< Ezekiel 35 >

1 And the word of the Lord came to me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Son of man, set your face against mount Seir, and you shall prophesy about it, and you shall say to it:
“Ɗan mutum, ka fuskanci Dutsen Seyir; ka yi annabci a kansa
3 Thus says the Lord God: Behold, I am against you, mount Seir, and I will extend my hand over you, and I will make you desolate and deserted.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, Dutsen Seyir, zan kuma miƙa hannuna gāba da kai in mai da kai kango.
4 I will tear down your cities, and you will be deserted. And you shall know that I am the Lord.
Zan mai da garuruwanka kufai za ka kuma zama kango. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
5 For you have been a continual adversary, and you have enclosed the sons of Israel, by the hands of the sword, in the time of their affliction, in the time of extreme iniquity.
“‘Domin ka riƙe ƙiyayya ta tun dā, ka kuma ba da mutanen Isra’ila domin a kashe su da takobi a lokacin masifarsu, lokacin da adadin horonsu ya cika,
6 Because of this, as I live, says the Lord God, I will hand you over to blood, and blood will pursue you. Even though you have hated blood, blood will pursue you.
saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sa a zub da jininka zan kuwa fafare ka. Da yake ba ka ƙi zub da jini ba, zub da jini zai fafare ka.
7 And I will make mount Seir desolate and deserted. And I will take away from it the one who departs and the one who returns.
Zan mai da Dutsen Seyir kango in kuma yanke dukan waɗanda suke shiga da fita a cikinka.
8 And I will fill up its mountains with its slain. In your hills, and in your valleys, as well as in your torrents, the slain will fall by the sword.
Zan cika duwatsunka da matattu; waɗanda aka kashe da takobi za su fāɗi a kan tuddanka, da cikin kwarurukanka, da cikin dukan kwazazzabanka.
9 I will hand you over to everlasting desolations, and your cities will not be inhabited. And you shall know that I am the Lord God.
Zan mai da kai kango har abada; ba za a zauna a cikin garuruwanka ba. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
10 For you have said, ‘Two nations and two lands will be mine, and I will possess them as an inheritance,’ though the Lord was in that place.
“‘Domin kun ce, “Waɗannan al’ummai biyu da ƙasashe za su zama namu za mu kuma mallake su,” ko da yake Ni Ubangiji ina a can,
11 Because of this, as I live, says the Lord God, I will act in accord with your own wrath, and in accord with your own zeal, by which you have acted with hatred toward them. And I will be made known by them, when I will have judged you.
saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sāka maka gwargwadon fushi da kuma kishin da ka nuna a ƙiyayyarsu da ka yi zan kuma sanar da kaina a cikinsu sa’ad da na hukunta ka.
12 And you shall know that I, the Lord, have heard all your disgraces, which you have spoken about the mountains of Israel, saying: ‘They are deserted. They have been given to us to devour.’
Sa’an nan za ka san cewa Ni Ubangiji na ji duk abubuwan banzan da ka faɗa a kan duwatsun Isra’ila. Ka ce, “An mai da su kango an kuma ba mu su mu cinye.”
13 And you rose up against me with your mouth, and you disparaged against me with your words. I have heard.
Ka yi fariya a kaina, ka kuma yi magana a kaina ba gaggautawa, na ji shi sarai.
14 Thus says the Lord God: When the whole earth will rejoice, I will reduce you to solitude.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa yayinda dukan duniya take farin ciki, zan mai da kai kango.
15 Just as you have rejoiced over the inheritance of the house of Israel, when it was laid waste, so will I act toward you. You will be laid waste, O mount Seir, with all of Idumea. And they shall know that I am the Lord.”
Domin ka yi farin ciki sa’ad da gādon gidan Isra’ila ya zama kufai, haka zan yi da kai, ya Dutsen Seyir, kai da dukan Edom. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”

< Ezekiel 35 >