< 1 Samuel 5 >

1 Then the Philistines took the ark of God, and they transported it from the Stone of Assistance into Ashdod.
Bayan Filistiyawa sun ƙwace akwatin alkawarin Allah, sai suka ɗauke shi daga Ebenezer suka kai shi Ashdod.
2 And the Philistines took the ark of God, and carried it into the temple of Dagon. And they stationed it beside Dagon.
Sa’an nan suka ɗauki akwatin alkawarin suka kai shi cikin haikalin gunkinsu Dagon, suka ajiye kusa da Dagon.
3 And when the Ashdodites had risen up at first light on the next day, behold, Dagon was lying prone on the ground before the ark of the Lord. And they took Dagon, and they set him again in his place.
Kashegari da safe da mutanen Ashdod suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a gaban akwatin alkawarin Ubangiji. Sai suka ɗauki Dagon suka ajiye a wurin zamansa.
4 And again, on the next day, rising up in the morning, they found Dagon lying on his face upon the ground, before the ark of the Lord. But the head of Dagon, and both palms of his hands had been cut off upon the threshold.
Amma kashegari kuma da safe suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a ƙasa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji! Kansa ya fashe, hannuwansa kuma sun kakkarye sun zube a madogarar ƙofa; jikinsa ne kaɗai ya rage.
5 Moreover, only the trunk of Dagon remained in its place. For this reason, the priests of Dagon, and all who enter his temple, do not tread upon the threshold of Dagon in Ashdod, even to this day.
Saboda haka firistocin Dagon da waɗanda suke sujada a haikalin Dagon ba sa taka bakin ƙofar Dagon a Ashdod har wa yau.
6 Now the hand of the Lord weighed heavily upon the Ashdodites, and he destroyed them. And he struck Ashdod and its borders at the inner part of the buttocks. And in the villages and fields, in the midst of that region, mice rose up and burst forth. And this caused a great tumult unto death in the city.
Hannun Ubangiji kuwa ya yi nauyi a bisa Ashdod da kewayenta. Ya kawo hallaka ga dukansu, ya kuma buga su da marurai.
7 Then the men of Ashdod, seeing this kind of plague, said: “The ark of the God of Israel shall not remain with us. For his hand is harsh, over us and over Dagon, our god.”
Da mutanen Ashdod suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Lalle Akwatin Alkawarin Allah na Isra’ila ba zai kasance da mu ba, domin hannunsa yana da nauyi a kanmu da bisan Dagon allahnmu.”
8 And sending, they gathered together all the princes of the Philistines to them, and they said, “What shall we do about the ark of the God of Israel?” And the Gathites responded, “Let the ark of the God of Israel be led around.” And they led the ark of the God of Israel around.
Saboda haka suka kira duka shugabannin Filistiyawa suka tambaye su, suka ce, “Me za mu da akwatin alkawarin Allahn Isra’ila?” Sai suka amsa suka ce, “A ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila a kai shi Gat.” Sai suka ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila.
9 And as they were carrying it around, the hand of the Lord fell upon every single city with an exceedingly great slaughter. And he struck down the men of each and every city, from the small even to the great. And cysts were festering at their buttocks. And the Gathites took counsel, and they made for themselves seat covers from pelts.
Amma bayan sun kai shi can, sai hannun Ubangiji ya yi gāba da birnin, aka jefa shi cikin wani mawuyacin hali. Ya buga mutanen birnin da marurai, babba da yaro.
10 Therefore, they sent the ark of God into Ekron. And when the ark of God had arrived at Ekron, the Ekronites cried out, saying, “They have brought the ark of the God of Israel to us, so that it may kill us and our people!”
Sai suka aika da akwatin alkawarin Allah zuwa Ekron. Yayinda akwatin alkawarin Allah yana shiga cikin Ekron, mutanen Ekron suka yi ihu, suka ce, “An kawo mana akwatin alkawarin Allah na Isra’ila domin yă kashe mu da mutanenmu.”
11 And so they sent and gathered together all the princes of the Philistines, and they said: “Release the ark of the God of Israel, and return it to its own place. And let it not kill us, with our people.”
Saboda haka suka kira ga dukan shugabannin Filistiyawa suka ce, “Ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra’ila inda ya fito; in ba haka ba zai kashe mu da mutanenmu.” Gama mutuwa ta cika garin da tsoro. Hannun Allah ya yi nauyi a kansa.
12 For the fear of death fell upon every single city, and the hand of God was very heavy. Also, the men who did not die were being afflicted in the inner part of the buttocks. And the wailing of each city was ascending to heaven.
Waɗanda ba su mutu ba kuwa, sun kamu da marurai. Kukan birnin kuwa ta hau har zuwa sama.

< 1 Samuel 5 >