< Deuteronomy 33 >

1 Nowe this is the blessing wherewith Moses the man of God blessed the children of Israel before his death, and said,
Wannan ita ce albarkar da Musa mutumin Allah ya furta a kan Isra’ilawa, kafin yă rasu.
2 The Lord came from Sinai, and rose vp from Seir vnto them, and appeared clearely from mount Paran, and he came with ten thousands of Saints, and at his right hand a firie Lawe for them.
Ya ce, “Ubangiji ya zo daga Sinai ya haskaka a bisansu daga Seyir; ya haskaka daga Dutsen Faran. Ya zo tare da dubban tsarkakansa daga kudu, daga gangara dutsensa.
3 Though hee loue the people, yet all thy Saints are in thine handes: and they are humbled at thy foete, to receiue thy words.
Tabbatacce kai ne wanda yake ƙaunar mutane; dukan tsarkaka suna a hannunka. A ƙafafunka, duk suka rusuna, daga wurinka kuma suka karɓi umarni,
4 Moses commanded vs a Lawe for an inheritance of the Congregation of Iaakob.
dokar Musa ta ba mu dokoki, mallakar taron Yaƙub.
5 Then he was among the righteous people, as King, when the heades of the people, and the tribes of Israel were assembled.
Shi ne sarki a bisa Yeshurun sa’ad da shugabannin mutane suka taru, tare da kabilan Isra’ila.
6 Let Reuben liue, and not die, though his men be a small nomber.
“Bari Ruben yă rayu, kada yă mutu, kada mutanensa su zama kaɗan.”
7 And thus he blessed Iudah, and said, Heare, O Lord, the voyce of Iudah, and bring him vnto his people: his hands shalbe sufficient for him, if thou helpe him against his enemies.
Ya kuma faɗa wannan game da Yahuda, “Ka ji, ya Ubangiji, kukan Yahuda; ka kawo shi wurin mutanensa. Da hannuwansa ya kāre kansa. Ka taimake shi a kan maƙiyansa!”
8 And of Leui he said, Let thy Thummim and thine Vrim be with thine Holy one, whome thou diddest proue in Massah, and didst cause him to striue at the waters of Meribah.
Game da Lawi ya ce, “Tummim da Urim na mutumin da ka nuna masa tagomashi ne. Ka gwada shi a Massa; ka yi faɗa da shi a ruwan Meriba.
9 Who said vnto his father and to his mother, I haue not seene him, neither knewe he his brethren, nor knewe his owne children: for they obserued thy word, and kept thy couenant.
Ya yi zancen mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, ‘Ban kula da su ba.’ Bai gane da’yan’uwansa ba, ko yă yarda da’ya’yansa, amma ya kiyaye maganarka ya tsare alkawarinka.
10 They shall teach Iaakob thy iudgements, and Israel thy Lawe: they shall put incense before thy face, and the burnt offring vpon thine altar.
Ya koyar da farillanka ga Yaƙub, dokarka kuma ga Isra’ila. Ya miƙa turare a gabanka da kuma hadaya ta ƙonawa ɗungum a kan bagadenka.
11 Blesse, O Lord, his substance, and accept the worke of his handes: smite through ye loynes of them that rise against him, and of them that hate him, that they rise not againe.
Ka albarkaci ɗaukan dabarunsa, ya Ubangiji, ka kuma ji daɗin aikin hannuwansa. Ka murƙushe kwankwaso waɗanda suka tayar masa; ka bugi abokan gābansa har sai ba su ƙara tashi ba.”
12 Of Beniamin he said, The beloued of the Lord shall dwell in safetie by him: the Lord shall couer him all the day long, and dwell betweene his shoulders.
Game da Benyamin ya ce, “Bari ƙaunataccen Ubangiji yă zauna lafiya kusa da shi, gama yana tsare shi dukan yini, wanda kuma Ubangiji yake ƙauna yana zama a tsakanin kafaɗunsa.”
13 And of Ioseph hee sayde, Blessed of the Lord is his land for the sweetenesse of heauen, for the dewe, and for the depth lying beneath,
Game da Yusuf ya ce, “Bari Ubangiji yă albarkaci ƙasarsa da raɓa mai daraja daga sama a bisa da kuma zurfin ruwan da suke kwance a ƙarƙashi;
14 And for the sweete increase of the sunne, and for the sweete increase of the moone,
da abubuwa masu kyau da rana take kawo, da kuma abubuwa mafi kyau da wata zai iya haifar;
15 And for the sweetenes of the top of the ancient mountaines, and for the sweetenes of the olde hilles,
da zaɓaɓɓun kyautai na daɗaɗɗun duwatsu, da kyawawan amfani na madawwaman tuddai.
16 And for the sweetenesse of the earth, and abundance thereof: and the good will of him that dwelt in the bushe, shall come vpon the head of Ioseph, and vpon the toppe of the head of him that was separated from his brethren.
