< Exodus 2 >

1 After these things, a man from the house of Levi went out, and he took a wife from his own stock.
Ana nan, sai wani Balawe ya auri wata Balawiya,
2 And she conceived and bore a son. And seeing him to be handsome, she hid him for three months.
ta kuwa yi ciki, ta haifi ɗa. Sa’ad da ta ga jaririn kyakkyawa ne, sai ta ɓoye shi har watanni uku.
3 And when she was no longer able to hide him, she took a small basket woven of bulrushes, and she smeared it with pitch as well as tar. And she placed the little infant inside, and she laid him in the sedges by the bank of the river.
Amma da ba tă iya ɓoye shi kuma ba, sai ta yi kwandon kyauro ta shafa masa kwalta. Bayan haka sai ta sa jaririn a cikin kwandon, ta je ta ajiye kwandon tare da jaririn a cikin kyauro, a bakin kogin.
4 His sister was standing at a distance and was wondering what would happen.
’Yar’uwarsa ta tsaya da ɗan rata tana lura da abin da zai faru da shi.
5 Then, behold, the daughter of Pharaoh descended to wash in the river. And her maids walked along the edge of the cove. And when she had seen the small basket among the papyruses, she sent one of her servants for it. And when it was brought,
Sai’yar Fir’auna ta gangara zuwa kogi domin tă yi wanka, bayinta kuwa suna tafiya a bakin kogi. Sai ta ga kwandon a ciyawa, ta aiki ɗaya daga cikin masu hidimarta tă ɗauko mata.
6 she opened it; and realizing that within it was a little one crying, she took pity on him, and she said: “This is one of the infants of the Hebrews.”
Da ta buɗe kwandon, sai ta ga yaro yana kuka, ta kuwa ji tausayinsa. Ta ce, “Wannan ɗaya daga cikin jariran Ibraniyawa ne.”
7 And the sister of the boy said to her: “If you wish, I will go and call to you a Hebrew woman, who will be able nurse the infant.”
Sai’yar’uwarsa ta tambayi’yar Fir’auna, ta ce, “In tafi in samo ɗaya daga cikin matan Ibraniyawa tă yi miki renon yaron?”
8 She responded, “Go.” The maid went directly and called her mother.
Sai ta amsa ta ce, “I, tafi.” Sai yarinyar ta tafi ta kawo mahaifiyar yaron.
9 And the daughter of Pharaoh said to her: “Take this boy and nurse him for me. I will give you your wages.” The woman took and nursed the boy. And when he was mature, she delivered him to the daughter of Pharaoh.
Diyar Fir’auna ta ce mata, “Ɗauki jaririn, ki yi mini renonsa, zan kuwa biya ki.” Saboda haka ta ɗauki yaron, ta yi renonsa.
10 And she adopted him in place of a son, and she called his name Moses, saying, “Because I took him from the water.”
Sa’ad da ya yi girma, sai ta kawo shi wajen’yar Fir’auna, ya kuwa zama ɗanta, ta kuma ba shi suna Musa, tana cewa, “Na tsamo shi daga ruwa.”
11 In those days, after Moses had grown up, he went out to his brothers. And he saw their affliction and an Egyptian man striking a certain one of the Hebrews, his brothers.
Wata rana, bayan Musa ya yi girma, sai ya haura, ya tafi inda mutanensa suke, ya kuma ga yadda suke shan wahala da aiki. Ya ga wani mutumin Masar yana dūkan mutumin Ibraniyawa, ɗaya daga cikin mutanensa.
12 And when he had looked around this way and that, and had seen no one nearby, he struck down the Egyptian and hid him in the sand.
Da ya leƙa nan da can bai kuwa ga kowa ba, sai ya kashe mutumin Masar, ya ɓoye shi a yashi.
13 And going out the next day, he spotted two Hebrews quarrelling violently. And he said to him who was causing the injury, “Why do you strike your neighbor?”
Kashegari ya fita, sai ya ga Ibraniyawa biyu suna faɗa. Ya tambayi mai laifin ya ce, “Don me kake bugun ɗan’uwanka, mutumin Ibraniyawa?”
14 But he responded: “Who appointed you as leader and judge over us? Do you want to kill me, just as yesterday you killed the Egyptian?” Moses was afraid, and he said, “How has this word become known?”
Mutumin ya ce masa, “Wa ya mai da kai mai mulki da mai hukunci a kanmu? Kana so ne ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan?” Sai Musa ya tsorata, ya yi tunani ya ce, “To, fa, abin nan da na yi, ya zama sananne.”
15 And Pharaoh heard this talk, and he sought to kill Moses. But fleeing from his sight, he stayed in the land of Midian, and he sat down next to a well.
Da Fir’auna ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă kashe Musa, amma Musa ya gudu daga wajen Fir’auna, ya tafi ƙasar Midiyan inda ya zauna kusa da wata rijiya.
16 Now there was a priest of Midian with seven daughters, who came to draw water. And having filled the troughs, they desired to water their father’s flocks.
To, fa, akwai wani firist na Midiyan, yana da’ya’ya mata bakwai, suka zo su shayar da dabbobin mahaifinsu.
17 The shepherds overcame them and drove them away. And Moses rose up, and defending the girls, he watered their sheep.
Sai waɗansu makiyaya suka zo suka kore su, amma Musa ya tashi ya taimake su ya shayar da dabbobinsu.
18 And when they had returned to their father, Reuel, he said to them, “Why have you arrived sooner than usual?”
Da’yan matan suka komo wurin Reyuwel mahaifinsu, sai ya tambaye su ya ce, “Yaya kuka dawo da wuri yau?”
19 They responded: “A man of Egypt freed us from the hands of the shepherds. Moreover, he also drew water with us and gave the sheep to drink.”
Suka amsa suka ce, “Wani mutumin Masar ne ya taimake mu daga hannun waɗansu makiyaya. Har ma ya ɗebo ruwa ya shayar da dabbobin.”
20 But he said: “Where is he? Why have you dismissed the man? Call him, so that he may eat bread.”
Ya tambayi’yan matansa, “To ina yake? Don me kuka bar shi a can? A gayyace shi, yă zo, yă ci wani abu.”
21 Therefore, Moses swore that he would live with him. And he accepted his daughter Zipporah as a wife.
Musa ya yarda yă zauna da mutumin wanda ya ba da’yarsa Ziffora aure da Musa.
22 And she bore a son to him, whom he called Gershom, saying, “I have been a newcomer in a foreign land.” In truth, she bore another, whom he called Eliezer, saying, “For the God of my father, my helper, has rescued me from the hand of Pharaoh.”
Ziffora ta haifi wa Musa ɗa, ya kuma raɗa masa suna Gershom cewa, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa.”
23 In truth, after a long time, the king of Egypt was dead. And the sons of Israel, groaning, cried out because of the works. And their cry ascended to God from the works.
Ana nan dai, a kwana a tashi, sai sarkin Masar ya mutu. Isra’ilawa suka yi kuka mai zafi saboda bautarsu mai wuya, sai kukar neman taimakonsu saboda bauta, ya kai wurin Allah.
24 And he heard their groaning, and he also remembered the covenant which he formed with Abraham, Isaac, and Jacob.
Allah kuwa ya ji kukansu sai ya tuna da alkawarinsa da Ibrahim da Ishaku da Yaƙub.
25 And the Lord looked with favor on the sons of Israel, and he knew them.
Sai Allah ya dubi Isra’ilawa, ya kuma damu da su.

< Exodus 2 >