< 5 Mosebok 1 >

1 Dette er de ord Moses talte til hele Israel i ørkenen på hin side Jordan, i ødemarken, midt imot Suf, mellem Paran og Tofel og Laban og Haserot og Di-Sahab,
Waɗannan su ne kalmomin da Musa ya yi wa dukan Isra’ila, a hamada gabas da Urdun, wato, Araba, ɗaura da Suf, tsakanin Faran da Tofel, Laban, Hazerot da Dizahab.
2 elleve dagsreiser fra Horeb efter den vei som fører til Se'ir-fjellene, til Kades-Barnea.
(Yakan ɗauki kwana goma sha ɗaya daga Horeb zuwa Kadesh Barneya ta hanyar Dutsen Seyir.)
3 Det var i det firtiende år, i den ellevte måned, på den første dag i måneden Moses talte til Israels barn og bar frem alt det Herren hadde befalt ham å tale til dem,
A shekara ta arba’in, a rana ta fari ga wata na goma sha ɗaya, Musa ya yi shela ga Isra’ilawa game da dukan abin da Ubangiji ya umarta shi game da su.
4 efterat han hadde slått Sihon, amorittenes konge, som bodde i Hesbon, og ved Edre'i hadde slått Og, kongen i Basan, som bodde i Astarot.
Wannan ya faru bayan ya ci Sihon sarkin Amoriyawa wanda ya yi mulki a Heshbon da yaƙi. A Edireyi kuma ya ci Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot da yaƙi.
5 På hin side Jordan, i Moabs land, tok Moses sig fore å utlegge denne lov og sa:
Gabas da iyakar Mowab, Musa ya fara bayyana wannan doka, yana cewa,
6 Herren vår Gud talte til oss ved Horeb og sa: Lenge nok har I opholdt eder ved dette fjell.
Ubangiji Allahnmu ya faɗa mana a Horeb cewa, “Daɗewarku a wannan dutse ya isa haka.
7 Bryt nu op og gi eder på veien til amoritter-fjellene og til alle de folk som bor deromkring, i ødemarken, i fjellbygdene og i lavlandet og i sydlandet og ved havstranden, til kana'anittenes land og til Libanon, helt til den store elv, elven Frat.
Ku tashi, ku ci gaba zuwa ƙasar tudun Amoriyawa; ku tafi wurin dukan maƙwabta a cikin Araba, a cikin duwatsu, a gindin yammancin tuddai, a Negeb da kuma a ta kwaruruka, da ƙasar Kan’aniyawa da kuma zuwa Lebanon, har zuwa babban kogi, wato, Yuferites.
8 Se, jeg har gitt landet i eders vold; dra avsted og innta det land som Herren har tilsvoret eders fedre Abraham, Isak og Jakob å ville gi dem og deres ætt efter dem!
Duba na riga na ba ku wannan ƙasa. Ku shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub, da kuma ga zuriyarsu bayansu.”
9 Dengang sa jeg til eder: Jeg makter ikke alene å bære eder.
A wancan lokaci na faɗa muku cewa, “Ku kaya ne masu nauyi da ni kaɗai ba zan iya ɗauka ba.
10 Herren eders Gud har gjort eder tallrike, så I idag er som stjernene på himmelen i mengde;
Ubangiji Allahnku ya ƙara yawanku har yau kuka zama da yawa kamar taurari a sarari.
11 og måtte bare Herren, eders fedres Gud, gjøre eder tusen ganger flere enn I er, og velsigne eder, som han har tilsagt eder!
Bari Ubangiji, Allahn kakanninku yă ƙara yawanku sau dubu, yă kuma albarkace ku yadda ya yi alkawari!
12 Men hvorledes kan jeg alene bære strevet og møien med eder og alle eders tretter?
Amma yaya zan ɗauka dukan damuwoyinku da nawayarku da kuma faɗace-faɗacenku duka ni kaɗai?
