< 1 Samuel 6 >

1 Now the ark of the Lord was in the region of the Philistines for seven months.
Lokacin da akwatin alkawarin Ubangiji ya kai wata bakwai a ƙasar Filistiyawa.
2 And the Philistines called for the priests and the diviners, saying: “What shall we do with the ark of the Lord? Reveal to us in what manner we should send it back to its place.” And they said:
Filistiyawa suka kira firistoci da bokaye suka ce, “Me za mu yi da akwatin alkawarin Ubangiji? Ku gaya mana yadda za mu komar da shi inda ya fito.”
3 “If you send back the ark of the God of Israel, do not choose to release it empty. Instead, repay to him what you owe because of sin. And then you will be cured. And you will know why his hand did not withdraw from you.”
Suka ce, in za ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra’ila kada ku komar da shi hannu wofi; amma ku tabbata kun aika da hadaya don laifi zuwa wurinsa. Sa’an nan za ku warke ku kuma san dalilin da ya sa bai cire hannunsa a kanku ba.
4 And they said, “What is it that we ought to repay to him because of transgression?” And they responded:
Filistiyawa suka ce, “Wace irin hadaya don laifi za mu aika masa?” Suka ce, “Marurai biyar na zinariya da ɓeraye biyar na zinariya bisa ga yawan sarakunan Filistiyawa. Saboda annoba iri ɗaya ce ta buga ku da shugabanninku.
5 “In accord with the number of the provinces of the Philistines, you shall fashion five gold cysts and five gold mice. For the same plague has been upon all of you and your princes. And you shall fashion a likeness of your cysts and a likeness of the mice, which have destroyed the land. And so shall you give glory to the God of Israel, so that perhaps he may lift off his hand from you, and from your gods, and from your land.
Ku yi siffofin marurai da na ɓeraye da suke hallaka gari, ku ba da girma ga Allah na Isra’ila. Wataƙila zai ɗauke hukuncinsa daga gare ku da allolinku da kuma ƙasarku.
6 Why have you hardened your hearts, just as Egypt and Pharaoh hardened their hearts? After he was struck, did he not then release them, and they went away?
Me ya sa kun taurare kanku kamar yadda Masarawa da Fir’auna suka yi? Da ya ba su matsanancin wahala, ba su bar Isra’ilawa suka tafi hanyarsu ba?
7 Now therefore, fashion and take a new cart, with two cows that have given birth, but on which no yoke has been imposed. And yoke them to the cart, but retain their calves at home.
“Yanzu fa ku shirya sabon keken shanu da shanu biyu masu ba wa’ya’yansu nono, waɗanda ba a taɓa sa musu karkiya ba. Ku daure keken shanu wa shanun, amma ku tsare’yan maruƙansu a gida.
8 And you shall take the ark of the Lord, and you shall place it upon the cart, with the articles of gold that you have paid to him on behalf of transgression. You shall place these in a little box at its side. And release it, so that it may go.
Ku ɗauki wani akwati ku sa siffofin zinariyan nan a ciki, waɗanda za su zama kyautai na shafen laifi, ku ajiye kusa da Akwati na UBANGIJI. Bayan haka sai ku sa keken shanun da akwatin a hanya, ku bar shi yă tafi.
9 And you shall watch. And if, indeed, it ascends by the way of his own parts, toward Beth-shemesh, then he has done this great evil to us. But if not, then we shall know that it is by no means his hand that has touched us, but instead it happened by chance.”
Amma ku zuba ido ku ga in ya haura zuwa yankinsa, zuwa Bet-Shemesh, to, Ubangiji ne ya kawo mana babban masifar a kanmu. Amma in bai bi ta nan ba, za mu san cewa ba shi ne ya buge mu ba, tsautsayi ne kawai.”
10 Therefore, they did it in this way. And taking two cows that were feeding calves, they yoked them to the cart, and they enclosed their calves at home.
Suka yi haka. Suka ɗauki shanun tatsa guda biyu suka ɗaura musu keken shanu, suka tsare’yan maruƙansu a gida.
11 And they placed the ark of God upon the cart, with the little box that held the gold mice and the likenesses of the cysts.
Suka aza akwatin alkawarin Ubangiji a bisa keken shanun tare da akwatin siffofin ɓerayen zinariya da siffofin maruran.
