< Genesis 24 >

1 Now Abraham was old and of many days. And the Lord had blessed him in all things.
Yanzu fa Ibrahim ya tsufa, yana da shekaru masu yawa, Ubangiji kuma ya albarkace shi a kowace hanya.
2 And he said to the elder servant of his house, who was in charge of all that he had: “Place your hand under my thigh,
Sai Ibrahim ya ce wa babban bawan gidansa, wanda yake lura da duk abin da yake da shi, “Sa hannunka a ƙarƙashin cinyata.
3 so that I may make you swear by the Lord, the God of heaven and earth, that you will not take a wife for my son from the daughters of the Canaanites, among whom I live.
Ina so ka rantse da sunan Ubangiji Allah na sama da ƙasa, cewa ba za ka samo wa ɗana mata daga’yan matan Kan’aniyawa, waɗanda nake zama cikinsu ba.
4 But that you will proceed to my land and kindred, and from there take a wife for my son Isaac.”
Amma za ka tafi ƙasata da kuma cikin’yan’uwana, ka samo mata saboda ɗana Ishaku.”
5 The servant responded, “If the woman is not willing to come with me into this land, must I lead your son back to the place from which you departed?”
Bawan ya ce masa, “Me zai faru in matar ba tă yarda tă zo tare da ni zuwa wannan ƙasa ba? In komar da ɗanka a ƙasar da ka fito ne ke nan?”
6 And Abraham said: “Beware that you never lead my son back to that place.
Ibrahim ya ce, “Ka tabbata ba ka komar da ɗana can ba.”
7 The Lord God of heaven, who took me from my father’s house, and from the land of my nativity, who spoke to me and swore to me, saying, ‘To your offspring I will give this land,’ himself will send his Angel before you, and you will take from there a wife for my son.
Ubangiji Allah na sama, wanda ya fitar da ni daga gidan mahaifina, da kuma ƙasar asalina wanda kuma ya yi magana da ni, ya yi mini alkawari da rantsuwa cewa, “Ga zuriyarka zan ba da wannan ƙasa, zai aika mala’ikansa yă sha gabanka domin ka samo wa ɗana mata daga can.
8 But if the woman is not willing to follow you, you will not be held by the oath. Only do not lead my son back to that place.”
In matar ba tă yarda tă zo tare da kai ba, za a kuɓutar da kai daga wannan rantsuwa. Sai dai kada ka kai ɗana a can.”
9 Therefore, the servant placed his hand under the thigh of Abraham, his lord, and he swore to him on his word.
Saboda haka bawan ya sa hannunsa a ƙarƙashin cinyar maigidansa Ibrahim, ya kuma rantse masa game da wannan al’amari.
10 And he took ten camels from his lord’s herd, and he went forth, carrying with him things from all of his goods. And he set out, and continued on, to the city of Nahor, in Mesopotamia.
Sai bawan ya ɗibi raƙuma goma na maigidansa ya tafi, ɗauke da kowane irin abubuwa masu kyau daga wurin maigidansa. Ya fita don yă tafi Aram-Naharayim, ya kama hanyarsa zuwa garin Nahor.
11 And when he had made the camels lie down outside of the town, near a well of water, in the evening, at the time when women are accustomed to go out to draw water, he said:
Ya sa raƙuman suka durƙusa kusa da rijiya a bayan gari; wajen yamma ne, lokacin da mata sukan fita ɗiban ruwa.
12 “O Lord, the God of my lord Abraham, meet with me today, I beg you, and show mercy to my lord Abraham.
Sai ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, ka ba ni nasara yau, ka kuma nuna alheri ga maigidana Ibrahim.
13 Behold, I stand near the fountain of water, and the daughters of the inhabitants of this city will go forth to draw water.
Duba, ina tsaye a bakin rijiyar ruwa,’ya’ya matan mutanen gari kuma suna fitowa domin ɗiban ruwa.
14 Therefore, the girl to whom I will say, ‘Tip your pitcher, so that I may drink,’ and she will respond, ‘Drink. In fact, I will give your camels a drink also,’ the same one is she whom you have prepared for your servant Isaac. And by this, I will understand that you have shown mercy to my lord.”