13 Kom med nogen vise og forstandige og prøvede menn fra hver av eders stammer! Så vil jeg sette dem til høvdinger over eder.
Ku zaɓi waɗansu masu hikima, masu ganewa, da kuma mutanen da ake girmama daga kowace kabilarku, zan kuma sa su a kanku.”
14 Da svarte I mig: Det er både rett og godt det du sier.
Kuka amsa mini, kuka ce, “Abin da ka ce za ka yi, yana da kyau.”
15 Så tok jeg høvdingene for eders stammer, vise og prøvede menn, og satte dem til høvdinger over eder, nogen over tusen og nogen over hundre og nogen over femti og nogen over ti, og jeg gjorde dem til tilsynsmenn over eders stammer.
Saboda haka na ɗauko shugabannin kabilanku masu hikima, waɗanda suka saba da ma’amala da jama’a, na sa su shugabanni a gabanku, waɗansu suka zama shugabanni a kan dubu-dubu, waɗansu a kan ɗari-ɗari, waɗansu a kan hamsin-hamsin, waɗansu kuma a kan goma-goma. Na sa su zama shugabanni a kabilanku.
16 Dengang bød jeg også eders dommere og sa: Hør på de saker som eders brødre har sig imellem, og døm med rettferdighet mellem en mann og hans bror eller en fremmed som bor hos ham!
Na kuma umarci alƙalanku a wancan lokaci, na ce, “Ku yi adalci cikin shari’a tsakanin’yan’uwanku, ko damuwar tana tsakanin’yan’uwa Isra’ilawa ne, ko kuwa tsakanin Isra’ilawa da baƙin da suke zaune a cikinku.
17 I skal ikke gjøre forskjell på folk når I dømmer; den minste som den største skal I høre på. I skal ikke være redde for nogen, for dommen hører Gud til. Men om nogen sak er for vanskelig for eder, skal I føre den frem for mig; så vil jeg høre på den.
Kada ku nuna sonkai a cikin hukuncinku, ku saurari kowane ɓangare, babba da ƙarami, kada ku ji tsoron wani, gama hukunci na Allah ne. Ku kawo kowane batun da ya sha ƙarfinku, zan kuwa saurare shi.”
18 Og på samme tid bød jeg eder alt det I skulde gjøre.
A wancan lokacin kuwa na faɗa muku dukan abin da ya kamata ku yi.
19 Så brøt vi op fra Horeb og drog gjennem hele den store og forferdelige ørken som I har sett, på veien til amoritter-fjellene, således som Herren vår Gud bød oss; og vi kom til Kades-Barnea.
Sa’an nan, muka kama hanya daga Horeb muka ratsa wajen ƙasar tudun Amoriyawa ta dukan hamadarta mai fāɗi, da kuma mai bantsoron da kuka gani, muka kuma kai Kadesh Barneya yadda Ubangiji, Allahnmu ya umarce mu.
20 Da sa jeg til eder: Nu er I kommet til amoritter-fjellene, som Herren vår Gud vil gi oss.
Sai na ce muku, “Kun iso ƙasar tudun Amoriyawa, wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.
21 Se, Herren din Gud har gitt landet i din vold; dra op og innta det, som Herren, dine fedres Gud, har tilsagt dig! Frykt ikke og vær ikke redd!
Duba, Ubangiji Allahnku ya ba ku ƙasar. Ku haura ku mallake ta yadda Ubangiji Allahn kakanninku ya faɗa muku. Kada ku ji tsoro, kada ku fid da zuciya.”
22 Da kom I til mig alle sammen og sa: La oss sende folk i forveien for oss, så de kan utspeide landet for oss og gi oss beskjed om hvad vei vi skal dra dit op, og hvad byer vi kommer til!
Sai dukanku kuka zo wurina kuka ce, “Bari mu aiki mutane su yi gaba su leƙi mana asirin ƙasar, su kuma kawo mana labari game da hanyar da za mu bi, da kuma biranen da za mu shiga.”
