< Ruth 1 >

1 In the days of one of the judges, when the judges ruled, there was a famine in the land. And a man from Bethlehem in Judah departed to sojourn in the region of the Moabites with his wife and two children.
A kwanakin da mahukunta suke mulki an yi yunwa a ƙasar, sai wani mutum daga Betlehem a Yahuda tare da matarsa da’ya’yansu maza biyu, suka tafi su yi zama na ɗan lokaci a ƙasar Mowab.
2 He called himself Elimelech, and his wife Naomi, and his two sons, the one Mahlon, and the other Chilion, Ephrathites from Bethlehem in Judah. And entering into the region of the Moabites, they stayed there.
Sunan mutumin, Elimelek ne, sunan matarsa Na’omi; sunayen’ya’yan nan nasu biyu, su ne Malon da Kiliyon. Su Efratawa ne daga Betlehem ta Yahuda. Suka kuwa tafi Mowab suka zauna a can.
3 And Elimelech the husband of Naomi died; and she remained with her sons.
To, Elimelek mijin Na’omi ya rasu, aka bar ta da’ya’yanta maza biyu.
4 They took wives from among the Moabites, of whom one was called Orpah, and the other Ruth. And they lived there ten years.
Suka auri mata Mowabawa, sunan ɗaya Orfa ɗayan kuma Rut. Bayan sun zauna a can kamar shekara goma,
5 And they both died, namely Mahlon and Chilion, and the woman was left alone, bereaved of her two children and her husband.
sai Malon da Kiliyon suka mutu su ma, aka kuma bar Na’omi babu’ya’yanta maza biyu da kuma mijinta.
6 And she arose so that she might journey to her native land, with both her daughters-in-law, from the region of the Moabites. For she had heard that the Lord had provided for his people and had given them food.
Sa’ad da ta ji a Mowab cewa Ubangiji ya zo don yă taimaki mutanensa ta wurin tanada musu da abinci, sai Na’omi tare da surukanta suka shirya su koma gida daga can.
7 And so she departed from the place of her sojourn, with both her daughters-in-law, and having set out upon the way, she was about to return to the land of Judah.
Tare da surukanta biyu suka bar inda suka zauna suka kuma kama hanya da za tă komar da su zuwa ƙasar Yahuda.
8 She said to them, “Go to the home of your mother. May the Lord deal mercifully with you, just as you have dealt with the dead and with me.
Sai Na’omi ta ce wa surukanta biyu, “Ku koma, kowannenku, zuwa gidan mahaifiyarta. Bari Ubangiji yă nuna muku alheri yadda kuka nuna wa matattun nan da kuma gare ni.
9 May he grant you to find rest in the houses of the husbands, whom you will obtain by lot.” And she kissed them. They lifted up their voice, and began to weep,
Bari Ubangiji yă sa kowannenku ta sami hutu a gidan wani miji.” Sa’an nan ta sumbace su suka kuma yi kuka da ƙarfi
10 and to say, “We will journey with you to your people.”
suka ce mata, “Za mu tafi tare da ke zuwa ga mutanenki.”
11 But she answered them, “Return, my daughters. Why come with me? Do I have any more sons in my womb, so that you could hope for husbands from me?
Amma Na’omi ta ce, “Ku koma gida,’ya’yana mata. Don me za ku tafi tare da ni? Zan ƙara samun waɗansu’ya’ya maza da za su zama mazanku ne?
12 Return, my daughters, go forth. For I am now exhausted by old age, and not fit for the bond of marriage. Even if I were to conceive on this night, and bear sons,
Ku koma gida’ya’yana mata; na tsufa ainun da zan sāke samun wani miji. Ko ma na yi tsammani har yanzu ina da bege, ko ma na sami miji a wannan dare na kuma haifi’ya’ya maza,
13 if you were willing to wait until they were grown and had completed the years of adolescence, you would be elderly before you could marry. Do not do so, I beg you, my daughters. For your difficulties weigh upon me greatly, and the hand of the Lord has been set against me.”
za ku jira sai sun yi girma? Za ku ci gaba da kasance babu aure saboda su? A’a,’ya’yana mata. Ina da baƙin ciki ƙwarai fiye da ku, domin hannun Ubangiji ya yi gāba da ni!”
14 In response, they lifted up their voice and began to weep again. Orpah kissed her mother-in-law, and then turned back. Ruth clung to her mother-in-law.
A kan wannan suka sāke ɓarke da kuka. Sa’an nan Orfa ta sumbaci surukarta ta yi bankwana, amma Rut ta manne mata.
15 Naomi said to her, “See, your kinswoman returns to her people, and to her gods. Hurry after her.”
Sai Na’omi ta ce, “Duba,’yar’uwanki ta koma zuwa ga mutanenta da kuma allolinta. Ki koma tare da ita.”
16 She answered, “Do not be against me, as if I would abandon you and go away; for wherever you will go, I will go, and where you will stay, I also will stay with you. Your people are my people, and your God is my God.
Rut Amma Rut ta amsa, “Kada ki roƙe ni in bar ki ko in koma daga gare ki. Inda za ki, zan tafi, kuma inda za ki zauna, zan zauna. Mutanenki, za su zama mutanena kuma Allahnki, zai zama Allahna.
17 Whichever land will receive you dying, in the same I will die, and there I will have the place of my burial. May God cause these things to happen to me, and add more also, if anything except death alone should separate you and I.”
Inda za ki mutu zan mutu, zan mutu a can kuma za a binne ni. Bari Ubangiji ya hukunta ni da tsanani sosai, in wani abu in ba mutuwa ce ta raba ke da ni ba.”
18 Therefore, Naomi saw that Ruth, being firmly resolved in her soul, was determined to go with her, and that she was unwilling to be dissuaded, and that nothing further could convince her to return to her own.
Sa’ad da Na’omi ta gane cewa Rut ta ƙudura tă tafi tare da ita, sai ta daina nema tă koma.
19 And so they set out together, and they came to Bethlehem. When they had entered the city, the news quickly spread among them all. And the women said, “This is that Naomi.”
Saboda haka matan biyu suka ci gaba da tafiya sai da suka isa Betlehem. Da suka isa Betlehem, sai dukan garin ya ruɗe saboda su, matan kuwa suka ce, “Na’omi ce wannan kuwa?”
20 But she said to them, “Do not call me Naomi (that is, beautiful), but call me Mara (that is, bitter). For the Almighty has greatly filled me with bitterness.
Ta ce musu, “Kada ku kira ni Na’omi. Ku kira ni Mara gama Maɗaukaki ya sa raina ya yi ɗaci sosai.
21 I went out full and the Lord led me back empty. So then, why call me Naomi, whom the Lord has humbled and the Almighty has afflicted?”
In tafi cikakke, amma Ubangiji ya dawo da ni ba kome. Don me kuke kirana Na’omi? Ubangiji ya wahalshe ni, Maɗaukaki ya kawo mini masifa.”
22 Therefore, Naomi went with Ruth, the Moabite, her daughter-in-law, from the land of her sojourn, and returned to Bethlehem, at the time of the first reaping of the barley.
Na’omi fa ta koma daga Mowab tare da Rut mutuniyar Mowab, surukarta, suka kai Betlehem a lokacin da ake fara girbin sha’ir.

< Ruth 1 >