< Lamentations 1 >

1 ALEPH. O how a city once filled with people now sits alone! The Governess of the Gentiles has become like a widow. The Prince of the provinces has been placed under tribute.
Yanzu birnin ya zama babu kowa a ciki, birnin da a dā yake cike da mutane! Yanzu birnin ya zama kamar gwauruwa, wadda a dā babba ce ita a cikin ƙasashe! Ita da take sarauniya a cikin larduna yanzu ta zama baiwa.
2 BETH. Weeping, she has wept through the night, and her tears are on her cheeks. There is no one to be a comfort to her and to all her beloved. All her friends have spurned her, and they have become her enemies.
Tana yin kuka mai zafi da dare, hawaye na gangara a kan kumatunta. A cikin masoyanta duka babu wanda ya yi mata ta’aziyya. Duk abokanta sun yashe ta; sun zama abokan gābanta.
3 GHIMEL. Judah has migrated because of affliction and great servitude. She has lived among the nations and not found rest. All of her persecutors have apprehended her, amid torments.
Bayan wahala da baƙin ciki, Yahuda ta tafi bauta. Ta zauna a cikin ƙasashe, ba tă samu wurin hutawa ba. Duk masu fafararta sun same ta sa’ad da take cikin matuƙar ɓacin rai.
4 DALETH. The pathways of Zion mourn, because there are none who approach for the solemnity. All her gates are destroyed. Her priests groan. Her virgins are filthy. And she is overwhelmed with bitterness.
Hanyoyin zuwa Sihiyona suna makoki, gama ba wanda ya zo bikin da ta shirya. Ba kowa a hanyoyin shiganta. Firistocinta suna gurnani,’yan matana kuma suna wahala, kuma tana cikin shan wahala ƙwarai.
5 HE. Her enemies have been made her leaders; her adversaries have been enriched. For the Lord has spoken against her, because of the multitude of her iniquities. Her little ones have been led into captivity before the face of the tribulator.
Maƙiyanta sun zama shugabanninta; Abokan gābanta suna da kwanciyar rai. Ubangiji ya kawo mata ɓacin rai domin yawan zunubanta.’Ya’yanta sun tafi bauta, a ƙarƙashin maƙiyanta.
6 VAU. And all her elegance has departed, from the daughter of Zion. Her leaders have become like rams that cannot find pasture, and they have gone away without strength before the face of the pursuer.
Diyar Sihiyona ba ta da sauran daraja.’Ya’yan sarakunanta sun zama kamar bareyi waɗanda suka rasa wurin kiwo; cikin rashin ƙarfi suka guje wa masu fafararsu.
7 ZAIN. Jerusalem has remembered the days of her affliction and the betrayal of all her desirable ones, whom she held from the days of antiquity, when her people fell into the hand of the enemy, and there was no one to be a helper. The enemies have looked upon her and mocked her Sabbaths.
A cikin kwanakin da take shan wahala take kuma yawo Urushalima ta tuna da dukan dukiyar da take da ita a kwanakin dā can. Sa’ad da mutanenta suka faɗa cikin hannun abokan gābanta, ba wanda ya taimake ta. Maƙiyanta suka dube ta suka yi mata dariya don hallakar da ta auko mata.
8 HETH. Jerusalem has sinned a grievous sinz. Because of this, she has become unstable. All who glorified her have spurned her, because they have looked upon her disgrace. Then she groaned and turned away again.
Urushalima ta yi zunubi ƙwarai saboda haka ta zama marar tsarki. Dukan masu martaba ta sun raina ta, gama sun ga tsiraicinta; ita ma da kanta tana nishi da ƙyar ta kuma juya baya.
9 TETH. Her filth is on her feet, and her end has not been remembered. She has been vehemently put down, having no consolation. O Lord, look upon my affliction, for the adversary has been lifted up.
Ƙazantarta ta manne wa rigunanta; ba tă kula da nan gaba ba, fāɗuwarta kuwa babban abu ne; babu wanda zai yi mata ta’aziyya. “Duba, ya Ubangiji, ka ga wahalata, gama maƙiyi ya yi nasara.”
10 JOD. The enemy has sent his hand against all her desirable ones. For she has watched the Gentiles enter her sanctuary, even though you instructed that they should not enter into your church.
Maƙiya ya kwashe dukiyarta duka; ta ga mutanen da ba su san Allah ba sun shiga wuri mai tsarkinta waɗanda ka hana su shiga taron jama’arka.
11 CAPH. All her people are groaning and seeking bread. They have given up whatever was precious in exchange for food, so as to remain alive. See, O Lord, and consider, for I have become vile.
