< Isaiah 19 >

1 The burden of Egypt. Behold, the Lord will ascend upon a lofty cloud, and he will enter into Egypt, and the false images of Egypt will be moved before his face, and the heart of Egypt will waste away in its midst.
Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
2 And I will cause Egyptian to rush against Egyptian. And they will fight: a man against his brother, and a man against his friend, city against city, kingdom against kingdom.
“Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
3 And the spirit of Egypt will be ruptured to its very core. And I will cast down their plan violently. And they will seek answers from their false images, and their diviners, and those led by demons, and their seers.
Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
4 And I will deliver Egypt into the hand of cruel masters, and a strong king will dominate them, says the Lord, the God of hosts.
Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
5 And the waters of the sea will dry up, and the river will be desolate and dry.
Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
6 And the rivers will fail. The streams of its banks will diminish and dry up. The reed and the bulrush will wither away.
Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
7 The channel of the river will be stripped down to its source, and everything irrigated by it will dry up and wither and be no more.
haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
8 And the fishermen will grieve. And all who cast a hook into the river will mourn. And those who cast a net upon the surface of its waters will languish.
Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
9 Those who work with linen, combing and weaving fine textiles, will be confounded.
Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
10 And its irrigated places will begin to fail, with all those who make pools to take fish.
Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
11 The leaders of Tanis are foolish. The wise counselors of Pharaoh have given foolish counsel. How can you say to Pharaoh: “I am the son of wise men, the son of the kings of antiquity?”
Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
12 Where are your wise men now? Let them announce it to you, and let them reveal what the Lord of hosts intends for Egypt.
Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
13 The leaders of Tanis have become foolish. The leaders of Memphis have decayed. They have deceived Egypt, the corner of its people.
Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
14 The Lord has mixed a spirit of giddiness into its midst. And they have caused Egypt to err in all its works, like a drunken man who staggers and vomits.
Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
15 And there will be no work for Egypt that would produce a head or a tail, one who bows down or one who refrains from bowing down.
Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
16 In that day, Egypt will be like women, and they will be stupefied and fearful before the presence of the shaking hand of the Lord of hosts, the hand which he will move over them.
A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
17 And the land of Judah will be a dread to Egypt. Everyone who thinks about it will be terrified before the presence of the plan of the Lord of hosts, the plan which he has decided concerning them.
Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
18 In that day, there will be five cities in the land of Egypt which speak the language of Canaan, and which swear by the Lord of hosts. One will be called the City of the Sun.
A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
19 In that day, there will be an altar of the Lord in the midst of the land of Egypt and a monument of the Lord beside its borders.
A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
20 This shall be a sign and a testimony to the Lord of hosts in the land of Egypt. For they will cry out to the Lord before the face of the tribulation, and he will send them a savior and a defender who will free them.
Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
21 And the Lord will be acknowledged by Egypt, and the Egyptians will recognize the Lord in that day, and they will worship him with sacrifices and gifts. And they will make vows to the Lord, and they will fulfill them.
Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
22 And the Lord will strike Egypt with a scourge, and he will heal them. And they will return to the Lord. And he will be placated toward them, and he will heal them.
Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
23 In that day, there will be a way from Egypt to the Assyrians, and the Assyrian will enter into Egypt, and the Egyptian will be with the Assyrians, and the Egyptians will serve Assur.
A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
24 In that day, will Israel be the third to the Egyptian and the Assyrian, a blessing in the midst of the earth,
A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
25 which the Lord of hosts has blessed, saying: Blessed be my people of Egypt, and the work of my hands for the Assyrian, but Israel is my inheritance.
Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”

< Isaiah 19 >