< Job 29 >

1 Addidit quoque Iob, assumens parabolam suam, et dixit:
Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
2 Quis mihi tribuat, ut sim iuxta menses pristinos secundum dies, quibus Deus custodiebat me?
“Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
3 Quando splendebat lucerna eius super caput meum, et ad lumen eius ambulabam in tenebris?
lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
4 Sicut fui in diebus adolescentiæ meæ, quando secreto Deus erat in tabernaculo meo?
Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
5 Quando erat Omnipotens mecum: et in circuitu meo pueri mei?
lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
6 Quando lavabam pedes meos butyro, et petra fundebat mihi rivos olei?
lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
7 Quando procedebam ad portam civitatis, et in platea parabant cathedram mihi?
“Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
8 Videbant me iuvenes, et abscondebantur: et senes assurgentes stabant.
matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
9 Principes cessabant loqui, et digitum superponebant ori suo.
sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
10 Vocem suam cohibebant duces, et lingua eorum gutturi suo adhærebat.
Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
11 Auris audiens beatificabat me, et oculus videns testimonium reddebat mihi.
Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
12 Eo quod liberassem pauperem vociferantem, et pupillum, cui non esset adiutor.
domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
13 Benedictio perituri super me veniebat, et cor viduæ consolatus sum.
Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
14 Iustitia indutus sum: et vestivi me, sicut vestimento et diademate, iudicio meo.
Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
15 Oculus fui cæco, et pes claudo.
Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
16 Pater eram pauperum: et causam quam nesciebam, diligentissime investigabam.
Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
17 Conterebam molas iniqui, et de dentibus illius auferebam prædam.
Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
18 Dicebamque: In nidulo meo moriar, et sicut palma multiplicabo dies.
“Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
19 Radix mea aperta est secus aquas, et ros morabitur in messione mea.
Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
20 Gloria mea semper innovabitur, et arcus meus in manu mea instaurabitur.
Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
21 Qui me audiebant, expectabant sententiam, et intenti tacebant ad consilium meum.
“Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
22 Verbis meis addere nihil audebant, et super illos stillabat eloquium meum.
Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
23 Expectabant me sicut pluviam, et os suum aperiebant quasi ad imbrem serotinum.
Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
24 Siquando ridebam ad eos, non credebant, et lux vultus mei non cadebat in terram.
Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
25 Si voluissem ire ad eos, sedebam primus: cumque sederem quasi rex, circumstante exercitu, eram tamen mœrentium consolator.
Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.

< Job 29 >