< Isaiah 21 >

1 The burden of the desert of the sea. Just as the whirlwinds approach from Africa, it approaches from the desert, from a terrible land.
Abin da Allah ya faɗa game da Hamada da take kusa da Teku. Kamar guguwa mai share cikin ƙasar kudu, mai hari ya zo daga hamada, daga ƙasar mai banrazana.
2 A difficult vision has been announced to me: he who is unbelieving, he acts unfaithfully, and he who is a plunderer, he devastates. Ascend, O Elam! Lay siege, O Media! I have caused all its mourning to cease.
An nuna mini mugun wahayi, mai bashewa ya bashe, mai washewa ya washe. Elam, ki yi yaƙi! Mediya, ki yi kwanto! Zan kawo ƙarshen dukan nishe-nishen da ta jawo.
3 Because of this, my lower back has been filled with pain, and anguish has possessed me, like the anguish of a woman in labor. I fell down when I heard it. I was disturbed when I saw it.
Game da wannan jikina yana ciwo, zafi ya kama ni, kamar na mace mai naƙuda; na razana game da abin da na ji, na yi mamakin abin da na gani.
4 My heart withered. The darkness stupefied me. Babylon, my beloved, has become a wonder to me.
Gabana tana ta fāɗuwa, tsoro ya sa ina rawan jiki; hasken da nake marmari ya zo da razana gare ni.
5 Prepare the table. Contemplate, from a place of observation, those who eat and drink. Rise up, you leaders! Take up the shield!
Sun shirya teburori, sun shimfiɗa dardumai, sun ci, sun sha! Tashi, ku hafsoshi, sa mai a garkuwoyi!
6 For the Lord has said this to me: “Go and station a watchman. And let him announce whatever he will see.”
Ga abin da mai girma ya ce mini, “Tafi, ka sa mai tsaro ka kuma sa ya ba da rahoton abin da ya gani.
7 And he saw a chariot with two horsemen, and a rider on a donkey, and a rider on a camel. And he considered them diligently, with an intense gaze.
Sa’ad da ya ga kekunan yaƙi tare da ƙungiyoyin dawakai, mahaya a kan jakuna, ko mahaya a kan raƙuma, to, fa ya zauna a faɗake, ya kintsa sosai.”
8 And a lion cried out: “I am on the watchtower of the Lord, standing continually by day. And I am at my station, standing throughout the night.
Mai tsaron kuma ya yi ihu, “Kowace rana, ranka yă daɗe, nakan tsaya a hasumiyar tsaro; kowane dare nakan tsaya a wurin aikina.
9 Behold, a certain man approaches, a man riding on a two-horse chariot.” And he responded, and he said: “Fallen, fallen is Babylon! And all its graven gods have been crushed into the earth!
Duba, ga wani mutum tafe a keken yaƙin tare da ƙungiyar dawakai. Ya kuma mayar da amsa, ‘Babilon ta fāɗi, ta fāɗi! Dukan siffofin allolinta kwance a ragargaje a ƙasa!’”
10 O my threshed grain! O sons of my threshing floor! What I have heard from the Lord of hosts, the God of Israel, I have announced to you.”
Ya mutanena, an ragargaje ku a masussuka, na faɗa muku abin da na ji daga Ubangiji Maɗaukaki, daga Allah na Isra’ila.
11 The burden of Dumah, cried out to me from Seir: “Watchman, how goes the night? Watchman, how goes the night?”
Abin da Allah ya faɗa game da Duma, Wani ya kira ni daga Seyir, “Mai tsaro, me ya rage a daren? Mai tsaro, me ya rage a daren?”
12 The watchman said: “Morning approaches with the night. If you are seeking: seek, and convert, and approach.”
Mai tsaro ya amsa, “Safiya ta gabato, haka kuma dare. In za ka yi tambaya, to, yi tambaya; sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”
13 The burden in Arabia. In the forest you shall sleep, in the evening on the paths of Dedanim.
Abin da Allah ya faɗa game da Arabiya. Ku ayarin Dedanawa, ku da kuka sauka a jejin Arabiya,
14 You who inhabit the land of the south: upon meeting the thirsty, bring water; meet the fugitive with bread.
ku kawo ruwa don ƙishirwa; ku da kuke zama a Tema, ku kawo abinci don masu gudun hijira.
15 For they are fleeing before the face of swords, before the face of a sword hanging over them, before the face of a bent bow, before the face of a grievous battle.
Sun gudu daga takobi, daga takobin da aka janye, daga bakan da aka tanƙware da kuma daga zafin yaƙi.
16 For the Lord said this to me: “After one more year, just like one year for a hired hand, all the glory of Kedar will be taken away.
Ga abin da mai girma ya ce mini, “Cikin shekara ɗaya, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, dukan sojojin Kedar za su zo ga ƙarshe.
17 And the remainder of the multitude of strong archers from the sons of Kedar will be few, for the Lord, the God of Israel, has spoken it.”
Waɗanda suka yi rai na maharba, jarumawan Kedar, za su zama kaɗan.” Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa.

< Isaiah 21 >