< Exodus 14 >

1 Then the Lord spoke to Moses, saying:
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “Speak to the sons of Israel. Let them turn back and encamp away from the region of Pihahiroth, which is between Migdol and the sea, opposite Baal-zephon. In its sight you shall place your camp, above the sea.
“Ka faɗa wa Isra’ilawa, su juya su kafa sansani a Fi Hahirot, a tsakanin Migdol da teku. Za su kafa sansanin kai tsaye kusa da teku, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
3 And Pharaoh will say about the sons of Israel, ‘They have been confined by the land; the desert has enclosed them.’
Fir’auna zai yi tsammani, ‘Aha, Isra’ilawa sun rikice cikin ƙasar, hamada kuwa ta yimƙe su.’
4 And I will harden his heart, and so he will pursue you. And I will be glorified in Pharaoh, and in all his army. And the Egyptians will know that I am the Lord.” And they did so.
Zan kuma taurare zuciyar Fir’auna, zai kuwa bi su. Na shirya wannan domin in nuna ɗaukakata a bisa Fir’auna da ƙungiyar sojansa. Bayan wannan, mutanen Masar za su sani ni ne Ubangiji.” Sai Isra’ilawa suka yi haka.
5 And it was reported to the king of the Egyptians that the people had fled. And the heart of Pharaoh and of his servants was changed about the people, and they said, “What did we intend to do, so that we released Israel from serving us?”
Sa’ad da aka faɗa wa Fir’auna cewa Isra’ilawa sun gudu, sai Fir’auna da bayinsa suka canja ra’ayinsu game da su, suka ce, “Me muka yi? Mun bar Isra’ilawa suka tafi, mun kuwa rasa hidimarsu!”
6 Therefore, he harnessed his chariot, and he took all his people with him.
Sai shi da keken yaƙinsa suka shirya, ya kuma ɗauki sojojinsa tare da shi.
7 And he took six hundred chosen chariots, and whatever chariots were in Egypt, and also the leaders of the whole army.
Ya ɗauki kekunan yaƙi ɗari shida mafi kyau duka, tare da duk sauran keken yaƙin Masar, da shugabanni kuma a kan dukansu.
8 And the Lord hardened the heart of Pharaoh, king of Egypt, and he pursued the sons of Israel. But they were taken away by an exalted hand.
Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna sarkin Masar, domin yă bi Isra’ilawa waɗanda suke tafiya ba tsoro.
9 And when the Egyptians followed the footsteps of those who preceded them, they found them in a camp above the sea. All the horses and chariots of Pharaoh, and the entire army, were in Pihahiroth, opposite Baal-zephon.
Masarawa, dukan dawakan Fir’auna da kekunan yaƙi da mahaya da sojoji, suka bi Isra’ilawa suka cin musu yayinda suke a sansani kusa da teku kurkusa da Fi Hahirot, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
10 And when Pharaoh had drawn near, the sons of Israel, lifting up their eyes, saw the Egyptians behind them. And they were very afraid. And they cried out to the Lord.
Da Fir’auna ya yi kusa, Isra’ilawa suka ɗaga idanu sai suka hange Masarawa daga nesa suna tā da ƙura suna zuwa. Sai suka tsorata ƙwarai, suka kuwa yi kuka ga Ubangiji.
11 And they said to Moses: “Perhaps there were no graves in Egypt, for which reason you took us to die in the wilderness. What is it that you intended to do, in leading us out of Egypt?
Suka ce wa Musa, “Don babu makabarta a Masar ne, ka kawo mu a hamada mu mutu? Me ka yi mana ke nan da ka fitar da mu daga Masar?
12 Is this not the word that we spoke to you in Egypt, saying: Withdraw from us, so that we may serve the Egyptians? For it was much better to serve them, than to die in the wilderness.”
Ba mu faɗa maka a Masar ba, cewa ‘Ka bar mu mu bauta wa Masarawa’? Ai, da ya fi mana mu bauta wa Masarawa, da a ce mu mutu a hamada!”
13 And Moses said to the people: “Do not be afraid. Stand firm and see the great wonders of the Lord, which he will do today. For the Egyptians, whom you now see, will never again be seen, forever.
Musa ya amsa wa mutane ya ce, “Kada ku ji tsoro. Ku tsaya dai ku ga ceton da Ubangiji zai kawo muku yau. Masarawan da kuke gani yau, ba za ku ƙara ganinsu ba.
14 The Lord will fight on your behalf, and you will remain silent.”
Ubangiji zai yi yaƙi dominku, ku dai tsaya kurum.”
15 And the Lord said to Moses: “Why cry out to me? Tell the sons of Israel to continue on.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Don me kake mini kuka? Ka faɗa wa Isra’ilawa su ci gaba da tafiya.
16 Now, lift up your staff, and extend your hand over the sea and divide it, so that the sons of Israel may walk through the midst of the sea on dry ground.
Ka ɗaga sandanka, ka miƙa shi bisa teku don ruwa yă rabu domin Isra’ilawa su wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa.
