< Књига пророка Језекиља 1 >

1 Године тридесете, месеца четвртог, петог дана, кад бејах међу робљем на реци Хевару, отворише се небеса, и видех утваре Божје.
A shekara ta talatin, a wata na huɗu a rana biyar, yayinda nake cikin’yan zaman bauta kusa da Kogin Kebar, sai sammai suka buɗe na kuwa ga wahayoyin Allah.
2 Петог дана тог месеца, пете године од како се зароби цар Јоахин,
A rana biyar ga wata, a shekara ta biyar ne ta zaman bautan Sarki Yehohiyacin,
3 Дође реч Господња Језекиљу сину Вузијевом, свештенику, у земљи халдејској на реци Хевару, и онде дође рука Господња нада њ.
maganar Ubangiji ta zo wa Ezekiyel firist, ɗan Buzi, kusa da Kogin Kebar a ƙasar Babiloniyawa. A can hannun Ubangiji yana a kansa.
4 И видех, и гле, силан ветар долажаше од севера, и велик облак и огањ који се разгореваше, и око њега светлост, а исред огња као јака светлост;
Na duba, sai na ga guguwa ta taso daga arewa babban hadari cike da walƙiya kewaye da haske mai haske sosai. Tsakiyar wutar ta yi kamar ƙarfe mai cin wuta balbal,
5 Исред њега још као четири животиње, које на очи беху налик на човека;
a cikin wutar kuwa akwai abin da ya yi kamar halittu guda huɗu. A bayyane kamanninsu ya yi kamar siffar mutum,
6 И у сваке беху четири лица, и четири крила у сваке;
amma kowannensu yana da fuskoki huɗu da fikafikai guda huɗu.
7 И ноге им беху праве, а у стопалу беху им ноге као у телета; и севаху као углађена бронза.
Ƙafafunsu miƙaƙƙu ne; kuma ƙafafunsu sun yi kamar na maraƙi suna kuma walƙiya kamar tagullar da aka goge.
8 И руке им беху човечје под крилима над четири стране, и лица им и крила беху на четири стране.
A ƙarƙashin fikafikansu huɗu suna da hannuwan mutum a kowane gefe. Dukansu huɗu suna da fuskoki da fikafikai,
9 Састављена им беху крила једно с другим; и не окретаху се идући, него свака иђаше на према се.
kuma fikafikansu suna taɓan juna. Kowanne ya miƙe gaba; ba sa juyawa sa’ad da suke tafiya.
10 И лице беше у све четири лице човечје и лице лавово с десне стране, а с леве стране лице волујско и лице орлово у све четири.
Fuskokinsu sun yi kamar haka. Kowanne a cikin huɗun yana da fuskar mutum, kuma a gefen dama kowanne yana da fuskar zaki, a hagu kuma fuskar maraƙi; kowanne yana kuma da fuskar gaggafa.
11 И лица им и крила беху раздељена озго; у сваке се два крила састављаху једно с другим, а два покриваху им тело.
Haka fuskokinsu suka kasance. Fikafikansu sun buɗu sama; kowanne yana da fikafikai biyu, ɗaya yana taɓa fikafikan ɗayan halittar a ɗayan gefe, fikafikai biyu kuma suna rufe jikinsa.
12 И свака иђаше право на према се; иђаху куда дух иђаше, и не окретаху се идући.
Kowanne ya miƙe gaba sosai. Duk inda ruhu zai tafi, can za su, ba tare da juyawa ba yayinda suke tafiya.
13 И на очи беху те животиње као живо угљевље, гораху на очи као свеће; тај огањ пролажаше између животиња и светљаше се, и из огња излажаше муња.
Kamannin halittun ya yi kamar garwashi mai cin wuta ko kuwa kamar fitilu. Wuta tana kai da kawowa a cikin halittun; ta yi haske ƙwarai, walƙiya kuma tana wulgawa daga cikinta.
14 И животиње трчаху и враћаху се као муња.
Halittun suna gaggauta kai da kawowa kamar walƙiya.
15 И кад гледах животиње, гле, точак један беше на земљи уза сваку животињу према четири лица њихова.
Yayinda nake kallon rayayyun halittun nan, sai na ga da’ira a ƙasa kusa da kowace halitta da fuskokinsa huɗu.
16 Обличјем и направом беху точкови као боје хрисолитове, и сва четири беху једнака, и обличјем и направом беху као да је један точак у другом.
