< Isaiah 20 >

1 In the year in which Tharthan entered into Ashdod, when Sargon, the king of the Assyrians, had sent him, and when he had fought against Ashdod and had captured it,
A shekarar da babban shugaban yaƙin da Sargon sarkin Assuriya ya aika, ya zo Ashdod ya kuma fāɗa mata ya kuma ci ta da yaƙi,
2 in that same time, the Lord spoke by the hand of Isaiah, the son of Amoz, saying: “Go forth, and remove the sackcloth from your waist, and take your shoes from your feet.” And he did so, going out naked and barefoot.
a wannan lokaci Ubangiji ya yi magana ta wurin Ishaya ɗan Amoz. Ya ce masa, “Tuɓe tsummokin da kake saye da su, da kuma takalman da ka sa a ƙafafu.” Ya kuwa yi haka, yana yawo tsirara kuma ba takalma a ƙafa.
3 And the Lord said: Just as my servant Isaiah has walked naked and barefoot, as a sign and as a portent of three years over Egypt and over Ethiopia,
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kamar dai yadda bawana Ishaya ya yi ta yawo tsirara kuma ba takalmi a ƙafa shekara uku, a matsayin alama da shaida a kan Masar da Kush,
4 so also will the king of the Assyrians force the captivity of Egypt, and the transmigration of Ethiopia: young and old, naked and barefoot, with their buttocks uncovered, to the shame of Egypt.
haka sarkin Assuriya zai kwashe kamammun Masarawa da Kushawa tsirara kuma ba takalma a ƙafa, yaro da babba, asirinsu a tsiraice, don a kunyata Masar.
5 And they will be afraid and confounded over Ethiopia, their hope, and Egypt, their glory.
Waɗanda suka dogara ga Kush suka yi taƙama da Masar za su ji tsoro su kuma sha kunya.
6 And in that day, the inhabitants of a certain island will say: “Behold, this was our hope, we fled to them for help, to free us from the face of the king of the Assyrians. And now, how will we be able to escape?”
A wannan rana mutanen da suke zama a bakin teku za su ce, ‘Dubi abin da ya faru da waɗanda muka dogara a kai, waɗanda muka gudu muka je don neman taimako da ceto daga sarkin Assuriya! Yaya za mu tsira?’”

< Isaiah 20 >