23 Dette syntes jeg godt om, og jeg tok ut blandt eder tolv menn, én mann for hver stamme.
Ra’ayin nan naku ya yi mini kyau, saboda haka na zaɓe ku goma sha biyu, mutum guda daga kowace kabila.
24 Og de tok avsted og drog op i fjellene og kom til Eskol-dalen; og de utspeidet landet.
Suka tafi, suka haura zuwa ƙasar tudu, suka kai Kwarin Eshkol, suka leƙo asirin ƙasar.
25 Og de tok med sig av landets frukter ned til oss, og de gav oss beskjed tilbake og sa: Det land som Herren vår Gud vil gi oss, er et godt land.
Suka ɗebi’ya’yan itatuwan ƙasar, suka sauko mana da su, suka kuma ba da labari cewa, “Ƙasar da Ubangiji Allahnmu yake ba mu, kyakkyawa ce.”
26 Men I vilde ikke dra dit op; I var gjenstridige mot Herrens, eders Guds ord.
Amma ba ku yi niyya ku haura ba, kuka yi tawaye gāba da umarnin Ubangiji Allahnku.
27 Og I knurret i eders telter og sa: Herren hater oss; derfor har han ført oss ut av Egyptens land og vil gi oss i amorittenes hånd og ødelegge oss.
Kuka yi gunaguni a cikin tentunanku, kuna cewa, “Ubangiji ya ƙi mu; shi ya sa ya fitar da mu daga Masar don yă ba da mu ga hannuwan Amoriyawa su hallaka mu.
28 Hvad er det for et land vi skal dra op til! Våre brødre har gjort vårt hjerte mistrøstig ved å si: Det er et folk som er større og høiere enn vi, og de har store byer med murer som når til himmelen; og der så vi også anakittenes barn.
Ina za mu?’Yan’uwanmu suka sa muka fid da zuciya. Suka ce, ‘Mutanen sun fi mu ƙarfi, sun kuma fi mu tsayi; biranen manya ne, da katanga har sama. Mun ma ga Anakawa a can.’”
29 Da sa jeg til eder: I skal ikke forferdes og ikke være redde for dem;
Sai na ce muku, “Kada ku firgita; kada ku ji tsoronsu.
30 Herren eders Gud, som går foran eder, han skal stride for eder, således som I så han gjorde for eder i Egypten
Ubangiji Allahnku yana a gabanku, zai yi yaƙi saboda ku, kamar yadda ya yi a kan idanunku a Masar,
31 og i ørkenen du har sett, der hvor Herren din Gud bar dig som en mann bærer sitt barn, på hele den vei I har vandret til I kom til dette sted.
da kuma a cikin hamada. A can ma kun ga yadda Ubangiji Allahnku ya riƙe ku ko’ina da kuka tafi, kamar yadda mahaifi yakan riƙe ɗansa, sai da kuka kai wannan wuri.”
32 Men allikevel trodde I ikke på Herren eders Gud,
Duk da haka, ba ku amince da Ubangiji Allahnku ba,
33 han som gikk foran eder på veien for å søke ut leirplass for eder, om natten i en ild, så I kunde se den vei I skulde gå, og om dagen i en sky.
shi da ya sha gabanku a tafiyarku, cikin wuta da dad dare da kuma girgije da rana, don yă nemi wurare domin ku kafa sansani, don kuma yă nuna muku hanyar da za ku bi.
