< 1 Samuel 2 >

1 And Hannah prayed, and said, Mine heart reioyceth in the Lord, mine horne is exalted in the Lord: my mouth is enlarged ouer mine enemies, because I reioyce in thy saluation.
Sai Hannatu ta yi addu’a ta ce, “Zuciyata tana farin ciki a cikin Ubangiji; a cikin Ubangiji an sa ina jin daɗi ƙwarai. Na buɗe bakina na yi wa abokan gābana dariya. Kai! Ina murna domin ka cece ni!
2 There is none holy as the Lord: yea, there is none besides thee, and there is no god like our God.
“Babu wani mai tsarki kamar Ubangiji babu wani, in ban da kai; babu wani dutse kamar Allahnmu.
3 Speake no more presumptuously: let not arrogancie come out of your mouth: for the Lord is a God of knowledge, and by him enterprises are established.
“Ka daina maganganu na girman kai ka kuma daina faɗin kalmomin ɗaga kai; gama Ubangiji Allah ne masani daga gare shi kuma ana auna ayyuka.
4 The bow and the mightie men are broken, and the weake haue girded themselues with strength.
“An kakkarya bakkuna masu yaƙi, amma su da ka raunana an ba su makaman ƙarfi.
5 They that were full, are hired foorth for bread, and the hungrie are no more hired, so that the barren hath borne seuen: and shee that had many children, is feeble.
Waɗanda a dā suna da abinci sosai; yanzu suna ƙodago saboda abinci, masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa. Ita da take bakararriya, ta haifi’ya’ya bakwai amma ita da tana da’ya’ya da yawa, ta zama mai baƙin ciki.
6 The Lord killeth and maketh aliue: bringeth downe to the graue and raiseth vp. (Sheol h7585)
“Ubangiji ne ke kawo mutuwa, yă kuma rayar yana kai ga kabari, yă kuma tā da. (Sheol h7585)
7 The Lord maketh poore and maketh rich: bringeth lowe, and exalteth.
Ubangiji ne yakan aika da talauci da kuma dukiya; yakan ƙasƙantar yă kuma ɗaukaka.
8 He raiseth vp ye poore out of the dust, and lifteth vp the begger from the dunghill, to set them among princes, and to make them inherite the seate of glory: for the pillars of the earth are the Lordes, and he hath set the world vpon them.
Yakan tā da matalauci daga ƙura, yă kuma ɗaga mai bukata daga tarin toka; yă zaunar da su tare da’ya’yan sarki; yă kuma sa su gāji mulki na ɗaukaka. “Harsashin duniya na Ubangiji ne; a bisansu ne ya kafa duniya.
9 Hee will keepe the feete of his Saintes, and the wicked shall keepe silence in darkenes: for in his owne might shall no man be strong.
Zai kiyaye ƙafafun masu tsarki, amma mugaye za su lalace cikin duhu. “Ba bisa ga ƙarfi mutum ba ne mutum ke nasara;
10 The Lordes aduersaries shall be destroyed, and out of heauen shall he thunder vpon them: the Lord shall iudge the endes of the worlde, and shall giue power vnto his King, and exalt the horne of his Anoynted.
waɗanda suke gāba da Ubangiji za su hallaka. Zai yi musu tsawa daga sama, Ubangiji zai hukunta dukan duniya. “Zai ba wa sarkinsa ƙarfi, yă kuma ɗaukaka shafaffensa.”
11 And Elkanah went to Ramah to his house, and the childe did minister vnto the Lord before Eli the Priest.
Sa’an nan, Elkana ya koma gida a Rama amma yaron ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli firist.
12 Now the sonnes of Eli were wicked men, and knewe not the Lord.
’Ya’yan Eli firist, mutane ne masu mugunta. Ba su ɗauki Ubangiji a bakin kome ba.
13 For the Priestes custome towarde the people was this: when any man offered sacrifice, the Priestes boy came, while the flesh was seething, and a fleshhooke with three teeth, in his hand,
Al’ada ce ga firistoci da mutane cewa in wani ya miƙa hadaya, yayinda nama yake kan wuta, bawan firist zai zo da babban cokali mai yatsu,
14 And thrust it into the kettle, or into the caldron, or into the panne, or into the potte: all that the fleshhooke brought vp, the Priest tooke for himselfe: thus they did vnto all the Israelites, that came thither to Shiloh.
zai soka cokali mai yatsun a tukunyar, ko butar da ake dafan naman. Duk abin da cokali mai yatsun ya cako daga tukunyar, ya zama na firist. Haka aka yi ta yi wa Isra’ilawan da suka zo miƙa hadaya a Shilo.
