< Jeremiah 31 >

1 “In that time, says the Lord, I will be the God of all the families of Israel, and they will be my people.”
“A lokacin nan, zan zama Allah na dukan kabilan Isra’ila, za su kuma zama mutanena,” in ji Ubangiji.
2 Thus says the Lord: “The people who had remained after the sword, found grace in the desert. Israel will go to his rest.”
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Mutanen da suka tsere wa takobi za su sami tagomashi a hamada; zan zo don in ba da hutu ga Isra’ila.”
3 The Lord appeared to me from a distance: “And I have loved you in perpetual charity. Therefore, showing pity, I have drawn you.
Ubangiji ya bayyana mana a dā, yana cewa, “Na ƙaunace ku da madawwamiyar ƙauna; na janye ku da ƙauna marar iyaka.
4 And I will build you up again. And you shall be built up, O virgin of Israel. Still shall you be adorned with your timbrels, and still shall you go forth to the singing of those who play.
Zan sāke gina ki za ki kuwa sāke ginuwa, ya Budurwar Isra’ila. Za ki kuma ɗauki ganganki ki fita don ki yi rawa da masu farin ciki.
5 Still shall you plant vineyards on the mountains of Samaria. The planters will plant, and they will not gather the vintage until the time arrives.
Za ki sāke dasa gonakin inabi a kan tussan Samariya; manoma za su yi shuka a kansu su kuma ji daɗin amfaninsu.
6 For there will be a day on which the guardians on mount Ephraim will cry out: ‘Arise! And let us ascend on Zion to the Lord our God!’”
Za a yi ranar da matsara za su tā da murya a kan tuddan Efraim su ce, ‘Ku zo, bari mu haura Sihiyona, zuwa wurin Ubangiji Allahnmu.’”
7 For thus says the Lord: “Exult in the joy of Jacob, and neigh before the head of the Gentiles. Shout, and sing, and say: ‘O Lord, save your people, the remnant of Israel!’
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku rera don farin ciki wa Yaƙub; ku yi sowa don al’ummai da suke nesa. Ka sa a ji yabanku, ku kuma ce, ‘Ya Ubangiji ka ceci mutanenka, raguwar Isra’ila.’
8 Behold, I will lead them from the land of the north, and I will gather them from the ends of the earth. Among them will be the blind and the lame, she who is with child, together with she who is giving birth: a great assembly returning to this place.
Ga shi, zan kawo su daga ƙasar arewa in tattara su daga iyakar duniya. A cikinsu makafi da guragu za su kasance, mata masu ciki da matan da suke naƙuda; jama’a mai yawan gaske za su komo.
9 They will approach with weeping. And I will lead them back with mercy. And I will lead them through the torrents of water, by an upright way, and they will not stumble in it. For I have become Father to Israel, and Ephraim is my firstborn.”
Za su zo da kuka; za su yi addu’a yayinda nake komo da su. Zan bishe su kusa da rafuffukan ruwa a miƙaƙƙiyar hanya inda ba za su yi tuntuɓe ba, domin ni ne mahaifin Isra’ila, Efraim kuma ɗan farina ne.
10 Listen to the word of the Lord, O Gentiles, and announce it amid the islands that are far away, and say: “Whoever has scattered Israel will gather him, and he will guard him as a shepherd guards his flock.”
“Ku ji maganar Ubangiji, ya al’ummai; ku yi shelarta a gaban teku masu nesa cewa, ‘Shi wanda ya watsar da Isra’ila zai tattara su zai kuma lura da garkensa kamar makiyayi.’
11 For the Lord has redeemed Jacob, and he has freed him from the hand of one more powerful.
Gama Ubangiji zai fanshi Yaƙub zai cece su daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
12 And they will arrive and give praise on Mount Zion. And they will flow together, to the good things of the Lord, over grain, and wine, and oil, and the offspring of cattle and herds. And their soul will be like an irrigated garden, and they will no longer be hungry.
Za su zo su yi sowa don farin ciki a ƙwanƙolin Sihiyona; za su yi farin ciki cikin yalwar Ubangiji hatsi, sabon ruwan inabi da mai,’ya’yan garken tumaki da na shanu. Za su zama kamar gonar da aka yi wa banruwa, ba za su ƙara yin baƙin ciki ba.
13 Then the virgin will rejoice with singing, the young and the old together, and I will turn their mourning into gladness, and I will console them and gladden them after their sorrow.
