< Књига пророка Данила 12 >

1 А у то ће се време подигнути Михаило, велики кнез, који брани твој народ; и биће жалосно време, каквог није било откако је народа до тада; и у то ће се време избавити твој народ, сваки који се нађе записан у књизи.
“A wannan lokaci Mika’ilu, babban mai mulki wanda yake kāre mutanenka, zai tashi. Za a yi lokacin matsananciyar wahala wanda ba a taɓa yi tun farkon ƙasashe har zuwa yanzu. Amma a lokacin da mutanenka, kowane mutum wanda aka sami sunansa a rubuce a cikin littafin, za a cece shi.
2 И много оних који спавају у праху земаљском пробудиће се, једни на живот вечни, а други на срамоту и прекор вечни.
Ɗumbun mutanen da suka yi barci cikin turɓayar duniya za su farka, waɗansu zuwa ga rai madawwami, waɗansu zuwa ga madawwamiyar kunya da kuma madawwamin ƙasƙanci.
3 И разумни ће се сјати као светлост небеска, и који многе приведоше к правди, као звезде вазда и довека.
Waɗanda suke da hikima za su haskaka kamar hasken samaniya, waɗanda kuma suka jagoranci waɗansu da yawa zuwa adalci, za su zama kamar taurari har abada abadin.
4 А ти Данило затвори ове речи и запечати ову књигу до последњег времена; многи ће претраживати, и знање ће се умножити.
Amma kai, Daniyel, ka rufe zancen nan ka kuma liƙe kalmomin littafin nan har sai ƙarshe. Mutane da yawa za su yi ta kai komo don neman sani.”
5 Тада погледах ја, Данило, и гле, стајаху друга двојица, један с ове стране на брегу реке, а други с оне стране на брегу реке.
Sa’an nan ni, Daniyel, na duba, a gabana kuwa ga waɗansu mutum biyu tsaye, ɗaya a wannan hayen kogi ɗaya kuma a ƙetaren kogin.
6 И један рече човеку обученом у платно, који стајаше над водом у реци: Кад ће бити крај тим чудесима?
Ɗayansu ya ce wa mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, “Har yaushe waɗannan abubuwan banmamakin za su cika?”
7 И чух човека обученог у платно, који стајаше над водом у реци, и подиже десницу своју и левицу своју к небу, и закле се Оним који живи увек да ће се све ово испунити по времену, по временима и по по времена, и кад се сврши расап силе светог народа.
Mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, ya ɗaga hannun damansa da kuma na hagunsa sama, sai na ji yana rantsuwa da wannan da yake raye har abada, yana cewa, “Zai kasance na ɗan lokaci, lokuta da rabin lokaci. Za a kammala waɗannan abubuwa, sa’ad da aka gama ragargaje ikon tsarkakan mutane.”
8 И ја чух али не разумех; и рекох: Господару мој, какав ће бити крај томе?
Na kuma ji, amma ban fahimta ba. Don haka sai na yi tambaya, “Ranka yă daɗe, mene ne ƙarshen waɗannan abubuwa?”
9 А Он рече: Иди Данило, јер су затворене и запечаћене ове речи до последњег времена.
Sai ya amsa ya ce, “Ka kama hanyarka, Daniyel, domin a rufe kalmomin aka kuma liƙe su har sai ƙarshen lokaci.
10 Многи ће се очистити, убелити и окушати; а безбожници ће радити безбожно, нити ће који безбожник разумети, али ће разумни разумети.
Za a tsarkake mutane da yawa, za a maishe su marasa aibi a kuma tace su; amma mugaye za su ci gaba da mugunta. Babu wani mugun da zai fahimta, amma waɗanda za su zama masu hikima za su fahimta.
11 А од времена кад се укине жртва ваздашња и постави гнусоба пустошна, биће хиљаду и двеста и деведесет дана.
“Daga lokacin da za a hana miƙa hadayar ƙonawa ta yau da kullum, a kuma kafa abin banƙyama, wanda yake lalatarwa, za a yi kwana 1,290.
12 Благо ономе који претрпи и дочека хиљаду и три стотине и тридесет и пет дана.
Mai albarka ne wanda ya jira har yă zuwa ƙarshen kwanakin nan 1,335.
13 А ти иди ка свом крају; и почиваћеш и остаћеш на делу свом до свршетка својих дана.
“Gare ka dai, ka yi tafiyarka har zuwa ƙarshe. Za ka huta, sa’an nan a ƙarshen kwanaki za ka tashi don karɓi sashen gadon da aka ba ka.”

< Књига пророка Данила 12 >