< Ezekiel 47 >

1 And he turned me back to the gate of the house. And behold, waters went out, from under the threshold of the house, toward the east. For the face of the house looked toward the east. But the waters descended on the right side of the temple, toward the south of the altar.
Mutumin ya komo da ni zuwa mashigin haikalin, sai na kuwa ga ruwa yana malalowa daga ƙarƙashin madogarar ƙofar haikalin wajen gabas (gama haikalin yana fuskantar gabas). Ruwan yana malalowa daga ƙarƙashin gefen kudun haikalin, kudu da bagaden.
2 And he led me out, along the way of the north gate, and he turned me back toward the way outside the exterior gate, the way which looked toward the east. And behold, the waters overflowed on the right side.
Sai ya fitar da ni ta ƙofar arewa ya kewaye da ni ta waje zuwa ƙofar da take waje mai fuskantar gabas, ruwan kuwa yana malalowa daga wajen kudu.
3 Then the man who held the rope in his hand departed toward the east, and he measured one thousand cubits. And he led me forward, through the water, up to the ankles.
Yayinda mutumin ya yi wajen gabas da karan awo a hannunsa, sai ya auna kamu dubu ya kuma bi da ni ta ruwan da zurfinsa ya kama ni a idon ƙafa.
4 And again he measured one thousand, and he led me forward, through the water, up to the knees.
Ya auna wani kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa ya kai ni gwiwa. Ya sāke auna kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa kama ni a gindi.
5 And he measured one thousand, and he led me forward, through the water, up to the waist. And he measured one thousand, into a torrent, through which I was not able to pass. For the waters had risen to become a profound torrent, which was not able to be crossed.
Ya auna wani kamu dubu, amma a yanzu ruwan ya zama kogin da ban iya hayewa ba, domin ruwan ya taso ya kuma yi zurfin da ya isa a yi iyo a ciki, kogin da ba za a iya hayewa ba.
6 And he said to me: “Son of man, certainly you have seen.” And he led me out, and he turned me back to the bank of the torrent.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga wannan?” Sa’an nan ya komo da ni zuwa bakin kogin.
7 And when I had turned myself around, behold, on the bank of the torrent, there were very many trees on both sides.
Sa’ad da na iso can, sai na ga itatuwa masu yawa a kowane gefen kogin.
8 And he said to me: “These waters, which go forth toward the hillocks of sand to the east, and which descend to the plains of the desert, will enter the sea, and will go out, and the waters will be healed.
Sai ya ce mini, “Wannan ruwa yana malalowa zuwa yankin gabas ya kuma gangaro zuwa cikin Araba, inda zai shiga Teku. Sa’ad da ya shiga cikin Tekun sai ruwan a can ya zama mai daɗi.
9 And every living soul that moves, wherever the torrent arrives, will live. And there will be more than enough fish, after these waters have arrived there, and they will be healed. And all things will live, where the torrent arrives.
Tarin halittu masu rai za su rayu a duk inda ruwan ya malalo. Za a kasance da kifi masu yawa, domin wannan ruwa yana malalowa a can yana kuma mai da ruwan gishiri yă zama ruwa mai daɗi; saboda haka duk inda ruwan ya malalo, kome zai rayu.
10 And fishermen will stand over these waters. There will be the drying of nets, from Engedi even to Eneglaim. There will be very many kinds of fish within it: a very great multitude, like the fish of the great sea.
Masunta za su tsaya a gaɓar; daga En Gedi zuwa En Eglayim, za a kasance da wuraren jefa abin kamun kifi. Za a sami kifayen iri-iri, kamar kifaye Bahar Rum.
11 But on its shore and in the marshes, they will not be healed. For these will be made into salt pits.
Amma fadamun da tafkunan ba za su zama masu daɗi ba; za a bar su a gishirinsu.
12 And above the torrent, on its banks on both sides, every kind of fruit tree will rise up. Their foliage will not fall away, and their fruit will not fail. Every single month they will bring forth first-fruits. For its waters will go forth from the sanctuary. And its fruits will be for food, and its leaves will be for medicine.”