Ga kamanni da fasalin da’irorin. Suna ƙyalƙyali kamar kirisolit, kuma dukan huɗun sun yi kama da juna. Kowacce ta yi kamar da’ira a cikin da’ira.
17 Кад иђаху, иђаху сва четири сваки на своју страну, и идући не скретаху.
Yayinda suke tafiya, sukan nufi duk wani gefe guda cikin gefe huɗun da halittun suka nufa; da’irorin ba za su juya ba sa’ad da halittun suke tafiya.
18 И наплаци им беху високи страхота; и беху наплаци пуни очију унаоколо у сва четири.
Ƙarafansu da suka yi kamar zobe sun yi tsayi suna kuma da bantsoro, dukan ƙarafan nan huɗu kuwa da suka yi kamar zobe suna cike da idanu a kewaye.
19 И кад иђаху животиње, иђаху и точкови уз њих; и кад се животиње подизаху од земље, подизаху се и точкови.
Sa’ad da rayayyun halittun suke tafiya, da’irorin da suke kusa da su kan motsa; kuma sa’ad da rayayyun halittun sun tashi sama, da’irorin su ma sukan tashi sama.
20 Куда дух иђаше, онамо иђаху, и подизаху се точкови према њима, јер дух животињски беше у точковима.
Duk inda ruhu za shi, su ma can za su, kuma da’irorin za su tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun nan yana a cikin da’irorin.
21 Кад оне иђаху, иђаху и они; и кад оне стајаху, стајаху и они; и кад се оне подизаху од земље, подизаху се и точкови према њима, јер дух животињски беше у точковима.
Sa’ad da halittun sun motsa, sai su ma su motsa; sa’ad da halittun sun tsaya cik, su ma sai su tsaya cik, sa’ad da kuma halittun sukan tashi sama, da’irorin suka tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun nan yana a cikin da’irorin.
22 А над главама животињама беше као небо, по виђењу као кристал, страшно, разастрто озго, над главама њиховим.
A bisa kawunan rayayyun halittun nan akwai abin da ya yi kamar ƙanƙara, mai bantsoro.
23 А под тим небом беху им крила пружена, једно према другом, а два крила свакој покриваху тело.
A ƙarƙashin al’arshin fikafikansu sun miƙe kyam ɗaura da juna, kuma kowanne yana da fikafikai biyu da suka rufe jikinsa.
24 И чух хуку крила њихових кад иђаху као да беше хука велике воде, као глас Свемогућег и као граја у логору; и кад стајаху, спуштаху крила.
Sa’ad da halittun suke tafiya, sai na ji ƙarar fikafikansu, kamar rurin ruwaye masu gudu, kamar muryar Maɗaukaki, kamar hayaniyar rundunar mayaƙa. In sun tsaya cik, sukan sauko da fikafikansu.
25 И кад ставши спуштаху крила, чујаше се глас озго из неба, које беше над главама њиховим.
Sai aka ji murya daga al’arshi a kan kawunansu yayinda suke tsaye da fikafikansu a sauke.
26 И озго на оном небу што им беше над главама, беше као престо, по виђењу као камен сафир, и на престолу беше по обличју као човек.
A bisa al’arshin a kan kawunansu akwai abin da ya yi kamar saffaya, kuma a can bisa a kan kursiyin akwai siffa kamar na mutum.
27 И видех као јаку светлост, и у њој унутра као огањ наоколо, од бедара горе, а од бедара доле видех као огањ и светлост око њега.
Na ga daga abin da ya yi kamar kwankwasonsa zuwa bisa ya yi kamar ƙarfe mai walƙiya, sai ka ce wuta, kuma daga kwankwasonsa zuwa ƙasa ya yi kamar wuta; haske kuma mai walƙiya sosai kewaye da shi.
28 Као дуга у облаку кад је киша, таква на очи беше светлост унаоколо. То беше виђење славе Божје на очима; и кад видех, падох на лице своје, и чух глас Некога који говораше.
Kamar kamannin bakan gizo a cikin gizagizai a ranar da aka yi ruwan sama, haka hasken da ya kewaye shi. Wannan shi ne kwatancin kamannin ɗaukakar Ubangiji. Sa’ad da na gani, sai na fāɗi rubda ciki, na kuma ji muryar wani tana magana.

< Књига пророка Језекиља 1 >