< Hosea 11 >

1 Just as the morning passes, so has the king of Israel passed by. For Israel was a child and I loved him; and out of Egypt I called my son.
“Sa’ad da Isra’ila yake yaro, na ƙaunace shi, daga Masar kuma na kira ɗana.
2 They called them, and so they departed before their face. They offered victims to the Baals, and they sacrificed to graven images.
Amma yawan kiran da na yi wa Isra’ila haka nesa da ni da suke ta yi. Suka miƙa hadaya ga Ba’al suka kuma ƙona turare ga siffofi.
3 And I was like a foster father to Ephraim. I carried them in my arms. And they did not know that I healed them.
Ni ne na koya wa Efraim tafiya ina kama su da hannu; amma ba su gane cewa ni ne na warkar da su ba.
4 I will draw them with the cords of Adam, with the bands of love. And I will be to them like one who raises the yoke over their jaws. And I will reach down to him so that he may eat.
Na bishe su da linzamin alheri da tausayi, da ragamar ƙauna; Na cire karkiya daga wuyansu na kuma rusuna na ciyar da su.
5 He will not return to the land of Egypt, but Assur himself will be the king over him, because they were not willing to be converted.
“Ba za su koma Masar ba Assuriya kuma ba za tă yi mulki a bisansu ba saboda sun ƙi su tuba ba?
6 The sword has begun in his cities, and it will consume his elect and devour their heads.
Takuba za su yi ta wulgawa a biranensu, za su hallaka sandunan ƙarafan ƙofofinsu su kuma kawo ƙarshen ƙulle-ƙullensu.
7 And my people will long for my return. But a yoke will be imposed on them together, which will not be taken away.
Mutanena sun ƙudura su juye daga gare ni. Ko da ma suka yi kira ga Mafi Ɗaukaka, ta ko ƙaƙa ba zai girmama su ba.
8 How will I provide for you, Ephraim; how will I protect you, Israel? How will I provide for you as for Adam; will I set you like Zeboiim? My heart has changed within me; together with my regret, it has been stirred up.
“Yaya zan ba da kai, Efraim? Yaya zan miƙa ka, Isra’ila? Yaya zan yi da kai kamar Adma? Yaya zan yi da kai kamar Zeboyim? Zuciyata ta canja a cikina; dukan tausayina ya huru.
9 I will not act on the fury of my wrath. I will not turn back to utterly destroy Ephraim. For I am God, and not man, the Divine in your midst, and I will not advance upon the city.
Ba zan zartar da fushina mai zafi ba, ba kuwa zan juya in ragargaza Efraim ba. Gama ni Allah ne, ba mutum ba, Mai Tsarki a cikinku. Ba zan zo cikin fushi ba.
10 They will walk after the Lord; he will roar like a lion. For he himself will roar, and the sons of the sea will dread.
Za su bi Ubangiji; zai yi ruri kamar zaki. Sa’ad da ya yi ruri,’ya’yansa za su zo da rawan jiki daga yamma.
11 And they will fly like a bird out of Egypt, and like a dove from the land of the Assyrians. And I will arrange them in their own houses, says the Lord.
Za su zo da rawan jiki kamar tsuntsaye daga Masar, kamar kurciyoyi daga Assuriya. Zan zaunar da su a cikin gidajensu,” in ji Ubangiji.
12 Ephraim has besieged me with denials, and the house of Israel with deceit. But Judah went down as a witness before God and the holy ones of faith.
Mutanen Efraim sun kewaye ni da ƙarairayi, gidan Isra’ila da ruɗu. Mutanen Yahuda kuma suna yi wa Allah ƙin ji, har ma a kan Mai Tsarkin nan mai aminci.

< Hosea 11 >