< Jeremiah 30 >

1 This is the word that came to Jeremiah from the Lord, saying:
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
2 “Thus says the Lord, the God of Israel, saying: You shall write in a book all the words that I have spoken to you.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ka rubuta a cikin littafi dukan maganganun da na yi maka.
3 For behold, the days are approaching, says the Lord, when I will convert the turning away of my people, Israel and Judah, says the Lord. And I will return them to the land which I gave to their fathers, and they will possess it.”
Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan komo da mutanena Isra’ila da Yahuda daga bauta in kuma maido da su ga ƙasar da na ba wa kakanninsu mallaka,’ in ji Ubangiji.”
4 And these are the words which the Lord has spoken to Israel and to Judah:
Ga kalmomin Ubangiji da ya yi game da Isra’ila da Yahuda,
5 For thus says the Lord: ‘We have heard a voice of terror. There is dread, and there is no peace.’
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ana jin kukan tsoro, razana, ba salama ba.
6 Inquire and see, does a male give birth? Then why have I seen every man with his hand on his lower back, like a woman bearing a child? And why have all of their faces turned pale?
Ku tambaya ku ji. Namiji zai iya haifi’ya’ya? To, me ya sa kuke ganin kowane mai ƙarfi da hannuwansa a kwankwaso kamar mace mai naƙuda, kowace fuska ta koma fari?
7 Woe! For that day is great, and there is nothing like it. For it is the time of tribulation for Jacob, but he will be saved from it.
Kaito, gama wannan rana za tă zama mai girma! Babu kamar ta. Zai zama lokacin wahala wa Yaƙub, amma za a cece shi daga cikinta.
8 And this shall be in that day, says the Lord of hosts: I will crush his yoke from your neck, and I will break open his bands. And strangers will no longer rule over him.
“‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan karya karkiya daga wuyansu zan kuma cire musu kangi; baƙi ba za su ƙara bautar da su ba.
9 Instead, they will serve the Lord their God, and David their king, whom I will raise up for them.
A maimakon haka, za su bauta wa Ubangiji Allahnsu Dawuda sarkinsu kuwa, wanda na tayar musu.
10 Therefore, O my servant Jacob, you should not be afraid, says the Lord, and you should not be frightened, O Israel. For behold, I will save you from a far away land, and your offspring from the land of their captivity. And Jacob will return and have rest, and he shall flow with every good thing. And there will be no one for him to dread.
“‘Saboda haka kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila,’ in ji Ubangiji. ‘Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nesa, zuriyarka daga ƙasar zaman bautansu. Yaƙub zai sami salama da zaman lafiya, kuma ba wanda zai sa ya ji tsoro.
11 For I am with you, says the Lord, so that I may save you. For I will bring about the consummation of all the nations, among which I have scattered you. But I will not bring about your consummation. Instead, I will chastise you in judgment, so that you will not seem innocent to yourself.”
Ina tare da kai zan kuma cece ka,’ in ji Ubangiji. ‘Ko da yake na hallakar da dukan al’umma gaba ɗaya a inda na warwatsa ku, ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba. Zan hore ku amma da adalci kaɗai; ba zan ƙyale ku ku tafi gaba ɗaya ba hukunci ba.’
12 For thus says the Lord: “Your fracture is incurable; your wound is very serious.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Mikinku marar warkewa ne, raunin da kuka ji ya sha ƙarfin warkarwa.
13 There is no one who may judge your judgment, so as to bandage it; there is no useful treatment for you.
Babu wanda zai yi roƙo saboda damuwarku, ba magani domin mikinku babu warkarwa dominku.
14 All your lovers have forgotten you, and they will not seek you. For I have wounded you with the strike of an enemy, with a cruel chastisement. Your sins have become hardened because of the multitude of your iniquities.
Dukan abokanku sun manta da ku; ba su ƙara kulawa da ku. Na buge ku kamar yadda abokin gāba zai yi na kuma hukunta ku yadda mai mugunta zai yi, domin laifinku da girma yake zunubanku kuma da yawa suke.
15 Why do you cry out over your affliction? Your pain is incurable. I have done these things to you because of the multitude of your iniquity and because of your hardened sins.
Me ya sa kuke kuka a kan mikinku, wahalarku da ba ta da magani? Domin laifinku da girma yake da kuma zunubanku masu yawa na yi muku waɗannan abubuwa.
16 Because of this, all those who devour you, will be devoured. And all your enemies will be led into captivity. And those who devastate you, will be devastated. And all those who prey upon you, I will offer as a prey.
“‘Amma duk wanda ya cinye ku za a cinye shi; dukan abokan gābanku za su tafi zaman bauta. Waɗanda suka washe ku su ma za a washe su; dukan waɗanda suka mai da ku ganima su ma zan mai da su ganima.
17 For I will close up your scar, and I will heal you of your wounds, says the Lord. For they have called you an outcast, O Zion: ‘This is she who has no one asking for her.’”
Amma zan mayar muku da lafiya in kuma warkar da mikinku,’ in ji Ubangiji, ‘domin ana ce da ku yasassu, Sihiyona wadda ba wanda ya kula da ita.’
18 Thus says the Lord: “Behold, I will turn back the turning away of the tabernacles of Jacob, and I will take pity on his roofs. And the city will be built up in her heights, and the temple will be founded according to its order.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Zan mayar da wadatar tentin Yaƙub in kuma ji tausayin wuraren zamansa; za a sāke gina birnin a kufansa, fadar kuwa za tă tsaya a wurin da ya dace da ita.
19 And praise will go forth from them, with the voice of those who play. And I will multiply them, and they will not be lessened. And I will glorify them, and they will not be weakened.
Daga gare su waƙoƙi za su fito na godiya da kuma sowa ta farin ciki. Zan riɓaɓɓanya su, ba za su kuwa ragu ba; zan kawo musu ɗaukaka, ba kuwa za a ƙasƙanta su ba.
20 And their sons will be as in the beginning. And their assembly will remain in my sight. And I will visit against all those who trouble them.
’Ya’yansu za su kasance kamar a kwanakin dā jama’arsu kuma za su kahu a gabana; zan hukunta duk wanda ya zalunce su.
21 And their ruler will be one of their own. And their prince will be led forward from their midst. And I will draw him near, and he will cling to me. For who is the one who applies his heart, so that he may draw near to me, says the Lord?
Shugabansu zai zama ɗaya daga cikinsu; mai mulkinsu zai taso daga cikinsu. Zan kawo shi kusa zai kuma zo kusa da ni, gama wane ne zai miƙa kansa don yă yi kusa da ni?’ In ji Ubangiji.
22 And you shall be my people, and I will be your God.”
‘Saboda haka za ku zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnku.’”
23 Behold the whirlwind of the Lord, his fury going forth, a destroying storm! It will rest upon the head of the impious.
Ga shi, hadarin Ubangiji zai fasu cikin hasala, iskar guguwa mai hurawa a kan kawunan mugaye.
24 The Lord will not turn back the wrath of his indignation, until he has accomplished and completed the plan of his heart. In the last days, you shall understand these things.
Fushi mai zafi na Ubangiji ba zai kawu ba sai ya cika manufofin zuciyarsa gaba ɗaya. A kwanaki masu zuwa za ku gane wannan.

< Jeremiah 30 >