< Ezekiel 37 >

1 The hand of the Lord was set upon me, and he led me away in the Spirit of the Lord, and he released me in the midst of a plain which was full of bones.
Hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma fitar da ni ta wurin Ruhun Ubangiji ya sa ni a tsakiyar kwarin; yana cike da ƙasusuwa.
2 And he led me around, through them, on every side. Now they were very many upon the face of the plain, and they were exceedingly dry.
Ya sa na kai na komo a ciki, na kuma ga ƙasusuwa masu girma da yawa a ƙasar kwarin, ƙasusuwan da suka bushe ƙwarai.
3 And he said to me, “Son of man, do you think that these bones will live?” And I said, “O Lord God, you know.”
Sai ya tambaye ni cewa, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa za su iya rayu?” Ni kuwa na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai kaɗai ka sani.”
4 And he said to me, “Prophesy about these bones. And you shall say to them: Dry bones, listen to the word of the Lord!
Sai ya ce mini, “Ka yi wa waɗannan ƙasusuwa annabci ka ce musu, ‘Busassun ƙasusuwa, ku ji maganar Ubangiji!
5 Thus says the Lord God to these bones: Behold, I will send spirit into you, and you shall live.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa waɗannan ƙasusuwa. Zan sa numfashi ya shiga muku, za ku kuwa rayu.
6 And I will set sinews upon you, and I will cause flesh to grow over you, and I will extend skin over you. And I will give you spirit, and you shall live. And you shall know that I am the Lord.”
Zan harhaɗa muku jijiyoyi in sa muku tsoka in kuma rufe ku da fata; zan sa numfashi a cikinku, za ku kuwa rayu. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
7 And I prophesied, just as he had instructed me. But a noise occurred, as I was prophesying, and behold: a commotion. And the bones joined together, each one at its joint.
Saboda haka sai na yi annabci yadda aka umarce ni. Da nake annabcin, sai aka ji motsi, ƙarar girgiza, sai ƙasusuwan suka harhaɗu, ƙashi ya haɗu da ƙashi.
8 And I saw, and behold: sinews and flesh rose up over them; and skin was extended over them. But they had no spirit within them.
Na duba, sai ga jijiyoyi da nama suka bayyana a kansu fata kuma ta rufe su, amma ba numfashi a cikinsu.
9 And he said to me: “Prophesy to the spirit! Prophesy, O son of man, and you shall say to the spirit: Thus says the Lord God: Approach, O spirit, from the four winds, and blow across these ones who were slain, and revive them.”
Sa’an nan ya ce mini, “Ka yi annabci wa numfashi; ka yi annabci, ɗan mutum, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka fito daga kusurwoyi huɗu, ya numfashi, ka kuma numfasa cikin waɗannan matattu, don su rayu.’”
10 And I prophesied, just as he had instructed me. And spirit entered into them, and they lived. And they stood upon their feet, an exceedingly great army.
Saboda haka na yi annabci yadda aka umarce ni, sai numfashi ya shiga musu; suka rayu suka kuma miƙe tsaye a ƙafafunsu babbar runduna ce ƙwarai.
11 And he said to me: “Son of man: All these bones are the house of Israel. They say: ‘Our bones are dried out, and our hope has perished, and we have been cut off.’
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa su ne dukan gidan Isra’ila. Suna cewa, ‘Ƙasusuwanmu sun bushe, sa zuciyarmu duk ya tafi; an share mu ƙaf.’
12 Because of this, prophesy, and you shall say to them: Thus says the Lord God: Behold, I will open your tombs, and I will lead you away from your sepulchers, O my people. And I will lead you into the land of Israel.
Saboda haka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ya mutanena, zan buɗe kaburburanku in fitar da ku daga cikinsu; zan mai da ku ƙasar Isra’ila.
13 And you shall know that I am the Lord, when I will have opened your sepulchers, and when I will have led you away from your tombs, O my people.
Sa’an nan ku, mutanena, za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na buɗe kaburburanku na fitar da ku daga cikinsu.
14 And I will place my Spirit within you, and you shall live. And I will cause you to rest upon your own soil. And you shall know that I, the Lord, have spoken and acted, says the Lord God.”
Zan sa Ruhuna a cikinku za ku kuwa rayu, zan kuma zaunar da ku a ƙasarku. Sa’an nan za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata, in ji Ubangiji.’”