Bari yă zama sa’ad da na ce wa wata yarinya, ‘Ina roƙonki ki saukar da tulunki domin in sha,’ in ta ce, ‘Ka sha, zan kuma ba wa raƙumanka ma’; bari tă zama ita ce ka zaɓa wa bawanka Ishaku. Ta haka zan san cewa ka nuna wa maigidana alheri.”
15 But he had not yet completed these words within himself, when, behold, Rebekah went out, the daughter of Bethuel, son of Milcah, the wife of Nahor, the brother of Abraham, having a pitcher on her shoulder.
Kafin ya gama addu’a, sai Rebeka ta fito da tulu a kafaɗarta. Ita’yar Betuwel ɗan Milka, matar Nahor, ɗan’uwan Ibrahim.
16 She was an exceedingly elegant girl, and a most beautiful virgin, and unknown by man. And she descended to the spring, and she filled her pitcher, and then was returning.
Yarinyar kuwa kyakkyawa ce, budurwa, ba namijin da ya taɓa kwana da ita. Ta gangara zuwa rijiyar, ta cika tulunta ta kuma hauro.
17 And the servant ran to meet her, and he said, “Provide me with a little water to drink from your pitcher.”
Bawan ya yi sauri ya same ta ya ce, “Ina roƙonki ki ba ni ɗan ruwa daga tulunki.”
18 And she responded, “Drink, my lord.” And she quickly brought down the pitcher on her arm, and she gave him a drink.
Ta ce, “Ka sha, ranka yă daɗe,” ta yi sauri ta saukar da tulun a hannuwanta, ta kuma ba shi, ya sha.
19 And after he drank, she added, “In fact, I will draw water for your camels also, until they all drink.”
Bayan ta ba shi ya sha, sai ta ce, “Zan ɗebo wa raƙumanka ruwa su ma, har sai sun gama sha.”
20 And pouring out the pitcher into the troughs, she ran back to the well to draw water; and having drawn, she gave it to all the camels.
Sai ta yi sauri ta juye ruwan da yake tulunta cikin kwami, ta koma zuwa rijiyar da gudu don ta ƙara ɗebo ruwa, ta kuma ɗebo isashe saboda dukan raƙumansa.
21 But he was contemplating her silently, wanting to know whether the Lord had caused his journey to prosper or not
Mutumin bai ce uffam ba, ya dai kalle ta sosai don yă san ko Ubangiji ya ba shi nasara a tafiyarsa ko babu.
22 Then, after the camels drank, the man took out gold earrings, weighing two shekels, and the same number of bracelets, ten shekels in weight.
Sa’ad da raƙuman suka gama shan ruwa, mutumin ya fitar da zoben hanci na zinariya mai nauyin giram biyar da woroworo biyu na zinariya masu nauyin shekel goma, ya ba ta.
23 And he said to her: “Whose daughter are you? Tell me, is there any place in your father’s house to lodge?”
Sa’an nan ya tambaye ta ya ce, “Ke’yar wace ce? Ina roƙonki ki faɗa mini, akwai wuri a gidan mahaifinki da za mu kwana?”
24 She responded, “I am the daughter of Bethuel, the son of Milcah, to whom she gave birth for Nahor.”
Sai ta ce masa, “Ni’yar Betuwel ce ɗan da Milka ta haifa wa Nahor.”
25 And she continued, saying, “There is very much straw and hay with us, and a spacious place to stay.”
Ta ƙara da cewa, “Muna da isashen ciyawa da abincin dabbobi, da kuma wuri domin ku kwana.”
26 The man bowed himself down, and he adored the Lord,
Sa’an nan mutumin ya rusuna ya yi wa Ubangiji sujada,
27 saying, “Blessed be the Lord, the God of my lord Abraham, who has not taken away his mercy and truth from my lord, and who has led me on a direct journey to the house of the brother of my lord.”
yana cewa, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, wanda bai daina nuna alheri da amincinsa ga maigidana ba. Ni kam, Ubangiji ya bishe ni a tafiyata zuwa gidan’yan’uwan maigidana.”
