< Deuteronomy 32 >

1 Hearken, ye heauens, and I will speake: and let the earth heare the words of my mouth.
Ku saurara, ya ku sammai, zan yi magana; bari duniya ta ji maganar bakina.
2 My doctrine shall drop as the raine, and my speach shall stil as the dew, as the showre vpon the herbes, and as the great raine vpon the grasse.
Bari koyarwata tă zubo kamar ruwan sama kalmomina kuma su sauko kamar raɓa, kamar yayyafi a kan sabuwar ciyawa, kamar ruwan sama mai yawa a kan tsirai marasa ƙarfi.
3 For I will publish the name of the Lord: giue ye glorie vnto our God.
Zan yi shelar sunan Ubangiji. Ku yabi girman Allahnmu!
4 Perfect is the worke of the mighty God: for all his wayes are iudgement. God is true, and without wickednesse: iust, and righteous is he.
Shi Dutse ne, ayyukansa cikakku ne, dukan hanyoyinsa kuwa masu adalci ne. Allah mai aminci, wanda ba ya yin rashi gaskiya, shi mai adalci ne, nagari ne kuma.
5 They haue corrupted them selues towarde him by their vice, not being his children, but a frowarde and crooked generation.
Sun aikata mugunta a gabansa; saboda abin kunyarsu, su ba’ya’yansa ba ne, amma wata muguwar tsara ce, karkatacciya.
6 Doe ye so rewarde the Lord, O foolish people and vnwise? is not he thy father, that hath bought thee? he hath made thee, and proportioned thee.
Haka za ku biya Ubangiji, Ya ku wawaye da kuma mutane marasa hikima? Shi ba Ubanku ba ne, Mahaliccinku, wanda ya yi ku, ya kuma siffanta ku?
7 Remember the dayes of olde: consider the yeeres of so many generations: aske thy father, and he will shewe thee: thine Elders, and they will tell thee.
Ku tuna da kwanakin dā, ku tuna da tsararrakin da suka wuce tun tuni, Ku tambayi iyayenku, za su faɗa muku, dattawanku, za su kuma bayyana muku.
8 When the most hie God deuided to the nations their inheritance, when he separated the sonnes of Adam, he appoynted the borders of the people, according to the nomber of the children of Israel.
Sa’ad da Mafi Ɗaukaka ya ba da al’ummai gādonsu, sa’ad da ya raba dukan’yan adam, ya kafa iyakoki wa mutane bisa ga yawan’ya’yan Isra’ila maza.
9 For the Lordes portion is his people: Iaakob is the lot of his inheritance.
Gama rabon Ubangiji shi ne mutanensa, Yaƙub shi ne rabon gādonsa.
10 He found him in ye land of ye wildernes, in a waste, and roaring wildernes: he led him about, he taught him, and kept him as ye apple of his eye.
A cikin hamada ya same shi, a jeji marar amfani, inda namomi suke kuka. Ya tsare shi, ya kuma lura da shi; ya bi da shi kamar ƙwayar idonsa,
11 As an eagle stereth vp her nest, flootereth ouer her birdes, stretcheth out her wings, taketh them, and beareth them on her wings,
kamar gaggafar da take yawo a kan sheƙarta tana rufe’ya’yanta, ta buɗe fikafikanta don tă kwashe su tă ɗauke su a kafaɗunta.
12 So the Lord alone led him, and there was no strange god with him.
Ubangiji kaɗai ya jagorance shi; babu wani baƙon gunkin da yake tare da shi.
13 He caryed him vp to the hie places of the earth, that he might eate the fruites of the fieldes, and he caused him to sucke hony out of the stone, and oyle out of the hard rocke:
Ya sa shi ya hau ƙwanƙolin dutse ya ciyar da shi da amfanin gona. Ya shayar da shi da zuma daga dutse, da kuma mai daga dutsen ƙanƙara,
14 Butter of kine, and milke of sheepe with fat of the lambes, and rammes fed in Bashan, and goates, with the fat of the graines of wheat, and the red licour of the grape hast thou drunke.
da kindirmo da madara daga shanu da tumaki da ƙibabbun tumaki da awaki, da zaɓaɓɓun ragunan Bashan da kuma ƙwayoyin alkama mafi kyau. Ka sha ruwan inabi ja wur mai kumfa.
15 But he that should haue bene vpright, when he waxed fat, spurned with his heele: thou art fat, thou art grosse, thou art laden with fatnes: therefore he forsooke God that made him, and regarded not the strong God of his saluation.
Yeshurun ya yi ƙiba, ya yi kauri; cike da abinci, ya zama da nauyi, ya kuma zama sumul. Ya yashe Allahn da ya yi shi, ya ƙi Dutse Cetonsa.
16 They prouoked him with strange gods: they prouoked him to anger with abominations.
Suka sa shi kishi saboda baƙin allolinsu, suka husata shi da gumakan banƙyamarsu.
17 They offred vnto deuils, not to God, but to gods whome they knew not: new gods that came newly vp, whome their fathers feared not.