15 Yea, before they burnt the fat, the priests boy came and saide to the man that offered, Giue me flesh to rost for the priest: for he wil not haue sodden flesh of thee, but rawe.
Tun ma kafin a ƙona kitse, bawan firist yakan zo yă ce wa mutumin da yake miƙa hadaya, “Ka ba wa firist nama domin yă gasa, ba zai karɓi dafaffen nama daga wurinka ba, sai ɗanye.”
16 And if any man saide vnto him, Let them burne the fatte according to the custome, then take as much as thine heart desireth: then hee would answere, No, but thou shalt giue it nowe: and if thou wilt not, I will take it by force.
In kuwa mutumin ya ce masa, “Bari kitse yă ƙone tukuna, sa’an nan ka ɗiba duk abin da kake so.” Sai bawan yă ce masa, “A’a, ka ba ni yanzu, in ka ƙi kuwa zan ɗiba ƙarfi da yaji.”
17 Therefore the sinne of the yong men was very great before the Lord: for men abhorred the offering of the Lord.
Wannan zunubin samarin ya yi muni ƙwarai a gaban Ubangiji, domin sun wulaƙanta hadayar Ubangiji, ƙwarai da gaske.
18 Now Samuel being a yong childe ministred before the Lord, girded with a linen Ephod.
Amma yaron nan Sama’ila, yana hidima a gaban Ubangiji yana sanye da efod na lilin.
19 And his mother made him a litle coat, and brought it to him from yeere to yeere, when she came vp with her husband, to offer the yerely sacrifice.
Kowace shekara mahaifiyarsa takan ɗinka’yar taguwa ta kai masa sa’ad da ita da mijinta suka je miƙa hadaya ta shekara.
20 And Eli blessed Elkanah and his wife, and said, The Lord giue thee seede of this woman, for the petition that she asked of the Lord: and they departed vnto their place.
Eli yakan sa wa Elkana da matarsa albarka, yă ce, Ubangiji yă ba ka waɗansu’ya’ya ta wurin matan nan, maimakon wanda ta roƙa daga Ubangiji, ta kuma ba da shi ga Ubangiji. Bayan haka sai su koma gida.
21 And the Lord visited Hannah, so that she conceiued, and bare three sonnes, and two daughters. And the childe Samuel grewe before the Lord.
Hannatu kuwa ta sami alfarma daga Ubangiji. Ta yi ciki. Ana cikin haka Sama’ila kuwa sai girma yake ta yi a gaban Ubangiji.
22 So Eli was very olde, and heard all that his sonnes did vnto all Israel, and howe they laye with the women that assembled at the doore of the tabernacle of the Congregation.
To, Eli kuwa ya tsufa ƙwarai, yana kuma jin labari duk abin da’ya’yansa suke yi wa dukan Isra’ila, da yadda suke lalata da matan da suke hidima a bakin ƙofar Tentin Sujada.
23 And hee saide vnto them, Why doe ye such things? for of all this people I heare euill reportes of you.
Saboda haka ya ce musu, “Don me kuke yin waɗannan abubuwa? Na sami labari daga wurin mutane a kan duk ayyukan muguntanku.
24 Do no more, my sonnes, for it is no good report that I heare, which is, that ye make the Lords people to trespasse.
A’a,’ya’yana ba labari mai kyau nake ji cikin mutanen Ubangiji ba.
25 If one man sinne against another, the Iudge shall iudge it: but if a man sinne against the Lord, who will pleade for him? Notwithstanding they obeyed not the voyce of their father, because the Lord would slay them.
In mutum ya yi wa wani laifi Allah yakan kāre shi; amma in mutum ya yi wa Ubangiji zunubi wa zai kāre shi?” Duk da haka,’ya’yansa ba su kula da gargaɗin mahaifinsu ba, domin nufin Ubangiji ne yă hallaka su.
26 (Nowe the childe Samuel profited and grewe, and was in fauour both with the Lord and also with men)
Yaron nan Sama’ila ya dinga girma cikin kwarjini da cikin tagomashi a gaba Ubangiji da mutane.