28 And so the girl ran, and she reported all that she had heard in the house of her mother.
Yariyan ta gudu ta faɗa wa mutanen gidan mahaifiyarta game da abubuwan nan.
29 Now Rebekah had a brother, named Laban, who went out quickly to the man, where the spring was.
Rebeka fa tana da wani ɗan’uwa mai suna Laban, sai ya yi hanzari ya fita zuwa wurin mutumin a rijiyar.
30 And when he had seen the earrings and bracelets in his sister’s hands, and he had heard all the words being repeated, “This is what the man spoke to me,” he came to the man who stood by the camels and near the spring of water,
Nan da nan da ya ga zoben hancin da woroworo a hannuwan’yar’uwansa, ya kuma ji Rebeka ta faɗa abin da mutumin ya ce mata, sai ya fita zuwa wurin mutumin, ya same shi yana tsaye wajen raƙuma kusa da rijiyar.
31 and he said to him: “Enter, O blessed of the Lord. Why do you stand outside? I have prepared the house, and a place for the camels.”
Sai ya ce, “Zo, ya kai mai albarka na Ubangiji, don me kake tsaye a waje? Gama na shirya gida da wuri domin raƙuma.”
32 And he brought him into his guest quarters. And he unharnessed the camels, and he distributed straw and hay, and water to wash his feet and that of the men who arrived with him.
Don haka mutumin ya tafi gidan, aka kuma saukar da kaya kan raƙuman. Aka kawo wa raƙuman ciyawa da abincin dabbobi, aka kuma kawo ruwa dominsa da mutanensa su wanke ƙafafunsu.
33 And bread was set out in his sight. But he said, “I will not eat, until I have spoken my words.” He answered him, “Speak.”
Sa’an nan aka ajiye abinci a gabansa, amma ya ce, “Ba zan ci ba, sai na faɗi abin da yake tafe da ni.” Sai Laban ya ce, “Faɗa mana.”
34 Then he said: “I am the servant of Abraham.
Saboda haka ya ce, “Ni bawan Ibrahim ne.
35 And the Lord has blessed my lord greatly, and he has become great. And he has given him sheep and oxen, silver and gold, men servants and women servants, camels and donkeys.
Ubangiji ya albarkaci maigidana sosai, ya kuma zama mai arziki. Ya ba shi tumaki, shanu, azurfa, zinariya, bayi maza da mata, raƙuma, da kuma jakuna.
36 And Sarah, the wife of my lord, has given birth to a son for my lord in her old age, and he has given him all that he had.
Saratu matar maigidana ta haifa masa ɗa a tsufanta, ya kuma ba shi duk mallakarsa.
37 And my lord made me swear, saying: ‘You shall not take a wife for my son from the Canaanites, in whose land I dwell.
Maigidana ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, ‘Kada ka ɗauko wa ɗana mata daga’ya’ya matan Kan’aniyawa, waɗanda nake zama a ƙasarsu,
38 But you shall travel to my father’s house, and you shall take a wife of my own kindred for my son.’
amma ka tafi wajen gidan mahaifina da kuma dangina, ka ɗauko wa ɗana mata.’
39 But truly, I answered my lord, ‘What if the woman is not willing to come with me?’
“Sai na ce wa maigidana, ‘A ce matar ba tă yarda tă zo tare da ni ba fa?’
40 ‘The Lord,’ he said, ‘in whose sight I walk, will send his Angel with you, and he will direct your way. And you shall take a wife for my son from my own kindred and from my father’s house.
“Maigidana ya ce, ‘Ubangiji wanda yake tare da ni zai aiki mala’ikansa tare da kai, yă kuma sa tafiyarka tă yi nasara, don ka samo wa ɗana mata daga dangina, daga kuma gidan mahaifina.
41 But you will be innocent of my curse, if, when you will arrive at my close relatives, they will not grant this to you.’
Ta haka za ka kuɓuta daga rantsuwata sa’ad da ka tafi wurin dangina, ko ma sun ƙi su ba ka ita, za ka kuɓuta daga rantsuwata.’