15 And the word of the Lord came to me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
16 “And as for you, son of man, take up a piece of wood for yourself, and write upon it: ‘For Judah, and for the sons of Israel, his companions.’ And take up another piece of wood, and write upon it: ‘For Joseph, the wood of Ephraim, and for the entire house of Israel, and for his companions.’
“Ɗan mutum, ka ɗauki sanda ka rubuta a kansa, ‘Na Yahuda da Isra’ilawan da suke tare da shi.’ Sa’an nan ka ɗauki wani sanda, ka rubuta a kansa, ‘Sandan Efraim, na Yusuf da dukan gidan Isra’ilan da suke tare da shi.’
17 And join these, one to the other, for yourself, as one piece of wood. And they will be united in your hand.
Ka haɗa su su zama sanda guda saboda su kasance ɗaya a hannunka.
18 Then, when the sons of your people will speak to you, saying: ‘Will you not tell us what you intend by this?’
“In mutanen ƙasarka suka tambaye ka cewa, ‘Ba za ka faɗa mana abin da kake nufi da wannan ba?’
19 you shall say to them: Thus says the Lord God: Behold, I will take up the wood of Joseph, which is in the hand of Ephraim, and the tribes of Israel, which are joined to him, and I will put them together with the wood of Judah, and I will make them one piece of wood. And they will be one in his hand.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, Zan ɗauki sandan Yusuf, wanda yake a hannun Efraim, da na kabilan Isra’ilawan da suke tare da shi, in haɗa shi da sandan Yahuda, in mai da su sanda guda, za su kuwa zama ɗaya a hannuna.’
20 Then the pieces of wood, on which you have written, will be in your hand, before their eyes.
Ka riƙe sandunan da ka yi rubutun a gabansu
21 And you shall say to them: Thus says the Lord God: Behold, I will take up the sons of Israel, from the midst of the nations to which they have gone, and I will gather them together on every side, and I will lead them onto their own soil.
ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan fitar da Isra’ilawa daga al’ummai inda suka tafi. Zan tattara su daga dukan kewaye in komo da su ƙasarsu.
22 And I will make them one nation in the land, on the mountains of Israel, and one king will be ruler over all. And they will no longer be two nations, nor will they be divided any more into two kingdoms.
Zan mai da su al’umma ɗaya a cikin ƙasar, a kan duwatsun Isra’ila. Za a kasance da sarki guda a kan dukansu ba za su ƙara zama al’ummai biyu ko su rabu su zama masarautai biyu ba.
23 And they will no longer be defiled by their idols, and by their abominations, and by all their iniquities. And I will save them, out of all the settlements in which they have sinned, and I will cleanse them. And they will be my people, and I will be their God.
Ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumaka da mugayen siffofi ko kuma da wani daga laifofinsu ba, gama zan cece su daga dukan zunubinsu na ridda, zan kuma tsarkake su. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu.
24 And my servant David shall be the king over them, and they shall have one shepherd. They shall walk in my judgments, and they shall keep my commandments, and they shall do them.
“‘Bawana Dawuda zai zama sarki a kansu, dukansu kuwa za su kasance da makiyayi guda. Za su bi dokokina su kuma kiyaye ƙa’idodina.
25 And they shall live upon the land that I gave to my servant Jacob, in which your fathers lived. And they shall live upon it, they and their sons, and the sons of their sons, even for all time. And David, my servant, shall be their leader, in perpetuity.
Za su zauna a ƙasar da na ba wa bawana Yaƙub, ƙasar da kakanninsu suka zauna. Su da’ya’yansu da’ya’ya’ya’yansu za su zauna a can har abada, kuma Dawuda bawana zai zama sarkinsu har abada.
26 And I will strike a covenant of peace with them. This will be an everlasting covenant for them. And I will establish them, and multiply them. And I will set my sanctuary in their midst, unceasingly.
Zan yi alkawarin salama da su; zai zama madawwamin alkawari. Zan kafa su in ƙara yawansu, zan kuma sa wuri mai tsarkina a cikinsu har abada.
27 And my tabernacle shall be among them. And I will be their God, and they will be my people.
Mazaunina zai kasance da su; zan kuwa zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
28 And the Gentiles shall know that I am the Lord, the Sanctifier of Israel, when my sanctuary will be in their midst, forever.”
Sa’an nan al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji na mai da Isra’ila mai tsarki, sa’ad da wuri mai tsarkina yana a cikinsu har abada.’”

< Ezekiel 37 >