17 Then I will harden the heart of the Egyptians, so as to pursue you. And I will be glorified in Pharaoh, and in all his army, and in his chariots, and in his horsemen.
Zan taurare zukatan Masarawa su shiga don su bi su. Ta haka zan ci nasara bisa Fir’auna da rundunansa, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.
18 And the Egyptians will know that I am the Lord, when I will be glorified in Pharaoh, and in his chariots, as well as in his horsemen.”
Masarawa za su sani ni ne Ubangiji sa’ad da na sami nasara bisa kan Fir’auna, da keken yaƙinsa, da mahayan dawakansa.”
19 And the Angel of God, who preceded the camp of Israel, lifting himself up, went behind them. And the pillar of cloud, together with him, left the front for the rear
Sai mala’ikan Allah wanda yake tafiya a gaban sojojin Isra’ila, ya janye, ya koma bayansu. Al’amudin girgije shi ma ya koma, ya tsaya a bayansu,
20 and stood between the camp of the Egyptians and the camp of Israel. And it was a dark cloud, yet it illuminated the night, so that they could not succeed at approaching one another at any time all that night.
ya dawo tsakanin sojojin Masar da na Isra’ila. Duk dare, girgijen ya jawo duhu ga gefe ɗaya, haske kuma ga ɗaya gefen; saboda haka ba wanda ya kusaci wani duk dare.
21 And when Moses had extended his hand over the sea, the Lord took it away by an intense burning wind, blowing throughout the night, and he turned it into dry ground. And the water was divided.
Da Musa ya miƙa hannunsa a bisa teku, sai Ubangiji ya tura teku baya da iskar gabas mai ƙarfi duk dare, ya maishe shi busasshiyar ƙasa. Ruwa ya rabu,
22 And the sons of Israel went in through the midst of the dried sea. For the water was like a wall at their right hand and at their left hand.
sai Isra’ilawa suka wuce cikin teku a kan busasshiyar ƙasa, ruwan ya zama musu katanga dama da hagu.
23 And the Egyptians, pursuing them, went in after them, along with all of the horses of Pharaoh, his chariots and horsemen, through the midst of the sea.
Masarawa suka bi su da dukan dawakan Fir’auna, da kekunan yaƙi, da mahayan, suka bi su cikin teku.
24 And now the morning watch had arrived, and behold, the Lord, looking down upon the camp of the Egyptians through the pillar of fire and of cloud, put to death their army.
Da asubahin fāri, sai Ubangiji ya dubi ƙasa a kan sojojin Masarawa daga al’amudin wuta da kuma girgije, sai ya sa suka ruɗe.
25 And he overturned the wheels of the chariots, and they were carried into the deep. Therefore, the Egyptians said: “Let us flee from Israel. For the Lord fights on their behalf against us.”
Ya sa ƙafafun keken yaƙinsu suka fita don su kāsa tuƙi. Sai Masarawa suka ce, “Bari mu gudu daga Isra’ilawa gama Ubangiji yana yaƙi dominsu gāba da Masar.”
26 And the Lord said to Moses: “Extend your hand over the sea, so that the waters may return on the Egyptians, over their chariots and horsemen.”
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka bisa teku don ruwa yă koma kan Masarawa, da keken yaƙinsu, da kuma mahayansu.”
27 And when Moses had extended his hand opposite the sea, it was returned, at first light, to its former place. And the fleeing Egyptians met with the waters, and the Lord immersed them in the midst of the waves.
Musa ya miƙa hannunsa a bisa tekun, da wayewar gari kuwa teku ya koma wurinsa na dā. Masarawa suka yi ƙoƙari su gudu, sai Ubangiji ya tura su cikin teku.
28 And the waters were returned, and they covered the chariots and horsemen of the entire army of Pharaoh, who, in following, had entered into the sea. And not so much as one of them was left alive.
Ruwan ya komo ya rufe keken yaƙin da mahayan, dukan sojojin Fir’aunan da suka bi bayan Isra’ilawa cikin teku, ba ko ɗaya da ya tsira.
29 But the sons of Israel continued directly through the midst of the dried sea, and the waters were to them like a wall on the right and on the left.
Amma Isra’ilawa suka wuce cikin teku a busasshiyar ƙasa, ruwa kuwa ya yi musu katanga dama da hagu.
30 And so the Lord freed Israel on that day from the hand of the Egyptians.
A rana nan Ubangiji ya cece Isra’ila daga hannuwan Masarawa, Isra’ilawa kuwa suka ga gawawwakin Masarawa a bakin teku.
31 And they saw the Egyptians dead on the shore of the sea and the great hand that the Lord had exercised against them. And the people feared the Lord, and they believed in the Lord and in Moses his servant.
Sa’ad da Isra’ilawa suka ga iko mai girma da Ubangiji ya yi gāba da Masarawa, sai mutanen suka ji tsoron Ubangiji, suka amince da shi, da kuma bawansa Musa.

< Exodus 14 >