< Ezekiel 46 >

1 Thus says the Lord God: “The gate of the inner court which looks toward the east shall be closed for the six days on which work is done. Then, on the Sabbath day, it shall be opened. But also on the day of the new moon, it shall be opened.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a rufe ƙofa ta fili na can cikin da take fuskantar gabas ranaku shida na aiki, amma a ranar Asabbaci da kuma a ranar ganin Sabuwar Wata a buɗe ta.
2 And the prince shall enter from outside, by the way of the vestibule of the gate, and he shall stand at the threshold of the gate. And the priests shall offer his holocaust and his peace offerings. And he shall adore upon the threshold of the gate, and then depart. But the gate shall not be closed until evening.
Sarki zai shiga daga waje ta shirayin hanyar shiga yă tsaya a madogarar ƙofa. Firistoci za su miƙa hadayarsa ta ƙonawa da hadayunsa na salama. Zai yi sujada a madogarar ƙofar hanyar shiga sa’an nan ya fita, amma ba za a rufe ƙofar ba sai da yamma.
3 And the people of the land shall adore at the entrance of the same gate, on the Sabbaths and on the new moons, in the sight of the Lord.
A Asabbatai da kuma a Sabuwar Wata mutanen ƙasar za su yi sujada a gaban Ubangiji a mashigin wannan hanyar shiga.
4 Now this holocaust, which the prince shall offer to the Lord on the Sabbath day, shall be six immaculate lambs, and one immaculate ram.
Hadaya ta ƙonawar da sarki ya kawo wa Ubangiji a ranar Asabbaci’yan raguna shida ne da rago guda, dukansu marasa lahani.
5 The sacrifice shall be one ephah for each ram. But for the lambs, the sacrifice shall be whatever his hand shall give. And there shall be one hin of oil for each ephah.
Hadayar garin da aka bayar tare da ragon efa guda ne, hadayar garin da’yan ragunan yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
6 Then, on the day of the new moon, he shall offer one immaculate calf from the herd. Both the six lambs and the rams shall be immaculate.
A ranar Sabuwar Wata zai miƙa ɗan bijimi,’yan raguna guda shida da kuma rago guda, dukansu marasa lahani.
7 And he shall offer the sacrifice of one ephah for each calf, and also one ephah for each ram. But for the lambs, it shall be just as his hand will find. And there shall be one hin of oil for each ephah.
Zai tanada a matsayin hadaya ta gari, efa guda tare da bijimi, efa guda tare da’yan raguna, da kuma’yan raguna yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
8 And when the prince will enter, let him enter by the way of the vestibule of the gate, and let him go out by the same way.
Sa’ad da sarki zai shiga, zai shiga ta shirayin hanyar shiga, zai kuma fita ta nan.
9 And when the people of the land will enter in the sight of the Lord on the solemnities, whoever enters by the north gate so that he may adore, shall depart by the way of the south gate. And whoever enters by the way of the south gate shall depart by the way of the north gate. He shall not return by way of the gate through which he entered. Instead, he shall depart from the direction opposite to it.
“‘Sa’ad da mutanen ƙasar suka zo gaban Ubangiji a ƙayyadaddun bukukkuwa, duk wanda ya shiga ta ƙofar arewa don yă yi sujada sai ya fita ta ƙofar kudu; kuma duk wanda ya shiga ta ƙofar kudu sai ya fita ta ƙofar arewa. Ba wanda zai koma ta ƙofar da ya shiga, amma kowa zai fita a ƙofar ɗaura da wadda ya shiga.
10 But the prince in their midst shall enter when they enter, and he shall depart when they depart.
Sarki zai kasance a cikinsu, zai shiga sa’ad da suke shiga ya kuma fita sa’ad da suka fita.
11 And during the feasts and the solemnities, there shall be the sacrifice of one ephah for each calf, and one ephah for each ram. But for the lambs, the sacrifice shall be just as his hand will find. And there shall be one hin of oil for each ephah.
“‘A bukukkuwa da ƙayyadaddun bukukkuwa, hadaya ta gari zai zama efa tare da bijimi, efa da rago, da kuma’yan raguna da ya ga dama, haɗe da kwalabar mai.
12 But when the prince will offer a voluntary holocaust or a voluntary peace offering to the Lord, the gate which looks toward the east shall be opened to him. And he shall offer his holocaust and his peace offerings, just as is usually done on the Sabbath day. And he shall depart, and the gate shall be closed after he has gone out.