Suka yi hadaya ga aljanu, waɗanda ba Allah ba, ga allolin da ba su sani ba, ga allolin da aka shigo da su daga baya, allolin da kakanninku ba su ji tsoronsu ba.
18 Thou hast forgotten the mightie God that begate thee, and hast forgotten God that formed thee.
Kuka rabu da Dutsen da ya zama mahaifi gare ku; kuka manta da Allahn da ya haife ku.
19 The Lord then sawe it, and was angrie, for the prouocation of his sonnes and of his daughters.
Ubangiji ya ga wannan ya kuma ƙi su, domin’ya’yansa maza da mata sun husata shi.
20 And he said, I will hide my face from the: I will see what their ende shalbe: for they are a frowarde generation, children in who is no faith.
Ya ce, “Zan ɓoye fuskata daga gare su, in ga ƙarshensu; gama su muguwar tsara ce,’ya’ya ne marasa aminci.
21 They haue moued me to ielousie with that which is not God: they haue prouoked me to anger with their vanities: and I will moue them to ielousie with those which are no people: I wil prouoke them to anger with a foolish nation.
Sun sa ni kishi ta wurin abin da ba allah ba, suka kuma husata ni da gumakansu na wofi. Zan sa su yi kishi ta wurin waɗanda ba mutane ba; zan sa su yi fushi ta wurin al’ummar da ba ta da sani.
22 For fire is kindled in my wrath, and shall burne vnto the bottome of hell, and shall consume the earth with her increase, and set on fire the foundations of the mountaines. (Sheol h7585)
Gama fushina ya kama wuta, tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za tă cinye duniya da girbinta, tă kuma sa wuta a tussan duwatsu. (Sheol h7585)
23 I will spend plagues vpon them: I will bestowe mine arrowes vpon them.
“Zan tula masifu a kansu in kuma gama kibiyoyina a kansu.
24 They shalbe burnt with hunger, and consumed with heate, and with bitter destruction: I will also sende the teeth of beastes vpon them, with the venime of serpents creeping in the dust.
Zan aika da yunwa mai tsanani a kansu, zazzaɓi mai zafi da muguwar annoba; zan aika da haƙoran namun jeji a kansu, da dafin mesa masu ja da ciki.
25 The sworde shall kill them without, and in the chambers feare: both the yong man and the yong woman, the suckeling with the man of gray heare.
Waɗanda suke a waje, takobi zai kashe su, a cikin gidajensu kuma tsoro zai mamaye su.’Yan maza da’yan mata za su hallaka, haka ma jarirai da maza masu furfura.
26 I haue said, I would scatter them abroade: I would make their remembrance to cease from among men,
Na ce zan watsar da su in sa a manta da su a tunanin’yan adam.
27 Saue that I feared the furie of the enemie, least their aduersaries should waxe proude, and least they should say, Our hie hande and not the Lord hath done all this:
Amma ina tsoron tsokanar abokin gāba, don kada abokan gāba su kāsa ganewa har su ce, ‘Hannunmu ne ya yi nasara; ba Ubangiji ne ya aikata dukan wannan ba.’”
28 For they are a nation voide of counsel, neither is there any vnderstanding in them.
Al’ummai ne marasa azanci, babu ganewa a cikinsu.
29 Oh that they were wise, then they would vnderstand this: they would consider their latter ende.
A ce su masu hikima ne har su gane wannan su gane abin da ƙarshensu zai zama!
30 How should one chase a thousand, and two put ten thousande to flight, except their strong God had sold the, and the Lord had shut them vp?
Yaya mutum guda zai kore dubu, mutum biyu su sa dubu goma su gudu, sai ko Dutsensu ya sayar da su, sai ko Ubangiji ya bashe su.
31 For their god is not as our God, euen our enemies being iudges.
Gama dutsensu ba kamar Dutsenmu ba ne, abokan gābanmu sun san da haka.
32 For their vine is of the vine of Sodom, and of the vines of Gomorah: their grapes are grapes of gall, their clusters be bitter.
Kuringarsu ta fito daga kuringar Sodom ne, daga gonakin Gomorra kuma.’Ya’yan inabinsu dafi ne, nonnansu masu ɗaci ne.
33 Their wine is the poyson of dragons, and the cruel gall of aspes.
Ruwan inabinsu dafin macizai ne, mugun dafin gamshaƙa ne.
34 Is not this laide in store with me, and sealed vp among my treasures?
“Ban jibge wannan a ma’ajiya na kuma yimƙe shi a taskokina ba?
35 Vengeance and recompence are mine: their foote shall slide in due time: for the day of their destruction is at hand, and the things that shall come vpon them, make haste.
Sakayya nawa ne, zan kuwa ɗau fansa. A cikin lokaci, ƙafarsu za tă yi santsi; ranar masifarsu ta yi kusa hallakarsu kuma tana gaggautawa a kansu.”
36 For the Lord shall iudge his people, and repent towarde his seruants, when hee seeth that their power is gone, and none shut vp in holde nor left abroad.