’Ya’yan itatuwa na kowane iri za su yi girma a kowane gefen kogin. Ganyayensu ba su bushe ba, ba kuwa za su fasa yin’ya’ya ba. Kowane wata za su ba da’ya’ya domin ruwa daga wuri mai tsarki yana malalo musu.’Ya’yansu za su zama abinci, ganyayensu kuma za su zama magani.”
13 Thus says the Lord God: “This is the border, by which you shall possess the land, in accord with the twelve tribes of Israel. For Joseph shall have a double portion.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Waɗannan su ne iyakokin da za ku raba ƙasar gādo cikin kabilan Isra’ila goma sha biyu, da rabo biyu don Yusuf.
14 And you shall possess it, each one in equal manner as his brother. I lifted up my hand over it, so that I might give it to your fathers. And this land shall fall to you as a possession.
Za ku raba ta daidai a cikinsu. Gama na ɗaga hannu na rantse zan ba da ita ga kakanninku, wannan ƙasa za tă zama gādonku.
15 Now this is the border of the land toward the northern region, from the great sea, by the way of Hethlon, arriving at Zedad:
“Wannan ce za tă zama iyakar ƙasa. “A wajen arewa za tă fara daga Bahar Rum ta hanyar Hetlon ta wuce Lebo Hamat zuwa Zedad,
16 Hamath, Berothah, Sibraim, which is between the border of Damascus and the confines of Hamath, the house of Ticon, which is beside the border of Hauran,
Berota da Sibrayim (wadda take a iyaka tsakanin Damaskus da Hamat), har zuwa Hazer-Hattikon, wadda take a iyakar Hauran.
17 and the border will be from the sea, even to the entrance of Enon, at the border of Damascus, and from the north to the north, at the border of Hamath, on the northern side.
Iyakar za tă miƙe daga teku zuwa Hazar-Enon, ta iyakar Damaskus, da iyakar Hamat a arewa. Wannan ita ce iyakar a wajen arewa.
18 Moreover, the eastern region will be from the midst of Hauran, and from the midst of Damascus, and from the midst of Gilead, and from the midst of the land of Israel, to the Jordan, marking the boundary to the eastern sea. For so shall you measure the eastern region.
A wajen gabas iyakar za tă kama tsakanin Hauran da Damaskus, ta bi ta Urdun tsakanin Gileyad da ƙasar Isra’ila, zuwa tekun gabas har zuwa Tamar. Wannan ita ce iyakar a wajen gabas.
19 Now the southern region, toward the meridian, will be from Tamar, even to the Waters of Contradiction at Kadesh, and from the Torrent, even to the great sea. And this is the southern region, toward the meridian.
A wajen kudu za tă fara daga Tamar har zuwa ruwan Meriba Kadesh, sa’an nan ta bi Rafin Masar zuwa Bahar Rum. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu.
20 And the region toward the sea will have its confines from the great sea continuing directly until one arrives at Hamath. This is the region of the sea.
A wajen yamma, Bahar Rum ne zai zama iyakar zuwa wani wuri ɗaura da Lebo Hamat. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.
21 And you shall divide this land among yourselves according to the tribes of Israel.
“Za ku rarraba wannan ƙasa a tsakaninku bisa ga kabilan Isra’ila.
22 And you shall distribute it by lot as an inheritance, for yourselves and for the new arrival who will be added to you, who will conceive sons in your midst. And they shall be to you as the indigenous among the sons of Israel. They shall divide the possession with you, in the midst of the tribes of Israel.
Za ku raba ta kamar gādo wa kanku da kuma wa baƙin da suka zauna a cikinku waɗanda suke da’ya’ya. Za ku ɗauka su kamar’yan ƙasa haifaffun Isra’ilawa; za su yi gādo tare da ku a cikin kabilan Isra’ila.
23 And in whatever tribe the new arrival will be, there you shall give a possession to him, says the Lord God.”
A duk kabilar da baƙon yake zama, a can za ku ba shi gādonsa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.

< Ezekiel 47 >