< Genesis 21 >

1 Then the Lord visited Sarah, just as he had promised; and he fulfilled what he had spoken.
Ana nan sai Ubangiji ya nuna wa Saratu alheri kamar yadda ya ce, Ubangiji kuma ya yi wa Saratu abin da ya yi alkawari.
2 And she conceived and gave birth to a son in her old age, at the time that God had foretold to her.
Saratu ta yi ciki, ta kuma haifa wa Ibrahim ɗa a tsufansa; a daidai lokacin da Allah ya yi masa alkawari.
3 And Abraham called the name of his son, whom Sarah bore for him, Isaac.
Ibrahim ya sa wa ɗan da Saratu ta haifa masa suna Ishaku.
4 And he circumcised him on the eighth day, just as God had instructed him,
Sa’ad da ɗansa Ishaku ya kai kwana takwas da haihuwa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, kamar yadda Allah ya umarce shi.
5 when he was one hundred years old. Indeed, at this stage of his father’s life, Isaac was born.
Ibrahim yana da shekara ɗari, sa’ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku.
6 And Sarah said: “God has brought laughter to me. Whoever will hear of it will laugh with me.”
Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, kuma duk wanda ya ji game da wannan, zai yi dariya tare da ni.”
7 And again, she said: “Hearing this, who would believe Abraham, that Sarah breast-fed a son, to whom she gave birth, despite being elderly?”
Ta kuma ƙara da cewa, “Dā, wa zai iya ce wa Ibrahim, Saratu za tă yi renon yara? Duk da haka na haifar masa ɗa cikin tsufansa.”
8 And the boy grew and was weaned. And Abraham made a great feast on the day of his weaning.
Yaron ya yi girma, aka kuma yaye shi, a ranar da aka yaye shi kuwa, Ibrahim ya yi babban biki.
9 And when Sarah had seen the son of Hagar the Egyptian playing with her son Isaac, she said to Abraham:
Amma Saratu ta ga cewa yaron da Hagar, mutuniyar Masar ta haifa wa Ibrahim yana wa ɗanta Ishaku gori,
10 “Cast out this woman servant and her son. For the son of a woman servant will not be heir with my son Isaac.”
sai ta ce wa Ibrahim, “Ka kori baiwan nan tare da ɗanta, saboda ɗan baiwan nan ba zai taɓa raba gādo da ɗana Ishaku ba.”
11 Abraham took this grievously, for the sake of his son.
Al’amarin ya ɓata wa Ibrahim rai sosai domin zancen ya shafi ɗansa.
12 And God said to him: “Let it not seem harsh to you concerning the boy and your woman servant. In all that Sarah has said to you, listen to her voice. For your offspring will be invoked in Isaac.
Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada hankalinka yă tashi game da yaron nan da kuma baiwarka. Ka saurari duk abin da Saratu ta faɗa maka, saboda ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.
13 Yet I will also make the son of the woman servant into a great nation, for he is your offspring.”
Zan ba ɗan baiwan nan al’umma shi ma, domin shi zuriyarka ne.”
14 And so Abraham arose in the morning, and taking bread and a skin of water, he placed it upon her shoulder, and he handed over the boy, and he released her. And when she had departed, she wandered in the wilderness of Beersheba.
Kashegari da sassafe sai Ibrahim ya ɗauki abinci da salkar ruwa, ya ba wa Hagar. Ya ɗora su a kafaɗunta, sa’an nan ya sallame ta da yaron. Ta kama hanyarta ta kuma yi ta yawo a cikin jejin Beyersheba.
15 And when the water in the skin had been consumed, she set aside the boy, under one of the trees that were there.
Sa’ad da ruwan da yake cikin salkan ya ƙare, sai ta ajiye yaron a ƙarƙashin wani ƙaramin itace.
16 And she moved away and sat in a distant area, as far as a bow can reach. For she said, “I shall not see the boy die.” And so, sitting opposite her, he lifted up his voice and wept.
Sai ta tafi, ta zauna ɗan nesa da yaron, misalin nisan harbin baka, gama ta yi tunani ta ce, “Ba zan iya kallon yaron yana mutuwa ba.” Da ta zauna nesa da yaron, sai ta fara kuka.
17 But God heard the voice of the boy. And an Angel of God called to Hagar from heaven, saying: “What are you doing, Hagar? Do not be afraid. For God has heeded the voice of the boy, from the place where he is.