12 But the cows went directly along the way that leads to Beth-shemesh. And they advanced only in one direction, lowing as they went. And they did not turn aside, neither to the right, nor to the left. Moreover, the princes of the Philistines followed them, as far as the borders of Beth-shemesh.
Sai shanun suka miƙe zuwa Bet-Shemesh. Suka bi hanya daidai, ba su juya dama ko hagu ba. Shugabannin Filistiyawa suka bi har zuwa iyakar ƙasar Bet-Shemesh.
13 Now the Beth-shemeshites were harvesting wheat in the valley. And lifting up their eyes, they saw the ark, and they were glad when they had seen it.
A lokacin kuwa mutanen Bet-Shemesh suna girbin alkamansu a kwari da suka ɗaga ido suka hangi akwatin alkawarin Ubangiji, sai suka yi farin ciki ganinsa.
14 And the cart went into the field of Joshua, a Beth-shemeshite, and it stood still there. Now in that place was a great stone, and so they cut up the wood of the cart, and they placed the cows upon it as a holocaust to the Lord.
Keken shanun ya zo filin Yoshuwa a Bet-Shemesh ya tsaya a gefen wani babban dutse. Mutanen suka faskare keken shanun suka miƙa shanun hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
15 But the Levites took down the ark of God, and the little box that was at its side, in which were the articles of gold, and they placed them upon the great stone. Then the men of Beth-shemesh offered holocausts and immolated victims, on that day, to the Lord.
Lawiyawa suka saukar da akwatin alkawarin Ubangiji tare da babban akwati mai siffofin zinariya na ɓeraye da marurai suka ajiye su a kan ƙaton dutse. A wannan rana mutanen Bet-Shemesh suka miƙa hadaya ta ƙonawa da waɗansu hadayu ga Ubangiji.
16 And the five princes of the Philistines saw, and they returned to Ekron on the same day.
Shugabanni biyar na Filistiyawan nan suka ga duk abin da ya faru, suka koma zuwa Ekron a ranar.
17 Now these are the gold cysts, which the Philistines repaid to the Lord for transgression: for Ashdod one, for Gaza one, for Ashkelon one, for Gath one, for Ekron one.
Waɗannan su ne siffofi marurai na zinariya waɗanda Filistiyawa suka aika domin miƙa hadaya don laifi ga Ubangiji, ɗaya domin Ashdod, ɗaya domin Gaza, ɗaya domin Ashkelon, ɗaya domin Gat, ɗaya kuma domin Ekron.
18 And there were gold mice, according to the number of the cities of the Philistines, of the five provinces, from the fortified city to the village that was without a wall, and even to the great stone upon which they placed the ark of the Lord, which was, at last in that day, in the field of Joshua, the Beth-shemeshite.
Filistiyawa kuma suka aika da siffofin ɓeraye biyar na zinariya. Yawan ɓerayen sun yi daidai da yawan garuruwan sarakunan nan biyar na Filistiyawa. Garuruwan sun ƙunshi waɗanda aka gina katangar birni kewaye da su, da kuma ƙauyukansu. Babban dutsen da suka ajiye akwatin alkawarin Ubangiji, ya zama shaida har wa yau a filin Yoshuwa a Bet-Shemesh.
19 Then he struck down some of the men of Beth-shemesh, because they had seen the ark of the Lord. And he struck down some of the people: seventy men, and fifty thousand of the common people. And the people lamented, because the Lord had struck the people with a great slaughter.
Amma Allah ya kashe waɗansu mutum saba’in na mutanen Bet-Shemesh domin sun leƙa cikin akwatin alkawarin Ubangiji. Mutane kuwa suka yi makoki domin Ubangiji ya hallaka mutane da yawa.
20 And the men of Beth-shemesh said: “Who will be able to stand in the sight of the Lord, this holy God? And who will ascend to him from us?”
Mutanen Bet-Shemesh suka yi tambaya suka ce, wa zai iya tsaya a gaban Ubangiji Allah Mai Tsarki? Wurin wa akwatin alkawari zai je daga nan?
21 And they sent messengers to the inhabitants of Kiriath-jearim, saying: “The Philistines have returned the ark of the Lord. Descend and lead it back to you.”
Sai suka aiki manzanni zuwa Kiriyat Yeyarim suka ce, “Filistiyawa sun komo da akwatin alkawarin Ubangiji, ku zo ku ɗauka ku kai wajenku.”

< 1 Samuel 6 >