Tare da kyautai mafi kyau na duniya da cikarta, da tagomashi na wanda yake zama a ƙaramin itace mai ƙonewa. Bari duk waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin sarki a cikin’yan’uwansa.
17 His beautie shalbe like his first borne bullock, and his hornes as the hornes of an vnicorne: with them hee shall smite the people together, euen the endes of the world: these are also the ten thousands of Ephraim, and these are the thousands of Manasseh.
Cikin daraja yana yi kamar ɗan fari na bijimi; ƙahoninsa ƙahonin ɓauna ne. Tare da su zai tukwiyi al’ummai, har ma da waɗanda suke ƙarshen duniya. Haka dubu dubban Efraim suke; haka dubban Manasse suke.”
18 And of Zebulun he sayd, Reioice, Zebulun, in thy going out, and thou Isshachar in thy tents.
Game da Zebulun ya ce, “Ka yi farin ciki, Zebulun, a fitowarka, kai kuma Issakar, a cikin tentunanka.
19 They shall call ye people vnto the mountaine: there they shall offer the sacrifices of righteousnesse: for they shall sucke of the abundance of the sea, and of the treasures hid in the sand.
Za su kira mutane zuwa dutse, a can za su miƙa hadayun adalci; za su yi biki a yalwan tekuna, a dukiyoyin da aka ɓoye a cikin yashi.”
20 Also of Gad he said, Blessed be hee that enlargeth Gad: he dwelleth as a lion, that catcheth for his praye the arme with the head.
Game da Gad ya ce, “Mai albarka ne wanda ya fadada mazaunin Gad! Gad yana zama a can kamar zaki, yana yayyage a hannu da kai.
21 And hee looked to himselfe at the beginning, because there was a portion of the Lawe-giuer hid: yet hee shall come with the heades of the people, to execute the iustice of the Lord, and his iudgements with Israel.
Ya zaɓi ƙasa mafi kyau wa kansa; aka ajiye masa rabon shugaba. Sa’ad da shugabannin mutane suka taru, ya aikata adalcin Ubangiji da kuma hukuncinsa game da Isra’ila.”
22 And of Dan he said, Dan is a lions whelp: he shall leape from Bashan.
Game da Dan ya ce, “Dan ɗan zaki ne, yana tsalle daga Bashan.”
23 Also of Naphtali he sayd, O Naphtali, satisfied with fauour, and filled with the blessing of the Lord, possesse the West and the South.
Game da Naftali ya ce, “Naftali ƙosasshe ne da tagomashin Ubangiji, ya kuma cika albarkarsa; zai gāji gefen kudu zuwa tafki.”
24 And of Asher he saide, Asher shalbe blessed with children: he shalbe acceptable vnto his brethren, and shall dippe his foote in oyle.
Game da Asher ya ce, “Mafi albarka na’ya’yan, shi ne Asher; bari yă sami tagomashi daga’yan’uwansa, bari kuma yă wanke ƙafafunsa a cikin mai.
25 Thy shooes shalbe yron and brasse, and thy strength shall continue as long as thou liuest.
Madogaran ƙofofinka za su zama ƙarfe da tagulla, ƙarfinka kuma zai zama daidai da kwanakinka.
26 There is none like God, O righteous people, which rideth vpon the heauens for thine helpe, and on the cloudes in his glory.
“Babu wani kamar Allah na Yeshurun, wanda yake hawa a bisa sammai don yă taimake ka a kan gizagizai kuma a cikin darajarsa.
27 The eternall God is thy refuge, and vnder his armes thou art for euer: hee shall cast out the enemie before thee, and will say, Destroy them.
Allah madawwami shi ne mafakarka, a ƙarƙashina kuma madawwamin hannuwa ne. Zai kore abokin gābanka a gabanka, yana cewa, ‘Ka hallaka shi!’
28 Then Israel the fountaine of Iaakob shall dwell alone in safetie in a lande of wheat, and wine: also his heauens shall drop the dewe.
Haka Isra’ila zai zauna lafiya shi kaɗai; zuriyar Yaƙub a tsare a ƙasar hatsi da sabon ruwan inabi, inda sammai za su zuba raɓa.
29 Blessed art thou, O Israel: who is like vnto thee, O people saued by the Lord, the shielde of thine helpe, and which is the sword of thy glorie? therefore thine enemies shall bee in subiection to thee, and thou shalt tread vpon their hie places.
Kai mai albarka ne, ya Isra’ila! Wane ne yake kamar ka, mutanen da Ubangiji ya ceta? Shi ne mafakarka da mai taimakonka da kuma takobinka mai ɗaukaka. Abokan gābanka za su zo neman jinƙai a gabanka, za ka kuwa tattake masujadansu.”

< Deuteronomy 33 >