34 Da Herren hørte eders tale, blev han vred og svor:
Da Ubangiji ya ji abin da kuka faɗa, sai ya husata, ya kuma yi rantsuwa ya ce,
35 Sannelig, ikke nogen av disse menn, av denne onde slekt, skal se det gode land jeg har svoret å ville gi eders fedre -
“Babu wani a cikin wannan muguwar tsara da zai ga ƙasa mai kyau da na rantse zan ba wa kakanninku,
36 ingen uten Kaleb, Jefunnes sønn; han skal få se det; ham og hans barn vil jeg gi det land han har trådt på med sin fot, for han har trolig fulgt Herren.
sai dai Kaleb ɗan Yefunne. Zai gan ta, zan ba shi duk ƙasar da tafin ƙafarsa ta taka, shi da zuriyarsa, gama ya bi Ubangiji da zuciya ɗaya.”
37 Også mig blev Herren vred på for eders skyld og sa: Heller ikke du skal komme der inn.
Saboda ku Ubangiji ya husata da ni, ya kuma ce, “Kai ma, ba za ka shiga ƙasar ba.
38 Josva, Nuns sønn, som går dig til hånde, han skal komme der inn; styrk ham, for han skal skifte det ut til arv blandt Israel.
Amma mataimakinka, Yoshuwa ɗan Nun, zai shiga. Ka ƙarfafa shi gama shi ne zai jagoranci Isra’ila su gāje ta.
39 Og eders barn, som I sa vilde bli til rov, og eders sønner, som ennu ikke kan skille godt fra ondt, de skal komme der inn, dem vil jeg gi det, og de skal ta det i eie.
Amma’ya’yanku ƙanana waɗanda ba su san mugunta ko nagarta ba, waɗanda kuke tsammani za a kwashe su ganima, su za su shiga ƙasar. Zan ba da ita gare su, za su kuwa mallake ta.
40 Men vend I om og ta ut i ørkenen, på veien til det Røde Hav!
Amma ku kam, sai ku juya, ku koma cikin hamada ta hanyar Jan Teku.”
41 Da svarte I og sa til mig: Vi har syndet mot Herren; nu vil vi dra op og stride, således som Herren vår Gud har befalt oss. Og I omgjordet eder med eders stridsvåben hver og en, og I holdt det for en lett sak å dra op i fjellene.
Sai kuka amsa, kuka ce, “Mun yi zunubi ga Ubangiji. Za mu haura mu yi yaƙi yadda Ubangiji Allahnmu ya umarce mu.” Saboda haka kowannenku ya yi ɗamara da kayan yaƙinsa, kuka yi tsammani zai zama muku da sauƙi ku ci ƙasar tuddai da yaƙi.
42 Da sa Herren til mig: Si til dem: I skal ikke dra op, og I skal ikke stride; for jeg er ikke med eder; I kommer bare til å bli slått av eders fiender.
Amma Ubangiji ya ce mini, “In faɗa muku, ‘Kada ku fāɗa musu da yaƙi, gama ba zai kasance tare da ku ba. Idan kuka kuskura, abokan gābanku za su murƙushe ku.’”
43 Og jeg talte til eder, men I hørte ikke på mig; I var gjenstridige mot Herrens ord og dristet eder til å dra op i fjellene.
Sai na faɗa muku, amma ba ku saurara ba. Kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji, a cikin jahilcinku kuwa kuka taka, kuka haura cikin ƙasar tudu.
44 Da drog amorittene, som bodde der i fjellene, ut mot eder, og de forfulgte eder likesom en bisverm, og de slo eder sønder og sammen i Se'ir og drev eder like til Horma.
Amoriyawan da suke zama a waɗannan tuddai, suka fito kamar tarin ƙudan zuma gāba da ku, suka kore ku, suka fatattake ku daga Seyir har zuwa Horma.
45 Og I vendte tilbake og gråt for Herrens åsyn; men Herren hørte ikke på eders klager og vendte ikke sitt øre til eder.
Kuka dawo, kuka yi kuka a gaban Ubangiji, amma bai kula da ku ba, balle yă saurare ku.
46 Og I måtte bli i Kades i lang tid, hele den tid I var der.
Haka kuwa kuka zauna a Kadesh kwanaki masu yawa, kuka ci lokaci a can.

< 5 Mosebok 1 >