< Genesis 23 >

1 Now Sarah lived for one hundred and twenty-seven years.
Saratu ta yi shekara ɗari da ashirin da bakwai a duniya.
2 And she died in the city of Arba, which is Hebron, in the land of Canaan. And Abraham came to mourn and weep for her.
Ta rasu a Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar Kan’ana, Ibrahim kuwa ya tafi ya yi makokin Saratu, yana kuka saboda ita.
3 And when he had risen up from the funeral duties, he spoke to the sons of Heth, saying:
Sai Ibrahim ya tashi daga gefen matarsa da ta mutu, ya yi magana da Hittiyawa. Ya ce,
4 “I am a newcomer and a sojourner among you. Give me the right of a sepulcher among you, so that I may bury my dead.”
“Ni baƙo ne, kuma baƙo a cikinku. Ku sayar mini da wani wuri yă zama wurin binnewa a nan, domin in binne mataccena.”
5 The sons of Heth responded by saying:
Hittiyawa suka ce wa Ibrahim,
6 “Hear us, O lord, you are a leader of God among us. Bury your dead in our chosen sepulchers. And no man shall be able to prohibit you from burying your dead within his memorial.”
“Ranka yă daɗe, ka saurare mu. Kai babban yerima ne a cikinmu. Ka binne mataccenka a kabari mafi kyau na kaburburanmu. Babu waninmu da zai hana ka kabarinsa don binne mataccenka.”
7 Abraham arose, and he reverenced the people of the land, namely, the sons of Heth.
Sai Ibrahim ya tashi ya rusuna a gaban mutanen ƙasar, wato, Hittiyawan.
8 And he said to them: “If it pleases your soul that I should bury my dead, hear me, and intercede on my behalf with Ephron, the son of Zohar,
Ya ce musu, “In kuna so in binne mataccena, sai ku ji ni, ku roƙi Efron ɗan Zohar a madadina
9 so that he may give me the double cave, which he has at the far end of his field. He may transfer it to me for as much money as it is worth in your sight, for the possession of a sepulcher.”
domin yă sayar mini da kogon Makfela, wanda yake nasa, wannan da yake a ƙarshen filinsa. Ku ce masa yă sayar mini a cikakken farashi, yă zama mallakata domin makabarta tsakaninku.”
10 Now Ephron dwelt in the midst of the sons of Heth. And Ephron responded to Abraham in the hearing of everyone who was entering at the gate of his city, saying:
Efron mutumin Hitti yana zaune a cikin mutanensa, sai ya amsa wa Ibrahim a kunnuwan dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birni.
11 “Let it never be so, my lord, but you should pay greater heed to what I say. The field I will transfer to you, and the cave that is in it. In the presence of the sons of my people, bury your dead.”
Ya ce, “A’a, ranka yă daɗe, ka ji ni, na ba ka filin, na kuma ba ka kogon da yake cikinsa. Na ba ka shi a gaban mutanena. Ka binne mataccenka.”
12 Abraham reverenced in the sight of the people of the land.
Ibrahim ya sāke rusuna a gaban mutanen ƙasar
13 And he spoke to Ephron, standing in the midst of the people: “I ask you to hear me. I will give you money for the field. Take it, and so I will bury my dead in it.”
ya ce wa Efron a kunnuwansu, “Ka ji, in ka yarda. Zan biya farashin filin. Ka karɓa daga gare ni don in iya binne mataccena a can.”
14 And Ephron responded: “My lord, hear me.
Efron ya ce wa Ibrahim,
15 The land that you request is worth four hundred shekels of silver. This is the price between me and you. But how much is this? Bury your dead.”
“Ka saurare ni, ranka yă daɗe; darajan filin ya kai shekel ɗari huɗu na azurfa, amma mene ne wannan a tsakanina da kai? Ka binne mataccenka.”
16 And when Abraham had heard this, he weighed out the money that Ephron had requested, in the hearing of the sons of Heth, four hundred shekels of silver, of the approved public currency.
Ibrahim ya yarda da sharuɗan Efron, sai ya auna masa farashin da ya faɗa a kunnuwan Hittiyawa, shekel ɗari huɗu na azurfa, bisa ga ma’aunin da’yan kasuwa suke amfani da shi a lokacin.
17 And having confirmed that the field, in which there was a double cave overlooking Mamre, formerly belonged to Ephron, both it and the sepulcher, and all its trees, with all its surrounding limits,
Ta haka filin Efron a Makfela kusa da Mamre, wato, filin da kogon a cikinsa, da kuma dukan itatuwan da suke cikin iyakoki filin, aka
18 Abraham took it as a possession, in the sight of the sons of Heth and of everyone who was entering at the gate of his city.
ba wa Ibrahim a matsayin mallakarsa a gaban dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birnin.
19 So then, Abraham buried his wife Sarah in the double cave of the field that overlooked Mamre. This is Hebron in the land of Canaan.
Bayan wannan Ibrahim ya binne matarsa Saratu a kogon a filin Makfela kusa da Mamre (wanda yake a Hebron) a ƙasar Kan’ana.
20 And the field was confirmed to Abraham, with the cave that was in it, as a memorial possession before the sons of Heth.
Da filin da kuma kogon da yake cikinsa, Hittiyawa suka tabbatar wa Ibrahim a matsayin makabarta.

< Genesis 23 >