42 And so, today I arrived at the well of water, and I said: ‘O Lord, the God of my lord Abraham, if you have directed my way, in which I now walk,
“Sa’ad da na zo rijiya a yau, na ce, ‘Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, ina roƙonka ka ba ni nasara a tafiyar da na yi.
43 behold, I stand next to the well of water, and the virgin, who will go forth to draw water, will hear from me, “Give me a little water to drink from your pitcher.”
Duba, ina tsaye kusa da wannan rijiya; in wata yarinya ta fito domin tă ɗiba ruwa, wadda in na ce mata, “Ina roƙonki bari in ɗan sha ruwa daga tulunki,”
44 And she will say to me, “You drink, and I will also draw for your camels.” Let the same be the woman, whom the Lord has prepared for the son of my lord.’
in ta ce, “Ka sha, zan kuma ba wa raƙumanka ma,” bari tă zama wadda Ubangiji ya zaɓar wa ɗan maigidana.’
45 And while I thought over these things silently within myself, Rebekah appeared, arriving with a pitcher, which she carried on her shoulder. And she descended to the spring and drew water. And I said to her, ‘Give me a little to drink.’
“Kafin in gama addu’ar, a zuciyata, sai ga Rebeka ta fito da tulunta a kafaɗarta. Ta gangara zuwa rijiyar ta ɗebo ruwa, na kuma ce mata, ‘Ina roƙonki ki ba ni ɗan ruwa daga tulunki.’
46 And she quickly let down the pitcher from her arm, and said to me, ‘You drink, and to your camels I will also distribute drinking water.’ I drank, and she watered the camels.
“Ta yi sauri ta saukar da tulun daga kafaɗarta ta ce, ‘Sha, zan kuma ba wa raƙumanka su ma.’ Sai na sha, ta kuma shayar da raƙumana su ma.
47 And I questioned her, saying, ‘Whose daughter are you?’ And she responded, ‘I am the daughter of Bethuel, the son of Nahor, whom Milcah bore to him.’ And so, I hung the earrings on her, to adorn her face, and I put the bracelets on her hands.
“Na tambaye ta, ‘Ke’yar wane ne?’ “Ta ce, ‘’Yar Betuwel ɗan Nahor, wanda Milka ta haifa masa.’ “Sai na sa mata zobe a hancinta, woroworo kuma a hannuwata,
48 And falling prostrate, I adored the Lord, blessing the Lord, the God of my lord Abraham, who has led me along the straight path so as to take the daughter of my lord’s brother to his son.
na kuma sunkuya na yi wa Ubangiji sujada. Na yabi Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim wanda ya bi da ni a hanyar da take daidai, don in samo wa ɗan maigidana jikanyar ɗan’uwansa.
49 For this reason, if you would act according to mercy and truth with my lord, tell me so. But if it pleases you otherwise, say that to me also, so that I may go either to the right, or to the left.”
Yanzu fa in za ku nuna wa maigidana alheri da aminci, ku faɗa mini, in kuma ba haka ba, ku faɗa mini, don in san hanyar da zan juya.”
50 And Laban and Bethuel responded: “A word has proceeded from the Lord. We are not able to speak anything else to you, beyond what pleases him.
Laban da Betuwel suka ce, “Wannan daga wurin Ubangiji ne, ba abin da za mu ce I, ko a’a ba.
51 Lo, Rebekah is in your sight. Take her and continue on, and let her be the wife of the son of your lord, just as the Lord has spoken.”
Ga Rebeka, ɗauke ta ku tafi, bari tă zama matar ɗan maigidanka, yadda Ubangiji ya umarta.”
52 When Abraham’s servant had heard this, falling down to the ground, he adored the Lord.
Sa’ad da bawan Ibrahim ya ji abin da suka ce, sai ya rusuna har ƙasa a gaban Ubangiji.
53 And bringing forth vessels of silver and gold, as well as garments, he gave them to Rebekah as a tribute. Likewise, he offered gifts to her brothers and her mother.
