< Exodus 15 >

1 Then Moses and the sons of Israel sang this song to the Lord, and they said: “Let us sing to the Lord, for he has been gloriously magnified: the horse and the rider he has cast into the sea.
Sa’an nan Musa da Isra’ilawa suka rera wannan waƙa ga Ubangiji suka ce, “Zan rera waƙa ga Ubangiji gama an ɗaukaka shi ƙwarai. Doki da mahayinsa ya jefa su cikin teku.
2 The Lord is my strength and my praise, and he has become my salvation. He is my God, and I shall glorify him. He is the God of my father, and I shall exalt him.
“Ubangiji ne ƙarfina da mafakata, ya zama cetona. Shi Allahna ne, zan yabe shi. Allah na kakana, zan ɗaukaka shi.
3 The Lord is like a fighting man. Almighty is his name.
Ubangiji mai yaƙi ne Ubangiji ne sunansa.
4 The chariots of Pharaoh, and his army, he has cast into the sea; his elect leaders have been submerged in the Red Sea.
Karusan Fir’auna da sojojinsa ya jefa cikin teku. Zaɓaɓɓun jarumawansa ya nutsar da su cikin Bahar Maliya.
5 The abyss has covered them. They descended into the depths like a stone.
Zurfafan ruwaye sun rufe su; suka nutse cikin zurfi kamar dutse.
6 Your right hand, O Lord, has been magnified in strength. Your right hand, O Lord, has struck down the enemy.
Hannun damanka, ya Ubangiji, Mai kwarjini ne da iko, hannun damanka, ya Ubangiji, ya farfashe magabci.
7 And in the multitude of your glory you have put down your adversaries. You sent out your wrath, which devoured them like stubble.
“A cikin girman kwarjininka ka kā da waɗanda sun yi gāba da kai. Ka aiki fushinka mai zafi ya cinye su kamar tattaka.
8 And by the breath of your fury, the waters were gathered together. The flowing waves stood still. The abyss was gathered into the midst of the sea.
Da hucin numfashin hancinka ruwaye suka tattaru. Ruwaye masu kwararowa, suka tsaya kamar bango; ruwaye na zurfafa suka daskare a tsakiyar teku.
9 The enemy said: ‘I will pursue and overtake them. I will divide the spoils. My soul will be filled. I will unsheathe my sword. My hand will put them to death.’
Magabci ya yi fahariya, cewa ‘Zan fafare su, in ci musu. Zan raba ganima; abin da na so ya samu. Zan ja takobina hannuna kuwa zai hallaka su.’
10 Your breath blew, and the sea covered them. They were submerged like lead into the mighty waters.
Amma ka hura numfashinka sai teku ya rufe su. Suka nutse kamar darma cikin manyan ruwaye.
11 Who is like you in strength, O Lord? Who is like you: magnificent in sanctity, terrible and yet praiseworthy, accomplishing miracles?
Wane ne cikin alloli, ya yi kamar ka, ya Ubangiji? Wane ne kamar ka, mai ɗaukaka cikin tsarki, mai banrazana cikin ɗaukaka, mai aikata al’ajabai?
12 You extended your hand, and the earth devoured them.
“Ka miƙa hannunka na dama, ƙasa ta haɗiye abokan gābanka.
13 In your mercy, you have been a leader to the people whom you have redeemed. And in your strength, you have carried them to your holy dwelling place.
A cikin ƙaunarka marar iyaka, za ka bishe mutanen da ka fansa. A cikin ƙarfinka, za ka bishe su zuwa mazauninka mai tsarki.
14 Peoples rose up and became angry. Sorrows took hold of the inhabitants of Philistia.
Al’ummai za su ji, su yi rawar jiki tsoro zai kama mutanen Filistiya.
15 Then the leaders of Edom were stirred up, and trembling took hold of the robust of Moab. All the inhabitants of Canaan were petrified.
Sarakunan Edom za su tsorata, shugabannin Mowab za su yi rawar jiki, mutanen Kan’ana za su narke.
