< Judges 19 >

1 There was a certain man, a Levite, living beside mount Ephraim, who took a wife from Bethlehem of Judah.
A kwanakin nan Isra’ila ba su da sarki. To, wani Balawe wanda yake zama a wani lungu na ƙasar tudu ta Efraim ya ɗauko wa kansa ƙwarƙwara daga Betlehem cikin Yahuda.
2 She left him, and she returned to the house of her father in Bethlehem. And she stayed with him for four months.
Amma ba tă yi aminci ba. Ta bar shi ta komo gidan mahaifiyarta a Betlehem, a Yahuda. Bayan ta zauna a can wajen wata huɗu,
3 And her husband followed her, wishing to be reconciled with her, and to speak kindly to her, and to lead her back with him. And he had with him a servant and two donkeys. And she received him, and brought him into the house of her father. And when his father-in-law had heard about this, and had seen him, he met him with joy.
sai mijinta ya je wajenta biko don yă rarashe ta komo. Ya tafi tare bawansa da kuma jakuna biyu. Sai ta shigar da shi gidan mahaifinta, sa’ad da mahaifinta ya gan shi, ya marabce shi da murna.
4 And he embraced the man. And the son-in-law stayed in the house of his father-in-law for three days, eating and drinking with him in a friendly manner.
Surukinsa, mahaifin yarinyar, ya sha kansa, yă dakata; saboda haka ya dakata tare da shi har kwana uku, yana ci yana sha, yana kuma kwanciya a can.
5 But on the fourth day, arising in the night, he intended to set out. But his father-in-law took hold of him, and he said to him, “First taste a little bread, and strengthen your stomach, and then you shall set out.”
A rana ta huɗu suka tashi da sassafe ya kuma yi shiri yă tafi, amma mahaifinta yarinyar ya ce wa surukinsa, “Ka ɗan ci wani abu don ka sami ƙarfi; sa’an nan ka tafi.”
6 And they sat down together, and they ate and drank. And the father of the young woman said to his son-in-law, “I ask you to remain here today, so that we may rejoice together.”
Saboda haka suka zauna su biyu suka ci suka sha tare. Bayan haka sai mahaifin yarinyar ya ce, “Don Allah ka kwana ka ji wa kanka daɗi.”
7 But getting up, he intended to begin to set out. But nevertheless, his father-in-law pressed him resolutely, and made him remain with him.
Sa’ad da mutumin ya tashi zai tafi, sai surukinsa ya roƙe shi, saboda haka ya kwana a wannan dare.
8 But when morning came, the Levite was preparing for his journey. And his father-in-law said to him again, “I beg you to take a little food, and to be strengthened, until the daylight increases, and after that, you shall set out.” Therefore, they ate together.
Da sassafen kashegari rana ta biyar, ya tashi zai tafi, sai mahaifin yarinyar ya ce, “Ka ɗan zauna ka shaƙata sai rana ta yi sanyi mana!” Saboda haka su biyu suka zauna suka ci abinci tare.
9 And the young man got up, so that he might travel with his wife and servant. And his father-in-law spoke to him again: “Consider that the daylight is declining, and it approaches toward evening. Remain with me also today, and spend the day in gladness. And tomorrow you shall set out, so that you may go to your own house.”
Sa’ad da mutumin da ƙwarƙwaransa da bawansa, suka tashi don su tafi, surukinsa, mahaifin yarinyar ya ce, “Duba, rana ta kusan fāɗuwa, yamma ta riga ta yi, ka kwana a nan. Ka sāke kwana ka ji wa ranka daɗi. Kashegari da sassafe za ka iya tashi ka kama hanyarka zuwa gida.”
10 His son-in-law was not willing to agree to his words. Instead, he immediately continued on, and he arrived opposite Jebus, which by another name is called Jerusalem, leading with him two donkeys carrying burdens, and his mate.
Amma bai so ya sāke kwana a can ba, mutumin ya tashi ya tafi ya bi ta Yebus (wato, Urushalima), tare da jakunansa biyu da aka yi musu shimfiɗa da kuma ƙwarƙwaransa.
11 And now they were near Jebus, but day was turning into night. And the servant said to his lord, “Come, I beg you, let us turn aside to the city of the Jebusites, so that we may find lodging in it.”
Sa’ad da suka yi kusa da Yebus dare kuma ya riga ya yi, bawan ya ce wa maigidansa, “Mu dakata a birnin nan na Yebusiyawa mu kwana.”
12 His lord responded to him: “I will not enter into the town of a foreign people, who are not of the sons of Israel. Instead, I will cross over as far as Gibeah.
Maigidansa ya ce, “A’a. Ba za mu shiga birnin baƙi waɗanda mutanensu ba Isra’ilawa ba. Za mu ci gaba zuwa Gibeya.”
13 And when I will have arrived there, we will lodge in that place, or at least in the city of Ramah.”
Ya kuma ce, “Zo, mu yi ƙoƙari mu kai Gibeya ko Rama mu kwana a ɗaya cikinsu.”
14 Therefore, they passed by Jebus, and continuing on, they undertook the journey. But the sun went down on them when they were near Gibeah, which is of the tribe of Benjamin.
Saboda haka suka ci gaba, rana tana fāɗuwa sa’ad da suka yi kusa da Gibeya a Benyamin.
15 And so they diverted to it, so that they might lodge there. And when they had entered, they were sitting in the street of the city. For no one was willing to give them hospitality.
A can suka dakata don su kwana, suka tafi suka zauna a dandali birnin, amma wani ya shigar da su gidansa da daren.
16 And behold, they saw an old man, returning from the field and from his work in the evening, and he was also from mount Ephraim, and he was living as a stranger in Gibeah. For the men of that region were of the sons of Benjamin.
