< Job 36 >

1 Addens quoque Eliu, hæc locutus est:
Elihu ya ci gaba,
2 Sustine me paululum, et indicabo tibi: adhuc enim habeo quod pro Deo loquar.
“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 Repetam scientiam meam a principio, et operatorem meum probabo iustum.
Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
4 Vere enim absque mendacio sermones mei, et perfecta scientia probabitur tibi.
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
5 Deus potentes non abiicit, cum et ipse sit potens.
“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
6 Sed non salvat impios, et iudicium pauperibus tribuit.
Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
7 Non auferet a iusto oculos suos, et reges in solio collocat in perpetuum, et illi eriguntur.
Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
8 Et si fuerint in catenis, et vinciantur funibus paupertatis.
Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
9 Indicabit eis opera eorum, et scelera eorum, quia violenti fuerunt.
yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
10 Revelabit quoque aurem eorum, ut corripiat: et loquetur, ut revertantur ab iniquitate.
Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
11 Si audierint et observaverint, complebunt dies suos in bono, et annos suos in gloria:
In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
12 Si autem non audierint, transibunt per gladium, et consumentur in stultitia.
Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
13 Simulatores et callidi provocant iram Dei, neque clamabunt cum vincti fuerint.
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
14 Morietur in tempestate anima eorum, et vita eorum inter effeminatos.
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
15 Eripiet de angustia sua pauperem, et revelabit in tribulatione aurem eius.
Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
16 Igitur salvabit te de ore angusto latissime, et non habente fundamentum subter se: requies autem mensæ tuæ erit plena pinguedine.
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17 Causa tua quasi impii iudicata est, causam iudiciumque recipies.
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18 Non te ergo superet ira, ut aliquem opprimas: nec multitudo donorum inclinet te.
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19 Depone magnitudinem tuam absque tribulatione, et omnes robustos fortitudine.
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20 Ne protrahas noctem, ut ascendant populi pro eis.
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21 Cave ne declines ad iniquitatem: hanc enim cœpisti sequi post miseriam.
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
22 Ecce, Deus excelsus in fortitudine sua, et nullus ei similis in legislatoribus.
“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
23 Quis poterit scrutari vias eius? aut quis potest ei dicere: Operatus es iniquitatem?
Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
24 Memento quod ignores opus eius, de quo cecinerunt viri.
Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
25 Omnes homines vident eum, unusquisque intuetur procul.
Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
26 Ecce, Deus magnus vincens scientiam nostram: numerus annorum eius inæstimabilis.
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 Qui aufert stillas pluviæ, et effundit imbres ad instar gurgitum.
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28 Qui de nubibus fluunt, quæ prætexunt cuncta desuper.
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
29 Si voluerit extendere nubes quasi tentorium suum.
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30 Et fulgurare lumine suo desuper, cardines quoque maris operiet.
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31 Per hæc enim iudicat populos, et dat escas multis mortalibus.
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32 In manibus abscondit lucem, et præcepit ei ut rursus adveniat.
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
33 Annunciat de ea amico suo, quod possessio eius sit, et ad eam possit ascendere.
Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.

< Job 36 >