< Lamentations 2 >

1 ALEPH. O how the Lord has covered the daughter of Zion with gloom in his fury! O how he has thrown down from heaven to earth the famous one of Israel, and he has not remembered his footstool in the day of his fury.
Yadda Ubangiji ya rufe Diyar Sihiyona da gizagizan fushi! Ya jefar da darajar Isra’ila daga sama zuwa ƙasa; bai tuna da wurin ɗora ƙafafunsa ba a ranar fushinsa.
2 BETH. The Lord has cast down, and he has not been lenient, with all the beauties of Jacob. In his fury, he has destroyed the fortifications of the virgin of Judah, and he has thrown them down to the ground. He has polluted the kingdom and its leaders.
Ubangiji ya hallakar da wurin zaman Yaƙub ba tausayi; A cikin fushinsa kuma zai rurrushe kagaran Diyar Yahuda. Ya ƙasƙantar da mulki da masu mulki.
3 GHIMEL. In the anger of his fury, he has broken the entire horn of Israel. He has drawn back his right hand before the face of the enemy. And he has kindled within Jacob a flaming fire, devouring all around.
A cikin zafin fushi ya fasa kowane ƙaho na Isra’ila. Ya janye hannun damansa sa’ad da maƙiyi ya zo. Ya yi ƙuna a cikin Yaƙub kamar wuta mai ƙone duk abin da yake kusa da ita.
4 DALETH. He has bent his bow like an enemy. He has fixed his right hand like an adversary. And he has cut down all that was beautiful to behold in the tabernacle of the daughter of Zion. He has poured out his indignation like fire.
Kamar abokin gāba, ya ɗana bakansa; hannun damansa na shirye. Kamar maƙiyi, ya kashe duk wanda idonsa ya ji daɗin gani; ya zuba fushinsa kamar wuta a kan tenti na Diyar Sihiyona.
5 HE. The Lord has become like an enemy. He has thrown down Israel. He has thrown down all of his defenses. He has torn apart his fortifications. And he has filled the daughter of Judah with humbled men and humbled women.
Ubangiji kamar maƙiyi ne; ya hallaka Isra’ila. Ya hallaka wurarenta duka ya kuma hallaka kagaranta. Ya ƙara yawan makoki da baƙin ciki wa Diyar Yahuda.
6 VAU. And he has torn apart her tent like a garden. He has demolished her tabernacle. In Zion, the Lord has delivered feast and Sabbath into oblivion, and king and priest into disgrace, and into the indignation of his fury.
Ya rushe haikalinsa kamar lambu; ya hallaka wurin yi masa sujada. Ubangiji ya sa Sihiyona ta manta da bukukkuwanta da kuma ranakunta na Asabbaci; a cikin zafin fushinsa ya watsar da sarki da firist.
7 ZAIN. The Lord has pushed away his own altar. He has cursed his own sanctuary. He has delivered the walls of its towers into the hand of the enemy. They have made a noise in the house of the Lord, as if on the day of a solemnity.
Ubangiji ya ƙi bagadensa ya kuma yi wofi da haikalinsa. Ya ba maƙiyinta fadodinta; suka yi sowa a cikin gidan Ubangiji kamar a ranar da ake yin biki.
8 HETH. The Lord has decided to tear down the wall of the daughter of Zion. He has stretched out his measuring line, and he has not turned away his hand from perdition. And the rampart has mourned, and with the wall it has been torn apart.
Ubangiji ya ƙuduri niyya yă rushe bangon da yake kewaye da Diyar Sihiyona. Ya auna da igiyar awo bai fasa hallaka ta ba. Ya sa katanga da katanga duk suka lalace.
9 TETH. Her gates have been buried in the ground. He has ruined and crushed its bars. Her king and her princes are with the Gentiles. There is no law, and her prophets have found no vision from the Lord.
Ƙofofinta sun nutse a cikin ƙasa; ya kakkarya ƙarafanta. Sarakunanta da’ya’yan sarakunanta duk an kai su bauta cikin waɗansu ƙasashe, babu sauran doka, annabawa kuma ba su samun wahayi daga wurin Ubangiji.
10 JOD. The elders of the daughter of Zion have become idle; they sit on the ground. They have sprinkled their heads with ashes. They have been wrapped with haircloth. The virgins of Jerusalem have cast their heads down to the ground.
Dattawan Diyar Sihiyona sun zauna shiru a ƙasa; suka kuma sa rigar buhu.’Yan matan Urushalima suka sunkuyar da kawunansu ƙasa.
11 CAPH. My eyes have exhausted their tears. My internal organs have become disturbed. My liver has been poured out on the earth, over the grief of the daughter of my people, when the little ones and the infants passed away in the streets of the town.
Idanuna sun dushe don yawan kuka, raina na cike da baƙin ciki; zuciyata ta karaya domin mutanena sun hallaka, domin yara da jarirai suna suma a kan hanyoyi a cikin birni.