’Yan mata za su yi rawa su kuma yi murna, haka ma samari da tsofaffi. Zan mai da makokinsu farin ciki; zan ta’azantar da su in kuma sa su yi farin ciki a maimakon baƙin ciki.
14 And I will inebriate the soul of the priests with fatness, and my people will be filled with my good things, says the Lord.”
Zan ƙosar da firistoci da yalwa, mutanena kuma za su cika da yalwa,” in ji Ubangiji.
15 Thus says the Lord: “A voice has been heard on high: of lamentation, mourning, and weeping; of Rachel crying for her sons and refusing to be consoled over them, because they are not.”
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “An ji murya daga Rama, makoki da kuka mai zafi, Rahila tana kuka domin’ya’yanta ta kuma ƙi a ta’azantar da ita domin’ya’yanta ba su.”
16 Thus says the Lord: “Let your voice cease from crying and your eyes from tears. For there is a reward for your work, says the Lord. And they will return from the land of the enemy.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Hana muryarki kuka da kuma idanunki hawaye, gama za a sāka wa aikinki,” in ji Ubangiji. “Za su komo daga ƙasar abokin gāba.
17 And there is hope for your very end, says the Lord. And the sons will return to their own borders.
Saboda haka akwai sa zuciya domin nan gaba,” in ji Ubangiji. “’Ya’yanki za su komo ƙasarsu.
18 Listening, I heard Ephraim going into captivity: ‘You have chastised me, and I was instructed, like a young untamed bull. Convert me, and I shall be converted. For you are the Lord my God.
“Tabbatacce na ji gurnanin Efraim yana cewa, ‘Ka hore ni kamar ɗan maraƙi mai ƙin ji, na kuwa horu. Ka mayar da ni, zan kuwa dawo, domin kai ne Ubangiji Allahna.
19 For after you converted me, I did penance. And after you revealed to me, I struck my thigh. I am confounded and ashamed. For I have endured the disgrace of my youth.’
Bayan na kauce, sai na tuba; bayan na gane, sai na sunkuyar da kaina. Na ji kunya da ƙasƙanci domin ina ɗauke da kunyar ƙuruciyata.’
20 Certainly, Ephraim is an honorable son to me; surely, he is a tender child. For I will still remember him, as in the time when I first spoke about him. Because my heart is stirred up over him, surely I will take pity on him, says the Lord.
Efraim ba ƙaunataccen ɗana ba ne, ɗan da nake jin daɗinsa? Ko da yake sau da dama ina maganar gāba a kansa, duk da haka nakan tuna da shi. Saboda haka zuciyata tana marmarinsa; ina da jinƙai mai girma dominsa,” in ji Ubangiji.
21 Establish a watchtower for yourself. Place yourself in bitterness. Direct your heart into the upright way, in which you used to walk. Return, return, O virgin of Israel, to these your cities!
“Ki kafa alamun hanya; ki sa shaidun bishewa. Ki lura da babbar hanya da kyau, hanyar da kika bi. Ki komo, ya Budurwar Isra’ila, ki komo zuwa garuruwanki.
22 How long will you be absorbed in delights, O wandering daughter? For the Lord has created something new upon the earth: a woman will encompass a man.”
Har yaushe za ki yi ta yawo, Ya’ya marar aminci? Ubangiji zai ƙirƙiro sabon abu a duniya mace za tă kewaye namiji.”
23 Thus says the Lord of hosts, the God of Israel: “Still they will speak this word in the land of Judah, and in its cities, when I will convert their captivity: ‘May the Lord bless you, the beauty of justice, the holy mountain.’
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Sa’ad da na komo da su daga bauta mutane a ƙasar Yahuda da cikin garuruwanta za su sāke yi amfani da waɗannan kalmomi. ‘Ubangiji ya albarkace ka, ya mazauni mai adalci, ya tsarkakan dutse.’
24 And they will live in it: Judah together with all its cities, the farmer and those who drive the flocks.
Mutane za su zauna tare a Yahuda da dukan garuruwansa, manoma da waɗanda suke yawo da garkunansu.
25 For I have inebriated the weary soul, and I have satisfied every hungry soul.
Zan wartsake waɗanda suka gaji in kuma ƙosar da waɗanda ransu ya yi yaushi.”
26 Over this, I was awakened, as if from a deep sleep. And I saw, and my sleep became sweet to me.
A kan wannan na farka na duba kewaye. Barcina ya yi mini daɗi.
27 Behold, the days are approaching, says the Lord, when I will sow the house of Israel and the house of Judah with the offspring of men and with the offspring of cattle.
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan kafa gidan Isra’ila da gidan Yahuda da’ya’yan mutane da na dabbobi.
