< 2 Chronicles 10 >

1 Now Rehoboam set out for Shechem. For in that place all of Israel had convened, so that they might appoint him as king.
Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukan Isra’ilawa sun je can don su naɗa shi sarki.
2 But when Jeroboam, the son of Nabat, who was in Egypt, (indeed he had fled to that place from Solomon) had heard it, he promptly returned.
Da Yerobowam ɗan Nebat ya ji wannan (a lokacin yana a Masar, inda ya gudu daga Sarki Solomon ya tafi), sai ya dawo daga Masar.
3 And they summoned him, and he arrived with all of Israel. And they spoke to Rehoboam, saying:
Saboda haka suka aika a zo da Yerobowam, sai shi da dukan Isra’ila suka je wurin Rehobowam suka ce masa.
4 “Your father pressed upon us a very difficult yoke. You should govern us more lightly than your father, who imposed on us a heavy servitude, and so lift up some of the burden, so that we may serve you.”
“Mahaifinka ya sa mana kaya masu nauyi a kanmu, amma yanzu ka sauƙaƙa mana aiki mai zafin nan da kuma kaya masu nauyin da ya sa a kanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
5 But he said, “Return to me after three days.” And when the people had gone away,
Rehobowam ya amsa, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.” Saboda haka mutanen suka watse.
6 he took counsel with the elders, who had stood before his father Solomon while he was still living, saying, “What counsel would you give to me, so that I may respond to the people?”
Sai Sarki Rehobowam ya nemi shawarar dattawan da suka yi wa mahaifinsa Solomon hidima a lokacin da yake da rai, ya tambaye suya ce, “Wace shawara za ku ba ni don in amsa wa waɗannan mutane?”
7 And they said to him, “If you please this people, and if you soothe them with words of clemency, they will be your servants for all days.”
Suka amsa suka ce, “In za ka ji tausayi waɗannan mutane ka kuma gamshe su, ka kuma ba su amsar da ta dace, kullum za su zama bayinka.”
8 But he set aside the counsel of the elders, and he began to have discussion with the youth, who had been raised with him and who were among his companions.
Amma Rehobowam ya ƙi shawarar da dattawa suka ba shi ya kuma nemi shawarar matasan da suka yi girma tare, suke kuma yin masa hidima.
9 And he said to them: “How does it seem to you? Or how should I respond to this people, who have said to me, ‘Lift up the yoke that your father imposed upon us?’”
Ya tambaye su ya ce, “Mece ce shawararku? Yaya zan amsa wa waɗannan mutanen da suke ce mini, ‘Ka sauƙaƙa nauyin da mahaifinka ya sa a kanmu’?”
10 But they responded like youths, having been raised with him in luxury, and they said: “So shall you speak to the people, who said to you, ‘Your father made our yoke heavy; you should lighten it,’ and so shall you respond to them: ‘My little finger is thicker than the back of my father.
Matasan da suka yi girma tare shi suka amsa, “Faɗa wa mutanen da suke ce maka, ‘Mahaifinka ya sa kaya masu nauyi a kanmu, amma ka sauƙaƙa nauyinmu.’ Ka faɗa musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun mahaifina kauri.
11 My father imposed a heavy yoke upon you, and I will place more weight upon it. My father cut you with whips; truly, I will beat you with scorpions.’”
Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; zan ma sa mafi nauyi. Mahaifina ya bulale ku da bulala; zan bulale ku da kunamai.’”
12 Then Jeroboam, and the entire people, went to Rehoboam on the third day, just as he had instructed them.
Bayan kwana uku sai Yerobowam da dukan mutane suka dawo wurin Rehobowam, yadda sarki ya ce, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.”
13 And the king responded harshly, abandoning the counsel of the elders.
Sarki ya amsa musu da kakkausar murya. Ya ƙi shawarar dattawan,
14 And he spoke according to the will of the youths: “My father imposed a heavy yoke upon you, which I will make heavier. My father cut you with whips; truly, I will beat you with scorpions.”
ya kuma bi shawarar matasan ya ce, “Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; zan ma sa mafi nauyi. Mahaifina ya bulale ku da bulala; zan bulale ku da kunamai.”
15 And he did not acquiesce to the pleadings of the people. For it was the will of God that his word be fulfilled, which he had spoken by the hand of Ahijah, the Shilonite, to Jeroboam, the son of Nabat.
Saboda haka sarki bai saurari mutane ba, gama wannan juyin al’amura daga Allah ne, don a cika maganar Ubangiji da ya yi ga Yerobowam ɗan Nebat ta wurin Ahiya mutumin Shilo.
16 Then the entire people, speaking more harshly to the king, spoke to him in this way: “There is no portion for us in David, and there is no inheritance in the son of Jesse. Return to your dwellings, O Israel. Then you, O David, shall pasture your own house.” And Israel went away to their dwellings.
Sa’ad da Isra’ila suka ga sarki ya ƙi yă saurare su, sai suka amsa wa sarki, suka ce, “Wanda rabo muke da shi a wurin Dawuda, wanda sashe muke da shi daga ɗan Yesse? Kowa yă koma tentinsa, ya Isra’ila! Ka lura da gidanka, ya Dawuda!” Saboda haka dukan Isra’ilawa suka tafi gida.
17 But Rehoboam reigned over the sons of Israel who were living in the cities of Judah.
Amma game da Isra’ilawan da suke zama a garuruwan Yahuda kuwa, Rehobowam ya ci gaba da yin mulki a bisansu.
18 And king Rehoboam sent Aduram, who was in charge of the tributes. And the sons of Israel stoned him, and he died. And so king Rehoboam hurried to climb into the chariot, and he fled to Jerusalem.
Sarki Rehobowam ya aiki Hadoram wanda yake lura da aikin dole, amma Isra’ilawa suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu. Sarki Rehobowam kuwa ya gaggauta ya shiga keken yaƙinsa ya gudu zuwa Urushalima.
19 And Israel withdrew from the house of David, even to this day.
Ta haka Isra’ila ya kasance cikin tawaye a kan gidan Dawuda har yă zuwa wannan rana.

< 2 Chronicles 10 >