12 LAMED. They said to their mothers, “Where is the wheat and the wine?” when they fell like the wounded in the streets of the city, when they breathed out their lives into the bosoms of their mothers.
Suna ce wa uwayensu, “Ina burodi da ruwan inabi?” Yayinda suke suma kamar mutanen da aka ji masu ciwo a cikin birni, sa’ad da suke mutuwa a hannuwan uwayensu.
13 MEM. To what shall I compare you, or to what shall I liken you, O daughter of Jerusalem? To what shall I equate you, so as to console you, O virgin daughter of Zion? For your destruction is as great as the sea. Who will cure you?
Me zan ce miki? Da me zan kwatanta ki, ke Diyar Urushalima? Da me zan misalta ki, yadda zan iya yi miki ta’aziyya, Ke Budurwa Diyar Sihiyona? Ciwonki yana da zurfi kamar teku. Wane ne zai iya warkar da ke?
14 NUN. Your prophets have seen false and foolish things for you. And they have not laid open your iniquity, so as to provoke you to repentance. Yet they have seen for you false revelations and banishments.
Wahayin annabawanki ƙarya ne kuma marasa amfani; ba su tona zunubanki ba yadda za su iya ceto ki daga bauta ba. Sun yi miki annabcin ƙarya marar amfani.
15 SAMECH. All those who passed by the way have clapped their hands over you. They have hissed and shook their heads over the daughter of Jerusalem, saying, “Is this the city of perfect dignity, the joy of all the earth?”
Duk masu wucewa suna yi miki tafi na reni; suna yi wa Diyar Urushalima tsaki suna kaɗa kai suna cewa, “Wannan ne birnin da aka ce kyakkyawa ne, mai farantawa dukan duniya rai?”
16 PHE. All your enemies have opened their mouth over you. They have hissed and gnashed their teeth, and they said: “We will devour her. Yes, this is the day we waited for. We have found it, we have seen it.”
Maƙiyanki duka suna ta surutu game da ke; suna tsaki suna cizon haƙora suna cewa, “Mun hallaka ta. Wannan ce ranar da muke jira; yau mun gan ta.”
17 AIN. The Lord has done what he decided to do. He has fulfilled his word, which he instructed since the days of antiquity. He has destroyed, and he has not been lenient, and he has caused the enemy to rejoice over you, and he has exalted the horn of your adversaries.
Ubangiji ya yi abin da ya shirya; ya cika maganarsa, wadda ya umarta tun daɗewa. Ya jefar da ke ba tausayi, ya bari maƙiya sun yi nasara da ke, ya ɗaukaka ƙahon maƙiyanki.
18 SADE. Their heart cried out to the Lord from the walls of the daughter of Zion. Let tears run down like a torrent throughout the day and the night. Do not give rest to yourself, and do not allow the pupil of your eye to cease.
Zuciyar mutane ta yi kuka ga Ubangiji. Ya bangon Diyar Urushalima, bar hawayenki su zuba kamar rafi dare da rana; kada ki huta, kada idanunki su huta.
19 COPH. Rise up. Give praise in the night, in the first of the watches. Pour out your heart like water before the sight of the Lord. Lift up your hands to him on behalf of the souls of your little ones, who have passed away from famine at the head of all the crossroads.
Ki tashi, ki yi kuka cikin dare, dare na yi sai ki fara kuka; kina buɗewa Ubangiji zuciyarki. Ki ɗaga hannuwanki gare shi domin rayukan’ya’yanki, waɗanda suka suma don yunwa a kan kowane titi.
20 RES. O Lord, see and consider those whom you have made into such a vintage. So then, shall women eat their own fruit, little ones measured by the palm of the hand? Shall priest and prophet be killed in the sanctuary of the Lord?
“Ka duba, ka gani ya Ubangiji. Wane ne ka taɓa yi wa haka? Ko ya kamata uwaye su ci’ya’yansu,’ya’yan da suka yi reno? Ko ya kamata a kashe firistoci da annabawa a cikin haikalin Ubangiji?
21 SIN. The boy and the old man lie down on the ground outside. My virgins and my youths have fallen by the sword. You have slain them in the day of your fury. You have struck down, and you have not shown pity.
“Matasa da tsofaffi duk suna kwanciya a cikin ƙurar tituna; an karkashe matasa da’yan matana da takobi. Ka kashe su a ranar fushinka; ka kashe su ba tausayi.
22 THAU. You have called, as if to a day of solemnity, those who would terrify me all around. And there was no one, in the day of the fury of the Lord, who escaped or was left behind. Those whom I educated and nourished, my enemy has consumed.
“Kamar yadda kake yin gayyata a ranar biki, haka kake kawo mini tsoro a kowane gefe. A ranar fushin Ubangiji ba mai tserewa ba wanda zai tsira; maƙiyina ya kashe waɗanda na yi renonsu, na kuma lura da su.”

< Lamentations 2 >