< 4 Mosebok 36 >

1 Overhodene for familiene i den ætt som nedstammet fra Gilead, en sønn av Manasses sønn Makir, og hørte til Josefs barns ætter, gikk frem for Moses og for de høvdinger som var overhoder for Israels barns familier,
Sai shugabannin gidajen iyalan Gileyad ɗan Makir, ɗan Manasse, waɗanda suka fito daga kabilar zuriyar Yusuf, suka zo, suka yi magana a gaban Musa da shugabanni, shugabannin iyalan Isra’ilawa.
2 og de sa: Herren har befalt min herre å gi Israels barn landet til arv ved loddkasting, og min herre har fått befaling av Herren om å gi vår bror Selofhads arv til hans døtre.
Suka ce, “Sa’ad da Ubangiji ya umarce ranka yă daɗe, yă raba ƙasar gādo ga Isra’ilawa ta wurin ƙuri’a, ya umarce ka, ka ba wa’ya’ya matan nan na Zelofehad ɗan’uwanmu gādonsa.
3 Men blir nu de gift med menn av Israels barns andre stammer, så går deres arv fra våre fedres arv og legges til den stammes arv som de kommer til å tilhøre, og således blir vår arvelodd mindre.
To, a ce sun auri mutane daga waɗansu kabilan Isra’ilawa fa; ka ga, za a ɗebe gādonsu daga gādon kakanninmu a ƙara wa gādon kabilan mutanen da suka aura ke nan. Ta haka za a ɗebe sashe daga gādon da aka ba mu ke nan.
4 Og når jubelåret kommer for Israels barn, så blir deres arv lagt til den stammes arv som de kommer til å tilhøre, og deres arv går fra vår fedrenestammes arv.
Sa’ad da Shekara ta Murnar Isra’ilawa ta kewayo, za a haɗa gādonsu da na kabilan mutanen da suka aura, a kuma ba su mallakar gādon da aka ɗebe daga kabilar kakanninmu.”
5 Da bød Moses Israels barn efter Herrens ord og sa: Josefs barns stamme har rett i det de sier.
Ta wurin umarnin Ubangiji, Musa ya ba Isra’ilawa wannan umarni, “Abin da kabilar zuriyar Yusuf suke faɗi, daidai ne.
6 Således byder Herren om Selofhads døtre: De kan gifte sig med hvem de vil, bare de gifter sig innen sin fedrenestammes ætt,
Ga abin da Ubangiji ya umarta saboda’ya’ya matan nan na Zelofehad. Za su iya auri duk wanda suka ga dama, muddin sun yi aure a cikin kabilar kakanninsu.
7 forat ikke nogen arv hos Israels barn skal gå over fra en stamme til en annen - Israels barn skal holde fast hver ved sin fedrenestammes arv.
Ba gādon Isra’ilan da za a ba wa wata kabila daga wata kabila, gama kowane mutumin Isra’ila zai riƙe gādonsa na kabilar da ya gāda daga kakanninsa.
8 Og enhver datter i Israels barns stammer som får arv, skal gifte sig med en mann av sin fedrenestammes ætt, forat Israels barn kan arve hver sine fedres arv,
Kowace’ya wadda ta ci gādon ƙasa, a kowace kabilar Isra’ilawa, dole tă auri wani cikin kabilar kakanninta, saboda kowane mutumin Isra’ila yă mallaki gādon kakanninsa.
9 og forat ingen arv skal gå over fra en stamme til en annen, men Israels barns stammer holde fast hver ved sin arv.
Ba gādon da za a ba wa wata kabila daga wata kabila, gama kowace kabilar Isra’ilawa za tă riƙe mallaka da ta gāda.”
10 Selofhads døtre gjorde således som Herren hadde befalt Moses.
Saboda haka’ya’yan Zelofehad mata suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
11 Mahla, Tirsa og Hogla og Milka og Noa, Selofhads døtre, blev gift med sine farbrødres sønner;
’Ya’yan Zelofehad mata, Mala, Tirza, Hogla, Milka da Nowa, suka auri’ya’yan’yan’uwa na gefen mahaifinsu.
12 de blev gift med menn av Manasses, Josefs sønns ætter, så deres arv blev hos deres fedreneætts stamme.
Suka yi aure cikin kabilar zuriyar Manasse ɗan Yusuf, gādonsu kuwa ya kasance a cikin iyali da kuma kabilar mahaifinsu.
13 Dette er de bud og lover som Herren gav Israels barn ved Moses på Moabs ødemarker ved Jordan, midt imot Jeriko.
Waɗannan su ne umarnai da ƙa’idodin da Ubangiji ya ba wa Isra’ilawa ta wurin Musa, a filayen Mowab kusa da Urdun, ɗaura da Yeriko.

< 4 Mosebok 36 >