Sa’an nan bawan ya fito da kayan ado na zinariya da azurfa da kayayyaki na tufafi ya ba wa Rebeka; ya kuma ba wa ɗan’uwanta da mahaifiyarta kyautai masu tsada.
54 And a banquet began, and they feasted and drank together, and they lodged there. And rising up in the morning, the servant said, “Release me, so that I may go to my lord.”
Sa’an nan shi da mutanen da suke tare da shi suka ci, suka sha, suka kuma kwana a can. Kashegari da safe da suka tashi sai ya ce, “A sallame ni in koma wurin maigidana.”
55 And her brothers and mother responded, “Let the girl remain for at least ten days with us, and after that, she will continue on.”
Amma ɗan’uwanta da mahaifiyarta suka ce, “Bari yarinyar ta ɗan zauna tare da mu kwana goma ko fiye, sa’an nan ka ta fi.”
56 “Do not be willing,” he said, “to delay me, for the Lord has directed my way. Release me, so that I may journey to my lord.”
Amma ya ce musu, “Kada ku tsai da ni, tun da Ubangiji ya ba ni nasara a tafiyata. Ku sallame ni domin in tafi wurin maigidana.”
57 And they said, “Let us call the girl, and ask her will.”
Sa’an nan suka ce, “Bari mu kira yarinyar mu tambaye ta game da zancen.”
58 And when, having been called, she arrived, they wanted to know, “Will you go with this man?” And she said, “I will go.”
Saboda haka suka kira Rebeka suka ce mata, “Za ki tafi tare da mutumin nan?” Sai ta ce, “Zan tafi.”
59 Therefore, they released her and her nurse, and the servant of Abraham and his companions,
Saboda haka suka sallame Rebeka,’yar’uwarsu, duk da uwar goyonta da bawan Ibrahim da mutanensa.
60 wishing prosperity for their sister, by saying: “You are our sister. May you increase to thousands of thousands. And may your offspring possess the gates of their enemies.”
Suka kuma albarkaci Rebeka suka ce mata, “’Yar’uwarmu, bari ki zama mahaifiyar dubu dubbai, bari zuriyarki su mallaki ƙofofin abokan gābansu.”
61 And so, Rebekah and her maids, riding upon camels, followed the man, who quickly returned to his lord.
Sa’an nan Rebeka da bayinta mata suka shirya suka hau raƙumansu suka koma tare da mutumin. Da haka bawan ya ɗauki Rebeka ya tafi.
62 Then, at the same time, Isaac was walking along the way that leads to the well, whose name is: ‘of the One who lives and who sees.’ For he dwelt in the southern land.
Ishaku kuwa ya zo daga Beyer-Lahai-Royi, gama yana zama a Negeb.
63 And he had gone out to meditate in the field, as daylight was now declining. And when he had lifted up his eyes, he saw camels advancing from afar.
Wata rana da yamma ya fita zuwa fili domin yă yi tunani, sa’ad da ya ɗaga ido, sai ya ga raƙuma suna zuwa.
64 Likewise, Rebekah, having seen Isaac, descended from the camel.
Rebeka ma ta ɗaga ido sai ta ga Ishaku. Ta sauka daga raƙuminta da sauri,
65 And she said to the servant, “Who is that man who advances to meet us through the field?” And he said to her, “That is my lord.” And so, quickly taking up her cloak, she covered herself.
ta ce wa bawan, “Wane ne mutumin can a fili, da yake zuwa yă tarye mu?” Bawan ya ce, “Maigidana ne.” Saboda haka ta ɗauki mayafinta to rufe kanta.
66 Then the servant explained to Isaac all that he had done.
Sai bawan ya faɗa wa Ishaku duk abin da ya yi.
67 And he led her into the tent of Sarah his mother, and he accepted her as wife. And he loved her so very much, that it tempered the sorrow which befell him at his mother’s death.
Ishaku ya kawo ta cikin tentin mahaifiyarsa Saratu, ya kuma auri Rebeka. Ta haka ta zama matarsa, ya kuwa ƙaunace ta; Ishaku kuma ya ta’azantu bayan rasuwar mahaifiyarsa.

< Genesis 24 >