Allah kuwa ya ji yaron yana kuka, sai mala’ikan Allah ya kira Hagar daga sama ya ce mata, “Mene ne damuwarki, Hagar? Kada ki ji tsoro, Allah ya ji yaron yana kuka yayinda yake kwance a can.
18 Rise up. Take the boy and hold him by the hand. For I will make of him a great nation.”
Ki ɗaga yaron ki riƙe shi a hannu, gama zan mai da shi al’umma mai girma.”
19 And God opened her eyes. And seeing a well of water, she went and filled the skin, and she gave the boy to drink.
Sa’an nan Allah ya buɗe idanunta ta ga wata rijiyar ruwa. Don haka sai ta tafi ta cika salkan da ruwa, ta kuma ba wa yaron ruwa ya sha.
20 And God was with him. And he grew, and he stayed in the wilderness, and he became a young man, an archer.
Allah ya kasance da yaron, yayinda yake girma. Ya yi zama a jeji, ya kuma zama maharbi.
21 And he lived in the desert of Paran, and his mother took a wife for him from the land of Egypt.
Yayinda yake zama a Jejin Faran, sai mahaifiyarsa ta samo masa mata daga Masar.
22 At the same time, Abimelech and Phicol, the leader of his army, said to Abraham: “God is with you in everything that you do.
A lokacin nan Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka zo suka ce wa Ibrahim, “Allah yana tare da kai a ko mene ne kake yi.
23 Therefore, swear by God that you will do no harm to me, and to my posterity, and to my stock. But according to the mercy that I have done to you, you will do to me and to the land, to which you have turned as a newcomer.”
Yanzu ka rantse mini a nan a gaban Allah cewa, ba za ka yaudare ni ko’ya’yana ko kuma zuriyata ba. Ka nuna mini alheri, kai da ƙasar da kake zama baƙunci kamar yadda na nuna maka.”
24 And Abraham said, “I will swear.”
Ibrahim ya ce, “Na rantse.”
25 And he reproved Abimelech because of a well of water, which his servants had taken away by force.
Sa’an nan Ibrahim ya kawo kuka ga Abimelek game da rijiyar ruwan da bayin Abimelek suka ƙwace.
26 And Abimelech responded, “I do not know who did this thing, but you also did not reveal it to me, nor have I heard of it, before today.”
Sai Abimelek ya ce, “Ban san wanda ya yi wannan ba. Ba ka faɗa mini ba, ban kuwa taɓa ji ba, sai yau.”
27 And so Abraham took sheep and oxen, and he gave them to Abimelech. And both of them struck a pact.
Sai Ibrahim ya kawo tumaki da shanu ya ba wa Abimelek, sai su biyun suka yi yarjejjeniya.
28 And Abraham set aside seven female lambs from the flock.
Ibrahim ya ware’yan raguna bakwai daga cikin garke,
29 Abimelech said to him, “What purpose have these seven female lambs, which you have caused to stand separately?”
sai Abimelek ya ce wa Ibrahim, “Mene ne ma’anar’yan raguna bakwai da ka keɓe?”
30 But he said, “You will receive seven female lambs from my hand, so that they may be a testimony for me, that I dug this well.”
Ibrahim ya amsa ya ce, “Ka karɓi waɗannan’yan tumaki bakwai daga hannuna a matsayin shaida cewa ni ne na haƙa wannan rijiya.”
31 For this reason, that place was called Beersheba, because there both of them did swear.
Saboda haka aka kira wurin Beyersheba, domin a nan ne su biyun suka yi rantsuwa.
32 And they initiated a pact on behalf of the well of oath.
Bayan da aka yi yarjejjeniya a Beyersheba, sai Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka koma ƙasar Filistiyawa.
33 Then Abimelech and Phicol, the leader of his army, rose up, and they returned to the land of the Palestinians. In truth, Abraham planted a grove in Beersheba, and there he called upon the name of the Lord God Eternal.
Sai Ibrahim ya shuka itacen tsamiya a Beyersheba, a can kuma ya kira bisa sunan Ubangiji, Allah Madawwami.
34 And he was a settler in the land of the Palestinians for many days.
Ibrahim kuwa ya zauna a ƙasar Filistiyawa na dogon lokaci.

< Genesis 21 >