Dukan mutanenta suna nishi da ƙyar suna neman burodi; sun sayar da dukiyarsu don su samu abinci don kada su mutu da yunwa. “Ubangiji, ka duba ka gani, gama an yashe ni.”
12 LAMED. O all you who pass by the way, attend, and see if there is any sorrow like my sorrow. For he has made me a vintage, just as the Lord has spoken in the day of his furious anger.
“Ko wannan ba wani abu ba ne a wurinku, dukanku masu wucewa? Ku duba ku gani. Ko akwai wata wahala kamar irin wadda nake sha, wadda Ubangiji ya auko mini a cikin zafin fushinsa?
13 MEM. From on high, he has sent fire into my bones, and he has educated me. He has spread a net for my feet; he has turned me back. He has placed me in desolation, consumed by grief, all day long.
“Daga sama ya aiko da wuta, ya aiko ta cikin ƙasusuwana. Ya shimfiɗa raga a ƙafafuna ya juyo da ni. Ya bar ni ni kaɗai, sumamme dukan yini.
14 NUN. Vigilant is the yoke of my iniquities. They have been folded together in his hand and imposed on my neck. My virtue has been weakened. The Lord has given me into a hand, out of which I am not able to rise.
“Ya ɗaura zunubaina a wuyana; aka naɗe su a hannuwansa. Aka rataye su a wuyana Ubangiji ya kwashe ƙarfina. Ya bashe ni ga waɗanda suka fi ni ƙarfi.
15 SAMECH. The Lord has taken away all of my great ones from my midst. He has called forth time against me, so as to crush my elect ones. The Lord has trampled the winepress, which was for the virgin daughter of Judah.
“Ubangiji ya ƙi duk mayaƙan da suke tare da ni; ya sa wata runduna ta tayar mini ta kuma tattake samarina. Ubangiji ya tattake budurwa Diyar Yahuda kamar’ya’yan inabi a wurin matsewa.
16 AIN. For this I weep, and my eyes bring forth water. For the consoler has been far away from me, changing my soul. My sons have become lost, because the enemy has prevailed.
“Dalilin da ya sa nake kuka ke nan idanuna kuma suna ta zubar da hawaye. Babu wani a kusa da zai yi mini ta’aziyya, ba wanda zai sabunta ruhuna.’Ya’yana sun zama fakirai domin maƙiyina ya yi nasara.”
17 PHE. Zion has reached out her hands; there is no one to console her. The Lord has given orders against Jacob; his enemies are all around him. Jerusalem among them is like a woman made unclean by menstruation.
Sihiyona ta miƙa hannunta, amma ba wani da zai yi mata ta’aziyya. Ubangiji ya umarta cewa maƙwabtansa za su zama maƙiyansa; Urushalima ta zama abar ƙyama a cikinsu.
18 SADE. The Lord is just, for it is I who has provoked his mouth to wrath. I beg all people to listen and to see my sorrow. My virgins and my youths have gone into captivity.
“Ubangiji mai adalci ne, duk da haka na yi tawaye da umarninsa. Ku saurara, jama’a duka; ku dubi wahalar da nake sha. Samarina da’yan matana duka sun tafi bauta.
19 COPH. I called for my friends, but they deceived me. My priests and my elders have been consumed in the city. For they were seeking their food, so as to revive their life.
“Na kira abokaina amma sun yashe ni. Firistocina da dattawana sun hallaka a cikin birnin yayinda suke neman abinci don kada su mutu da yunwa.
20 RES. See, O Lord, that I am in tribulation. My bowels have been disturbed, my heart has been subverted within me, for I am filled with bitterness. Outside, the sword puts to death, and at home there is a similar death.
“Duba, Ubangiji, ka ga ƙuncin da nake ciki! Ina shan azaba a raina, ba ni da kwanciyar rai a cikin zuciyata, domin na yi tawaye sosai. A waje takobi na kisa; a ciki kuma akwai mutuwa.
21 SIN. They have heard that I groan and that there is no one to console me. All my enemies have heard of my misfortune; they have rejoiced that you caused it. You have brought in a day of consolation, and so they shall become like me.
“Mutane suna ji ina nishi da ƙyar, amma ba wanda zai yi mini ta’aziyya. Dukan maƙiyana sun ji wahalar da nake ciki; suna farin ciki da abin da ka yi. Ka kawo ranan nan da ka sanar domin su ma su zama kamar ni.
22 THAU. Let all their evil enter before you. And make vintage of them, just as you made vintage of me, because of all my iniquities. For my sighs are many, and my heart is grieving.
“Bari ka ga muguntarsu duka; ka yi musu yadda ka yi mini domin dukan zunubansu. Nishina da yawa kuma zuciyata ta gaji.”

< Lamentations 1 >