27 And there came a man of God vnto Eli, and said vnto him, Thus saith the Lord, Did not I plainely appeare vnto the house of thy father, when they were in Egypt in Pharaohs house?
Wani mutum ya zo wurin Eli ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ashe ban bayana kaina sosai ga mahaifinka lokacin da yake a Masar a ƙarƙashin Fir’auna ba?
28 And I chose him out of all the tribes of Israel to be my Priest, to offer vpon mine altar, and to burne incense, and to weare an Ephod before me, and I gaue vnto the house of thy father all the offrings made by fire of the children of Israel.
Na zaɓi mahaifinka daga cikin dukan kabilar Isra’ila yă zama firist nawa don yă yi hidima a bagade, don yă ƙona turare mai ƙanshi, don kuma yă sanya doguwar riga a gabana. Na kuma ba wa iyalin mahaifinka dukan hadaya ta ƙonawa da Isra’ila suka miƙa.
29 Wherefore haue you kicked against my sacrifice and mine offering, which I commanded in my Tabernacle, and honourest thy children aboue mee, to make your selues fatte of the first fruites of all the offerings of Israel my people?
Don me kuke rena hadayata da sadakokina da na ƙayyade domin mazaunina? Don me kake girmama’ya’yanka fiye da ni ta wurin cinye sashe mafi kyau na kowane hadayar da mutanena Isra’ila suka miƙa?’
30 Wherefore the Lord God of Israel saith, I saide, that thine house and the house of thy father should walke before mee for euer: but nowe the Lord saith, It shall not be so: for them that honour me, I will honour, and they that despise me, shall be despised.
“Saboda haka Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na yi alkawari cewa gidanka da gidan mahaifinka za su yi mini hidima a gabana har abada.’ Amma, yanzu Allah ya ce, ba zai yiwu ba; waɗanda suke girmama ni; Ni ma zan girmama su. Amma waɗanda suke ƙasƙantar da ni, haka za a ƙasƙantar da su.
31 Beholde, the dayes come, that I will cut off thine arme, and the arme of thy fathers house, that there shall not be an olde man in thine house.
Lokaci yana zuwa sa’ad da zan rage ƙarfinka da ƙarfin iyalin gidan mahaifinka. Domin kada a sāke samun tsohon mutum a zuriyarka.
32 And thou shalt see thine enemie in the habitation of the Lord in all thinges wherewith God shall blesse Israel, and there shall not be an olde man in thine house for euer.
Za ka zama da ɓacin rai a mazaunina ko da yake za a yi wa Isra’ila alheri. A zuriyarka ba za a taɓa samun tsohon mutum ba.
33 Neuerthelesse, I will not destroy euery one of thine from mine altar, to make thine eyes to faile, and to make thine heart sorowfull: and all ye multitude of thine house shall die when they be men.
Kowannenku da ban kashe daga hidima a bagadena ba, za a bar shi don yă cika idanunka da hawaye da kuma baƙin ciki, dukan sauran zuriyarka kuwa za su mutu a ƙuruciyarsu.
34 And this shalbe a signe vnto thee, that shall come vpon thy two sonnes Hophni and Phinehas: in one day they shall die both.
“‘Abin da kuma ya faru da’ya’yanka biyu Hofni da Finehas zai zama alama a gare ka; saboda mutuwarsu za tă zama a rana ɗaya.
35 And I will stirre me vp a faithfull Priest, that shall do according to mine heart and according to my minde: and I wil build him a sure house, and he shall walke before mine Anointed for euer.
Zan tayar wa kaina amintaccen firist wanda zai aikata abin da nake so yă yi, zan kuwa ba shi zuriya da koyaushe za su yi aiki a gaban zaɓaɓɓen sarkina.
36 And all that are left in thine house, shall come and bowe downe to him for a piece of siluer and a morsell of bread, and shall say, Appoint me, I pray thee, to one of the priestes offices, that I may eate a morsell of bread.
Sa’an nan duk wanda ya rage a zuriyarka zai zo yă durƙusa a gabansa yă roƙi kuɗi da abinci, zai kuma roƙa a yardar masa yă taimaki firistoci da aiki domin yă sami abin da zai ci.’”

< 1 Samuel 2 >