauke da wannan haikali, don in jingina a kai.”
27 Now the house was full of men and women. And all the leaders of the Philistines were there, as well as about three thousand persons, of both sexes, on the roof and in the upper level of the house, who were watching Samson being mocked.
To, haikalin ya cika da mutane maza da mata; dukan shugabannin Filistiyawa kuwa suna a can, a bisan rufin kuwa akwai mutum wajen dubu uku maza da mata suna kallon Samson yana wasa.
28 Then, calling upon the Lord, he said, “O Lord God remember me, and restore to me now my former strength, O my God, so that I may avenge myself against my enemies, and so that I may receive one vengeance for the deprivation of my two eyes.”
Sa’an nan Samson ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ya Allah ka tuna da ni, ka ƙarfafa ni sau ɗaya nan kaɗai, ka bar ni da bugu ɗaya kawai in ɗauki fansa a kan Filistiyawa domin idanuna.”
29 And taking hold of both the pillars, on which the house rested, and holding one with his right hand and the other with his left,
Sa’an nan Samson ya kai hannuwansa ga ginshiƙan waɗanda haikalin yake a kai, ya jingina jikinsa, hannunsa dama yana a ɗaya, hannun hagu kuma na ɗayan,
30 he said, “May my life die with the Philistines.” And when he had shaken the pillars strongly, the house fell upon all the leaders, and the rest of the multitude who were there. And he killed many more in his death than he had killed before in his life.
Samson ya ce, “Bari in mutu tare da Filistiyawa!” Sa’an nan da dukan ƙarfinsa ya tura haikali ya fāɗa a kan shugabanni da dukan mutanen da suke ciki. Ta haka ya kashe mutane da yawa fiye da yayinda yake da rai.
31 Then his brothers and all his relatives, going down, took his body, and they buried it between Zorah and Eshtaol, in the burying place of his father, Manoah. And he judged Israel for twenty years.
Sa’an nan’yan’uwansa da dukan dangin mahaifinsa suka gangaro don su ɗauke shi. Suka kawo shi suka binne tsakanin Zora da Eshtawol a kabarin Manowa mahaifinsa. Ya yi mulkin Isra’ila shekara ashirin.

< Judges 16 >