Ubangiji zai shari’anta mutanensa yă kuma ji tausayin bayinsa sa’ad da ya ga ƙarfinsu ya ƙare babu kowa kuma da ya rage, bawa ko’yantacce.
37 When men shall say, Where are their gods, their mighty God in whome they trusted,
Zai ce, “To, ina allolinsu, dutsen da suka yi mafaka a ciki,
38 Which did eate the fat of their sacrifices, and did drinke the wine of their drinke offring? let them rise vp, and help you: let him be your refuge.
allolin da suka ci kitsen hadayunsu suka kuma sha ruwan inabin hadayunsu? Ku sa su tashi su taimake ku mana! Bari su ba ku mafaka!
39 Behold now, for I, I am he, and there is no gods with me: I kill, and giue life: I wound, and I make whole: neither is there any that can deliuer out of mine hand.
“Ku duba yanzu cewa ni ne Shi! Ba wani allah in ban da ni. Nakan kashe in kuma rayar, nakan sa rauni in kuma warkar, ba wanda yake da iko yă cece wani daga hannuna.
40 For I lift vp mine hand to heauen, and say, I liue for euer.
Na ɗaga hannu sama na kuma furta. Muddin ina raye har abada,
41 If I whet my glittering sworde, and mine hand take holde on iudgement, I will execute vengeance on mine enemies, and will rewarde them that hate me.
sa’ad da na wasa takobi mai walƙiya hannuna kuwa ya cafke shi don yin hukunci, zan ɗau fansa a kan abokan gābana in sāka wa waɗanda suke ƙina.
42 I will make mine arrowes drunke with blood, (and my sword shall eate flesh) for the blood of the slaine, and of the captiues, when I beginne to take vengeance of the enemie.
Zan sa kibiyoyina su bugu da jini, yayinda takobina yana cin nama, jinin kisassu da na kamammu, kawunan shugabannin abokan gāba.”
43 Ye nations, praise his people: for he will auenge the blood of his seruants, and will execute vengeance vpon his aduersaries, and will bee mercifull vnto his lande, and to his people.
Ku yi farin ciki, ya ku al’ummai, tare da mutanensa, gama zai rama ɗau fansar jinin bayinsa; zai ɗau fansa a kan abokan gābansa yă kuma yi kafara domin ƙasarsa da mutanensa.
44 Then Moses came and spake all ye words of this song in the audience of the people, he and Hoshea the sonne of Nun.
Sai Musa ya zo da Yoshuwa ɗan Nun suka faɗa dukan waɗannan kalmomi wannan waƙa a kunnen mutane.
45 When Moses had made an end of speaking all these wordes to all Israel,
Sa’ad da Musa ya gama karanta waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila,
46 Then hee said vnto them, Set your heartes vnto all the wordes which I testifie against you this day, that ye may commande them vnto your children, that they may obserue and doo all the wordes of this Lawe.
ya ce musu, “Ku riƙe dukan kalmomin da na furta muku a yau, don ku umarce’ya’yanku su lura, su yi biyayya da dukan kalmomin wannan doka.
47 For it is no vaine worde concerning you, but it is your life, and by this worde ye shall prolong your dayes in the land, whither yee go ouer Iorden to possesse it.
Ba kalmomi kurum ba ne dominku, amma har ranku ma. Ta wurinsu za ku yi tsawon rai a ƙasar da kuke haye Urdun ku ci gādonta.”
48 And the Lord spake vnto Moses the selfe same day, saying,
A wannan rana Ubangiji ya ce wa Musa,
49 Goe vp into the mountaine of Abarim, vnto the mount Nebo, which is in the lande of Moab, that is ouer against Iericho: and beholde the lande of Canaan, which I giue vnto the children of Israel for a possession,
“Ka hau Duwatsun Abarim zuwa Dutsen Nebo a Mowab, tsallake daga Yeriko, ka hangi Kan’ana, ƙasar da nake ba wa Isra’ilawa gādo.
50 And die in the mount which thou goest vp vnto, and thou shalt be gathered vnto thy people, as Aaron thy brother died in mount Hor, and was gathered vnto his people,
A can kan dutsen da ka hau za ka mutu a kuma tara ka ga mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya mutu a Dutsen Hor aka kuma tara shi ga mutanensa.
51 Because ye trespassed against me among the children of Israel, at the waters of Meribah, at Kadesh in the wildernesse of Zin: for ye sanctified me not among the children of Israel.
Wannan kuwa domin ku biyu kun fid da aminci gare ni a gaban Isra’ilawa a ruwan Meriba ta Kadesh, a Hamadar Zin kuma saboda ba ku riƙe tsarkina a cikin Isra’ilawa ba.
52 Thou shalt therefore see the lande before thee, but shalt not go thither, I meane, into the land which I giue the children of Israel.
Saboda haka, za ka ga ƙasar daga nesa kawai; ba za ka shiga ƙasar da nake ba wa mutanen Isra’ila ba.”

< Deuteronomy 32 >