Sa’ad da sarki ya ba da hadaya ta yardar rai ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa ce ko hadayun salama ne, sai a buɗe masa ƙofar da take fuskantar gabas. Zai miƙa hadayarsa ta ƙonawa ko hadayarsa ta salama yadda yakan yi a ranar Asabbaci. Sa’an nan ya fita, bayan kuma ya fita, sai a rufe ƙofar.
13 And daily he shall offer, as a holocaust to the Lord, an immaculate lamb of the same age. He shall offer it always in the morning.
“‘Kullum za ku tanada ɗan rago bana ɗaya marar lahani don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji; kowace safiya za ku tanada shi.
14 And he shall offer as a sacrifice with it, morning after morning, one sixth part of an ephah, and one third part of a hin of oil, to be mixed with the fine flour, as a sacrifice to the Lord, by a continual and everlasting ordinance.
Tare da shi za ku tanada hadaya ta gari kowace safiya, da ya haɗa da kashi ɗaya bisa shida na efa tare da kashi ɗaya bisa uku na mai ga garin da aka cuɗa. Miƙawar wannan hadaya ta gari ga Ubangiji dawwammamiyar farilla ce.
15 He shall offer the lamb and the sacrifice and the oil, morning after morning, as an everlasting holocaust.
Saboda haka za a tanada ɗan rago da hadaya ta gari da kuma mai kowace safiya don hadaya ta ƙonawa ta kullum.
16 Thus says the Lord God: If the prince grants a gift to any of his sons, the inheritance of it will go to his sons; they shall possess it as an inheritance.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa in sarkin ya ba wa ɗaya daga cikin’ya’yansa kyauta daga gādonsa, zai kuwa zama na zuriyar; zai kuwa zama mallakarsu ta wurin gādo.
17 But if he grants a legacy from his inheritance to one of his servants, it shall be his only until the year of remission, and then it shall be returned to the prince. For his inheritance shall go to his sons.
In kuma ya ba wa ɗaya daga cikin bayinsa kyauta daga gadonsa, bawan zai iya riƙe shi sai shekarar’yantarwa; sa’an nan ya mayar wa sarkin. Gādon sarki na’ya’yansa maza ne kaɗai; na su ne.
18 And the prince shall not take from the inheritance of the people by force, nor from their possession. Instead, from his own possession, he shall give an inheritance to his sons, so that my people will not be scattered, each one from his possession.”
Kada sarki ya ƙwace gādon mutane, yana korinsu daga mallakarsu. Zai ba wa’ya’yansa maza gādonsu daga cikin mallakarsa, don kada a raba wani daga mutanena da mallakarsa.’”
19 And he led me in by the entrance which was at the side of the gate, into the storerooms of the sanctuary for the priests, which looked toward the north. And there was a place there which verged toward the west.
Sa’an nan mutumin ya fitar da ni ta ƙofar shiga a gefen ƙofar zuwa tsarkakakkun ɗakuna waɗanda suke fuskantar arewa, waɗanda suke na firistoci, ya kuma nuna mini wani wuri daga can ƙurewar yamma.
20 And he said to me: “This is the place where the priests will cook the offering for sin and the offering for trespasses. Here, they shall cook the sacrifice, so that they need not carry it to the outer court, and so that the people may be sanctified.”
Ya ce mini, “Wannan shi ne wurin da firistoci za su dafa hadaya don laifi, da hadaya don zunubi, a nan ne kuma za su toya hadaya ta gari, domin kada su kai su a filin da yake waje, su tsarkake mutane.”
21 And he led me away to the outer court, and he led me around by the four corners of the court. And behold, there was a little atrium at the corner of the court; a little atrium was at each corner of the court.
Sa’an nan ya kawo ni filin da yake waje ya kuma bi da ni kewaye da kusurwoyi huɗunsa, na kuma ga kowace kusurwa na wani fili.
22 At the four corners of the court, little atriums were positioned, forty cubits in length, and thirty in width; each of the four were of the same measure.
A kusurwoyi huɗu na filin da yake waje akwai waɗansu filaye a haɗe, tsawonsu kamu arba’in fāɗinsu kuwa kamu talatin; kowane fili a kusurwoyi huɗun nan girmansu ɗaya ne.
23 And there was a wall all around, encircling the four little atriums. And kitchens had been constructed under the porticos on all sides.
Kewaye da cikin kowane filin huɗun nan akwai ginin dutse, da murhu da aka gina a kewaye a ƙarƙashin ginin.
24 And he said to me: “This is the house of the kitchens, in which the ministers of the house of the Lord will cook the victims of the people.”
Sai ya ce mini, “Waɗannan su ne ɗakunan dahuwa inda masu hidima a haikali za su dafa hadayun da jama’a.”

< Ezekiel 46 >