< Isaiah 18 >

1 Woe to the land, that winged cymbal, which is beyond the rivers of Ethiopia,
Kaiton ƙasar da ake jin ƙarar fikafikai a bakin kogunan Kush,
2 which sends ambassadors by sea and in vessels of papyrus above the waters. Go forth, O swift Angels, to a nation which has been convulsed and torn apart, to a terrible people, after whom there is no other, to a nation apprehensive and downtrodden, whose land the rivers have spoiled.
wadda ta aiko da jakadu ta teku cikin jiragen ruwan da aka yi da kyauro a bisa ruwa. Ku tafi, ku’yan saƙo masu sauri, zuwa ga dogayen mutane masu sulɓin jiki, zuwa ga mutanen da ake jin tsoro a ko’ina, al’umma mai ƙarfin iko tana jawabin da ba a saba ji ba, mai ƙasar da koguna suka raba.
3 All inhabitants of the world, you who dwell upon the earth: when the sign will have been elevated on the mountains, you will see, and you will hear the blast of the trumpet.
Ku dukan mutanen duniya, ku da kuke zama a duniya, sa’ad da aka ɗaga tutar a kan duwatsu, za ku gan shi, sa’ad da kuma aka busa ƙaho, za ku ji shi.
4 For the Lord says this to me: I will be quiet, and I will consider in my place, as the light at midday is clear, and as a cloud of dew in the day of the harvest.
Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Zan yi shiru in kuma duba a hankali daga mazaunina, kamar ƙuna mai zafi a hasken rana, kamar girgijen raba a lokacin girbi.”
5 For before the harvest, all was flourishing. And it will spring forth with an untimely completion, and its little branches will be pruned with a curved blade. And what is left over will be cut away and shaken off.
Gama kafin girbi, sa’ad da furanni suka karkaɗe furanni kuma suka zama’ya’yan inabin da suka nuna, zai faffalle rassan kuringar inabi da wuƙa, ya yanke ya kuma kwashe rassan da suka bazu.
6 And together they will be abandoned to the birds of the mountains and to the wild beasts of the earth. And the birds will be continuously on them in the summer, and all the wild beasts of the earth will winter over them.
Duk za a bar su wa tsuntsayen dutse su ci da kuma namun jeji; tsuntsaye kuma za su ci rani a kansu, namun jeji kuma za su yi damina a kansu.
7 In that time, a gift will be carried to the Lord of hosts, from a people divided and torn apart, from a terrible people, after whom there has been no other, from an apprehensive nation, apprehensive and downtrodden, whose land the rivers have ruined, and it will be carried to the place of the name of the Lord of hosts, to mount Zion.
A wannan lokaci za a kawo kyautai wa Ubangiji Maɗaukaki daga dogayen mutane masu sulɓin jiki, daga mutanen da ake jin tsoro a ko’ina, al’umma mai ƙarfin iko na jawabin da ba a saba ji ba, mai ƙasar da koguna suka raba. Za a kawo kyautai zuwa Dutsen Sihiyona, wurin da Sunan Ubangiji Maɗaukaki yake.

< Isaiah 18 >