A wannan yamma sai ga wani tsoho daga ƙasar tudu ta Efraim, wanda yake zama a Gibeya (mutane wurin kuwa mutanen Benyamin ne), ya shigo daga wurin aiki a gonaki.
17 And the old man, lifting up his eyes, saw the man sitting with his bundles in the street of the city. And he said to him: “Where have you come from? And where are you going?”
Sa’ad da ya duba ya ga matafiyin a dandalin birnin, sai tsohon ya yi tambaya ya ce, “Ina za ku? Ina kuka fito?”
18 He answered him: “We set out from Bethlehem of Judah, and we are traveling to our own place, which is beside mount Ephraim. From there we went to Bethlehem, and now we go to the house of God. But no one is willing to receive us under his roof.
Balawen ya ce, “Muna fito daga Betlehem a Yahuda za mu wani lungu a ƙasar tudu ta Efraim inda nake da zama. Na tafi Betlehem a Yahuda, ga shi kuwa yanzu za ni gidan Ubangiji. Ba wanda ya shigar da ni gidansa.
19 We have straw and hay as fodder for the donkeys, and we have bread and wine for the use of myself, and for your handmaid and the servant who is with me. We lack nothing except lodging.”
Muna da ƙara da abinci don jakunanmu, muna kuma da burodi da ruwan inabi dominmu da bayinka, ni, baiwarka da kuma saurayin nan tare da mu. Ba ma bukatar kome.”
20 And the old man responded to him: “Peace be with you. I will provide all that is necessary. Only, I beg you, do not stay in the street.”
Tsohon ya ce, “Na marabce ku a gidana. Bari ni ba ku duk abin da kuke bukata. Kada ku dai kwana a dandali.”
21 And he led him into his house, and he gave fodder to his donkeys. And after they had washed their feet, he received them with a banquet.
Saboda haka sai kai shi zuwa gidansa ya ciyar da jakunansa. Bayan sun wanke ƙafafunsu, sai aka ba su abinci da abin sha.
22 And while they were feasting, and were refreshing their bodies with food and drink after the labor of the journey, the men of that city, sons of Belial (that is, without yoke), came and surrounded the old man’s house. And they began to knock at the door, calling out to the lord of the house, and saying, “Bring out the man who entered your house, so that we may abuse him.”
Yayinda suke jin wa kansu daɗi, sai waɗansu’yan iska daga birnin suka kewaye gidan. Suna bubbuga ƙofar, suna kira tsohon da yake da gidan suna cewa, “Ka fito mana da mutumin nan a gidanka domin mu yi jima’i da shi.”
23 And the old man went out to them, and he said: “Do not choose, brothers, do not choose to do this evil. For this man has entered to my hospitality. And you must cease from this senselessness.
Maigidan ya fita waje ya ce musu, “A’a, abokaina, kada ku yi abin kunyan nan. Da yake mutumin nan baƙona ne, kada ku yi rashin kunyan nan.
24 I have a virgin daughter, and this man has a mate. I will lead them out to you, so that you may debase them and may satisfy your lust. Only, I beg you, do not commit this crime against nature on the man.”
Duba, ga’yata da ba tă taɓa sanin namiji ba da kuma ƙwarƙwaransa. Zan fito muku da su a waje yanzu, za ku kuwa iya yin ko mene ne da kuke so da su. Amma wannan mutum, kada ku yi abin kunya.”
25 But they were not willing to agree to his words. So the man, discerning this, led out his mate to them, and he delivered her to their sexual abuse. And when they had abused her for the entire night, they released her in the morning.
Amma mutanen ba su saurare shi ba. Saboda haka mutumin ya ba da ƙwarƙwaransa, suka yi mata fyaɗe suka yi lalata da ita dukan dare, gari yana wayewa sai suka bar ta.
26 But the woman, as darkness was receding, came to the door of the house, where her lord was staying, and there she fell down.
Da safe matar ta koma gidan da maigidanta yake, ta fāɗi a ƙofa ta kwanta a can har rana ta yi.
27 When morning came, the man arose, and he opened the door, so that he might complete the journey that he had begun. And behold, his mate was lying before the door, with her hands reaching out to the threshold.
Sa’ad da maigidanta ya tashi da safe ya buɗe ƙofar gidan don yă fita ya ci gaba da tafiyarsa, sai ga ƙwarƙwararsa, ta fāɗi a bakin ƙofar gidan da hannuwanta a madogarar ƙofar.
28 And he, thinking that she was resting, said to her, “Get up, and let us walk.” But since she gave no response, realizing that she had died, he took her up, and he laid her on his donkey, and he returned to his house.
Ya ce mata, “Tashi; mu tafi.” Amma ba amsa. Sai ya sa ta a kan jakinsa ya kama hanyar gida.
29 And when he had arrived, he took up a sword, and he cut into pieces the dead body of his wife, with her bones, into twelve parts. And he sent the pieces into all the parts of Israel.
Da ya kai gida, sai ya ɗauki wuƙa ya yayyanka ƙwarƙwaransa gunduwa-gunduwa, kashi goma sha biyu ya aika da su a ko’ina a Isra’ila.
30 And when each one had seen this, they were crying out together, “Never has such a thing been done in Israel, from the day that our fathers ascended from Egypt, even to the present time. Let a sentence be brought and let us decide in common what ought to be done.”
Duk wanda ya gani, sai ya ce, “Ba a taɓa gani ko yin irin wannan abu ba, tun lokacin da Isra’ilawa suka fito daga Masar. Ku yi tunani wannan! Ku kuma yi la’akari! Ku gaya mana abin da za mu yi!”

< Judges 19 >