< 2 Chronicles 14 >

1 Then Abijah slept with his fathers, and they buried him in the City of David. And his son, Asa, reigned in his place. During his days, the land was quiet for ten years.
Abiya kuwa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki, a zamaninsa kuma ƙasar ta zauna lafiya na shekara goma.
2 Now Asa did what was good and pleasing in the sight of his God. And he overturned the altars of foreign worship, and the high places.
Asa ya yi abin da yake da kyau da kuma daidai a gaban Ubangiji Allahnsa.
3 And he broke apart the statues, and he cut down the sacred groves.
Ya kawar da baƙin bagade da masujadai bisa tudu, ya farfashe keɓaɓɓun duwatsu, ya kuma sassare ginshiƙan Ashera.
4 And he instructed Judah that they should seek the Lord, the God of their fathers, and that they should carry out the law and all the commandments.
Ya umarci Yahuda su nemi Ubangiji Allah na kakanninsu, su kuma yi biyayya da dokoki da kuma umarnansa.
5 And he took away, from all the cities of Judah, the altars and the shrines. And he reigned in peace.
Ya kawar da masujadan kan tudu da bagadan turare a kowane gari a Yahuda, masarautar kuwa ta zauna lafiya a ƙarƙashinsa.
6 Also, he built fortified cities in Judah. For it was quiet, and in his time no wars had arisen. For the Lord was generously granting peace.
Ya gina biranen katanga na Yahuda, da yake ƙasar tana zaman lafiya. Babu wanda yake yaƙi da shi a waɗannan shekaru, gama Ubangiji ya ba shi hutu.
7 Then he said to Judah: “Let us build these cities, and strengthen them with walls, and fortify them with towers and gates and bars, while all things are at rest from wars. For we have sought the Lord, the God of our fathers, and he has granted to us peace on every side.” And so they built, and there was nothing to impede them from building.
Ya ce wa Yahuda, “Bari mu gina waɗannan garuruwa mu sa katanga kewaye da su, da hasumiyoyi, ƙofofi da ƙyamare. Ƙasar har yanzu tamu ce domin mun nemi Ubangiji Allahnmu, mun neme shi ya kuwa ba mu hutu a kowane gefe.” Saboda haka suka gina suka kuma yi nasara.
8 Now Asa had in his army three hundred thousand men of Judah, carrying shields and spears, and truly, of Benjamin, two hundred eighty thousand men with shields and bows. All of these were very valiant men.
Asa ya kasance da mayaƙa dubu ɗari uku daga Yahuda, kintsatse da manyan garkuwoyi da māsu, da kuma mayaƙa dubu ɗari biyu da dubu tamanin daga Benyamin, riƙe da ƙananan garkuwoyi da kuma baka. Dukan waɗannan jarumawa ne ƙwarai.
9 Then Zerah, the Ethiopian, went forth against them with his army of one million men, and three hundred chariots. And he approached as far as Mareshah.
Zera mutumin Kush ya taka ya fita don yă yaƙe su da babban runduna da kuma kekunan yaƙi ɗari uku, ya kuma zo har Maresha.
10 And Asa traveled to meet him, and he set up a battle line for the war in the Valley of Zephathah, which is near Mareshah.
Asa ya fita don yă ƙara da shi, suka ja dāgā yaƙi a Kwarin Zefata kusa da Maresha.
11 And he called upon the Lord God, and he said: “O Lord, there is no difference to you, whether you assist by few, or by many. Help us, O Lord our God. For having faith in you and in your name, we have gone forth against this multitude. O Lord, you are our God. Do not allow man to prevail against you.”
Sai Asa ya kira ga Ubangiji Allahnsa ya ce, “Ubangiji, babu wani kamar ka da zai taimaki marar ƙarfi a kan mai ƙarfi. Ka taimake mu, ya Ubangiji Allahnmu, gama mun dogara a gare ka, kuma a cikin sunanka muka fito don mu yaƙi wannan babbar runduna. Ya Ubangiji, kai ne Allahnmu; kada ka bar mutum yă yi nasara a kanka.”
12 And so the Lord terrified the Ethiopians before Asa and Judah. And the Ethiopians fled.
Ubangiji fa ya bugi mutanen Kush a gaban Asa da Yahuda. Mutanen Kush suka gudu,
13 And Asa, and the people who were with him, pursued them as far as Gerar. And the Ethiopians fell, even unto utter destruction, for the Lord was striking, and his army was battling, and they were destroyed. Therefore, they took many spoils.
Asa kuwa da mayaƙansa suka bi su har Gerar. Mutanen Kush suka mutu a ranan nan har ba a iya ƙidaya, aka buge su a gaban Ubangiji da rundunansa. Mutanen Yahuda suka kwashi ganima sosai.
14 And they struck all the cities surrounding Gerar. For indeed, a great fear had overwhelmed everyone. And they despoiled the cities, and they carried away much plunder.
Suka hallaka dukan ƙauyukan kewaye da Gerar, gama tsoron Ubangiji ya kama su. Suka kwashi ganima na dukan ƙauyukan nan, da yake akwai ganima sosai a can.
15 Then too, destroying the fencing for the sheep, they took an innumerable multitude of cattle and camels. And they returned to Jerusalem.
Suka kuma yaƙi sansanin makiyaya suka kwashe tumaki da awaki da raƙuma. Suka koma Urushalima.

< 2 Chronicles 14 >