16 Let fear and dread fall upon them, by the magnitude of your arm. Let them become immobilized like stone, until your people cross through, O Lord, until this, your people whom you possess, cross through.
Razana da tsoro za su fāɗo a kansu. Da ikon hannunka za su tsaya cik kamar dutse, har sai mutanen da ka kawo sun wuce, ya Ubangiji.
17 You shall lead them in and plant them, on the mountain of your inheritance, in your most firm dwelling place, which you have formed, O Lord, your sanctuary, O Lord, which your hands have made firm.
Za ka kawo su, ka dasa su a kan dutsen nan naka inda, ya Ubangiji, ka shirya domin mazauninka, wuri mai tsarkin da hannuwanka suka kafa, ya Ubangiji.
18 The Lord will reign in eternity and beyond.
“Ubangiji zai yi mulki har abada abadin.”
19 For the rider Pharaoh, with his chariots and horsemen, was brought into the sea. And the Lord brought back upon them the waters of the sea. But the sons of Israel walked across dry ground in its midst.”
Sa’ad da dawakai, kekunan yaƙi da mahayan dawakan Fir’auna suka shiga cikin teku, Ubangiji ya mayar da ruwan teku a kansu, amma Isra’ilawa suka wuce a cikin teku a busasshiyar ƙasa.
20 And so Miriam, the prophetess, the sister of Aaron, took up a timbrel in her hand. And all the women followed her with timbrels and dancing.
Sa’an nan Miriyam annabiya,’yar’uwar Haruna ta ɗauki ganga a hannunta, dukan mata kuwa suka bi ta, da ganguna suna rawa.
21 And she prophesied, saying: “Let us sing to the Lord, for he has been gloriously magnified. The horse and its rider, he has thrown into the sea.”
Miriyam ta yi musu waƙa. “Ku rera ga Ubangiji gama ya ci gawurtacciyar nasara. Doki da mahayi, ya jefa cikin teku.”
22 Then Moses took Israel from the Red Sea, and they went forth into the desert of Shur. And they wandered for three days through the wilderness, and they found no water.
Sai Musa ya jagoranci Isra’ila daga jan teku zuwa hamadar Shur. Kwana uku suka yi tafiya cikin hamada ba su sami ruwa ba.
23 And they arrived at Marah. They were unable to drink the waters of Marah because they were bitter. Therefore, he also established a name befitting the place, calling it ‘Marah,’ that is, bitterness.
Da suka zo Mara, ba su iya shan ruwan ba saboda yana da ɗaci (shi ya sa ake kira wurin Mara).
24 And the people murmured against Moses, saying: “What shall we drink?”
Sai mutanen suka yi gunaguni a kan Musa, suna cewa, “Me za mu sha?”
25 So he cried out to the Lord, who showed him a tree. And when he had cast it into the waters, they were turned into sweetness. In that place, he established instructions for him, and also judgments. And he tested him there,
Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya nuna masa wani itace. Sai ya jefa shi cikin ruwan, sai ruwan ya zama mai daɗi. A can Ubangiji ya yi musu doka da farilla, a can kuma ya gwada su.
26 saying: “If you will listen to the voice of the Lord your God, and do what is right in his sight, and obey his commands, and keep all his precepts, I will not bring upon you any of the distress that I imposed on Egypt. For I am the Lord, your healer.”
Ya ce, “In kun kasa kunne ga muryar Ubangiji Allahnku kuka yi abin da yake daidai a idanunsa, in kun mai da hankali ga umarnansa, kuka kiyaye dukan farillansa, ba zan kawo muku wani ciwon da na kawo a kan Masarawa ba, gama ni ne Ubangiji da nake warkar da ku.”
27 Then the sons of Israel arrived in Elim, where there were twelve fountains of water and seventy palm trees. And they camped next to the waters.
Sai suka zo Elim inda akwai maɓulɓulan ruwa goma sha biyu da itatuwan dabino saba’in, suka sauka a can, kusa da ruwa.

< Exodus 15 >