< Hosea 12 >

1 Ephraim feeds on wind and follows burning heat; all day long he multiplies lies and desolation. And he has entered into a pact with the Assyrians, and he has carried oil into Egypt.
Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
2 Therefore, the judgment of the Lord is with Judah and a visitation is upon Jacob. He will repay him according to his ways and according to his inventions.
Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
3 In the womb, he supplanted his brother; for in his good fortune, he had been guided by an angel.
A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
4 And he prevailed over an angel, for he had been strengthened. He wept and petitioned him. He found him in Bethel, and there he has spoken to us.
Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
5 And the Lord God of hosts, the Lord is his memorial.
Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
6 And so, you should convert to your God. Keep mercy and judgment, and have hope in your God always.
Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
7 Canaan, in his hand is a deceitful balance, he has chosen false accusations.
Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
8 And Ephraim has said, “Nevertheless, I have become rich; I have found an idol for myself. All of my labors will not reveal to me the iniquity that I have committed.”
Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
9 And I, the Lord your God from the land of Egypt, nevertheless will cause you to dwell in tabernacles, just as during the days of the feast.
“Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
10 And I have spoken through the prophets, and I have multiplied visions, and I have used parables through the hands of the prophets.
Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
11 If Gilead is an idol, then they have been sacrificing cattle in Gilgal to no purpose. For even their altars are like clutter on the soil of the field.
Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
12 Jacob fled into the region of Syria, and Israel served like a wife, and was served by a wife.
Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
13 Yet by a prophet the Lord led Israel out of Egypt, and he was served by a prophet.
Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
14 Ephraim has provoked me to wrath with his bitterness, and his blood will overcome him, and his Lord will requite him for his shamefulness.
Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.

< Hosea 12 >