< Psalmów 107 >

1 Wysławiajcie PANA, bo [jest] dobry, bo jego miłosierdzie [trwa] na wieki.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Niech [to] mówią odkupieni przez PANA, ci, których odkupił z ręki wroga;
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 I zgromadził z ziem, ze wschodu i zachodu, z północy i południa.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 Błądzili po pustyni, po bezdrożnym pustkowiu, nie znajdując miasta, gdzie mogliby zamieszkać.
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 [Byli] głodni i spragnieni, aż omdlewała w nich dusza.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 A gdy zawołali do PANA w swoim utrapieniu, uwolnił ich z ucisku;
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 I prowadził ich prostą drogą, aby doszli do miasta, w którym mogliby zamieszkać.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Niech wysławiają PANA [za] jego miłosierdzie i cudowne dzieła [wobec] synów ludzkich;
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 Bo napoił spragnioną duszę, a głodną duszę napełnił dobrami.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Siedzieli w ciemności i w cieniu śmierci, spętani nędzą i żelazem;
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 Bo buntowali się przeciw słowom Boga i pogardzili radą Najwyższego.
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 Dlatego upokorzył ich serce trudem, upadli, a nie było nikogo, kto by im pomógł.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 A [gdy] wołali do PANA w swoim utrapieniu, wybawił ich z ucisku;
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 Wyprowadził ich z ciemności i z cienia śmierci, a ich pęta rozerwał.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Niech wysławiają PANA [za] jego miłosierdzie i za cudowne dzieła [wobec] synów ludzkich.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 Bo skruszył bramy spiżowe i połamał żelazne rygle.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Głupcy z powodu swej występnej drogi i nieprawości doznają utrapień.
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 Ich dusza brzydzi się wszelkim pokarmem i zbliżają się do bram śmierci.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 A gdy wołają do PANA w swoim utrapieniu, wybawia ich z udręczeń.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 Posłał swoje słowo i uzdrowił ich, i wybawił ich z grobu.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Niech wysławiają PANA [za] jego miłosierdzie i cudowne dzieła [wobec] synów ludzkich;
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 I niech składają ofiary dziękczynienia, i głoszą z radością jego dzieła.
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Ci, którzy na statkach wyruszają w morze, handlujący na wielkich wodach;
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 Widzą dzieła PANA i jego cuda w głębinach.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 Gdy daje rozkaz, powstaje wicher i podnoszą się fale morskie.
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 Oni wstępują aż [do] nieba i zstępują w głębiny, tak że ich dusza mdleje w niebezpieczeństwie.
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 Chwieją się i zataczają jak pijany, a cała ich mądrość zanika.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Gdy wołają do PANA w swoim utrapieniu, wybawia ich z udręczeń.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 Zamienia burzę w ciszę, tak że uspokajają się jej fale.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 Wtedy oni weselą się, że ucichły; i tak przyprowadza ich do upragnionego portu.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Niech wysławiają PANA [za] jego miłosierdzie i cudowne dzieła [wobec] synów ludzkich.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 Niech go wywyższają w zgromadzeniu ludu i w radzie starszych niech go chwalą.
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 Zamienia rzeki w pustynię, a źródła wód w suchą ziemię;
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 Ziemię urodzajną [zamienia] w jałową z powodu niegodziwości tych, którzy w niej mieszkają.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 Pustynię zamienia w jezioro, a suchą ziemię w źródła wód.
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 I osadza tam głodnych, aby zakładali miasta do zamieszkania;
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 I obsiewali pole, sadzili winnice i zbierali obfity plon.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 Błogosławi im tak, że bardzo się rozmnażają, i nie zmniejsza [liczebności] ich bydła.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 Ale potem maleje ich liczba i upokorzeni są uciskiem, nędzą i utrapieniem;
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 On wylewa wzgardę na władców i sprawia, że błądzą po bezdrożach pustkowia.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 Lecz podnosi nędznego z utrapienia i rozmnaża [jego] rodzinę jak stado.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 Widząc to, prawi rozweselą się, a wszelka nieprawość zamknie swe usta.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Kto jest tak mądry, aby tego upatrywał i rozumiał litość PANA?
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Psalmów 107 >