28 And just as I have watched over them, so that I may root up, and tear down, and scatter, and destroy, and afflict, so will I watch over them, so that I may build and plant them, says the Lord.
Kamar yadda na lura da su don su tumɓuke su kuma rusar, su lalatar, su hallaka su kuma kawo masifa, haka zan lura da su don su gina su kuma dasa,” in ji Ubangiji.
29 In those days, they will no longer say: ‘The fathers ate a bitter grape, and the teeth of the sons have been affected.’
“A waɗannan kwanaki mutane ba za su ƙara ce, “‘Ubanni suka ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya suka mutu ba.’
30 Instead, each one will die for his own iniquity. Each man who will have eaten a bitter grape, his own teeth will be affected.
A maimako, kowa zai mutu saboda zunubinsa; duk wanda ya ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoransa ne za su mutu.
31 Behold, the days are approaching, says the Lord, when I will form a new covenant with the house of Israel and with the house of Judah,
“Lokaci yana zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi sabon alkawari da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
32 not according to the covenant which I made with their fathers, in the day when I took them by the hand, so as to lead them away from the land of Egypt, the covenant which they nullified, though I was the ruler over them, says the Lord.
Ba zai zama kamar alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu ba sa’ad da na kama su da hannu na bishe su daga Masar, domin sun take alkawarina, ko da yake na zama miji a gare su,” in ji Ubangiji.
33 But this will be the covenant that I will form with the house of Israel, after those days, says the Lord: I will give my law to their inner most being, and I will write it upon their heart. And I will be their God, and they shall be my people.
“Ga alkawarin da zan yi da gidan Isra’ila bayan wannan lokaci,” in ji Ubangiji. “Zan sa dokata a tunaninsu in kuma rubuta ta a zukatansu. Zan zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
34 And they will no longer teach, a man his neighbor, and a man his brother, saying: ‘Know the Lord.’ For all will know me, from the littlest of them even to the greatest, says the Lord. For I will forgive their iniquity, and I will no longer remember their sin.
Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabci ba, ko ya koya wa ɗan’uwansa cewa, ‘Ka san Ubangiji,’ domin duk za su san ni, daga ƙaraminsu har zuwa babba,” in ji Ubangiji. “Gama zan gafarta muguntarsu ba zan kuwa ƙara tuna da zunubansu ba.”
35 Thus says the Lord, who gives the sun as the light of the day, who puts the moon and the stars in order as the light of the night, who stirs up the sea and makes its waves roar: the Lord of hosts is his name.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya kafa rana don tă yi haske a yini shi da ya sa wata da taurari su yi haske da dare, shi da yake dama teku don raƙuman ruwansa su yi ruri Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
36 If these laws fail in my sight, says the Lord, then the offspring of Israel will also fail, so that they will not be a people in my sight for all time.”
“In dai wannan kafaffiyar ƙa’ida ta daina aiki a gabana,” in ji Ubangiji, “to, sai zuriyar Isra’ila ta daina zama al’umma a gabana.”
37 Thus says the Lord: “If the heavens above are able to be measured, and if the foundations of the earth beneath can be examined, I also will cast aside all the offspring of Israel, because of all that they have done, says the Lord.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In a iya auna sammai a kuma bincike tushen duniya a ƙarƙas to, sai in ƙi dukan zuriyar Isra’ila ke nan saboda dukan abin da suka yi,” in ji Ubangiji.
38 Behold, the days are approaching, says the Lord, when a city will be built for the Lord from the tower of Hananel, even to the Gate of the Corner;
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da za a sāke gina wannan birni domina daga Hasumiyar Hananel zuwa Ƙofar Kusurwa.
39 and the measuring line will go on even further in his sight, over the hill of Gareb, and it will encircle Goah
Ma’auni zai miƙe daga can ya nausa kai tsaye zuwa tudun Gareb sa’an nan ya juya zuwa Gowa.
40 and the entire Valley of dead bodies and ashes, and the entire region of death, even to the torrent of Kedron, and to the corner of the Horse Gate to the east. All this will be the holy place of the Lord. It will not be rooted up, and it will not be torn down, anymore, forever.”
Dukan kwarin da ake zubar da toka da kuma gawawwaki, da dukan lambatun da suke can har zuwa Kwarin Kidron a gabas zuwa kusurwar Ƙofar Doki, za su zama mai tsarki ga Ubangiji. Ba za a ƙara tumɓuke birnin ko a rushe shi ba.”

< Jeremiah 31 >