< Yeremia 34 >

1 Ketika Nebukadnezar raja Babel dengan angkatan perangnya yang diperkuat oleh pasukan-pasukan dari segala bangsa dan negara yang takluk kepadanya datang menyerang Yerusalem dan kota-kota di sekitarnya, TUHAN berbicara kepadaku.
Yayinda Nebukadnezzar sarkin Babilon da dukan sojojinsa da kuma dukan mulkokinsa da mutanen masarautar da yake mulki suna yaƙi da Urushalima da dukan garuruwan da suke kewaye, sai wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
2 Ia menyuruh aku pergi kepada Zedekia raja Yehuda, dan berkata begini, "Aku, TUHAN Allah Israel, akan menyerahkan kota ini kepada raja Babel dan ia akan membakarnya.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi wurin Zedekiya sarkin Yahuda ka faɗa masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa ƙone ta.
3 Engkau tak akan lolos, melainkan ditangkap dan diserahkan kepadanya. Engkau akan bertemu dan berbicara sendiri dengan dia, lalu engkau akan pergi ke Babel.
Ba za ka tsere daga hannunsa ba amma tabbatacce za a kama ka a kuma ba da kai gare shi. Za ka ga sarkin Babilon da idanunka, zai kuwa yi magana da kai fuska da fuska. Za ka kuwa tafi Babilon.
4 Tetapi dengarkan perkataan-Ku ini mengenai engkau, Zedekia! Engkau tidak akan tewas dalam pertempuran,
“‘Duk da haka ka ji alkawarin Ubangiji, ya Zedekiya sarkin Yahuda. Ga abin da Ubangiji yake cewa game da kai. Ba za ka mutu ta takobi ba;
5 melainkan mati dengan tentram. Dan sebagaimana rakyat membakar kemenyan ketika memakamkan leluhurmu yang memerintah sebelum engkau, begitu pula rakyat akan membakar kemenyan untukmu. Mereka akan berkabung dan berkata, 'Aduh! Raja kami sudah tiada!' Aku, TUHAN, telah berbicara."
za ka mutu cikin salama. Yadda mutane suka ƙuna wutar jana’iza don girmama kakanninka, sarakunan da suka riga ka, haka za su ƙuna wuta don girmama da kuma makokinka suna cewa, “Kaito, ya maigida!” Ni kaina na yi wannan alkawari, in ji Ubangiji.’”
6 Maka pesan TUHAN itu kusampaikan kepada Raja Zedekia di Yerusalem,
Sa’an nan annabi Irmiya ya faɗi dukan wannan wa Zedekiya sarkin Yahuda, a Urushalima,
7 ketika pasukan raja Babel sedang menyerang kota itu. Mereka juga menyerang kota Lakhis dan Aseka, dua kota berbenteng yang masih bertahan di Yehuda.
yayinda sojojin sarkin Babilon suna yaƙi da Urushalima da sauran garuruwan Yahuda waɗanda suka ragu, Lakish da Azeka. Waɗannan su ne birane masu katanga kaɗai a Yahuda.
8 Raja Zedekia dan penduduk Yerusalem mengadakan perjanjian untuk membebaskan
Maganar ta zo wa Irmiya daga Ubangiji bayan Sarki Zedekiya ya yi yarjejjeniya da duka mutane a Urushalima ya yi shelar’yanci wa bayi.
9 budak-budak Ibrani mereka, baik laki-laki maupun perempuan supaya tak ada seorang pun dari bangsa Israel yang memperbudak orang sebangsanya.
Kowa ya’yantar da bayinsa da suke Ibraniyawa, maza da mata; kada kowa ya riƙe bawa wanda yake mutumin Yahuda.
10 Seluruh rakyat dan para pejabat pemerintah yang telah mengadakan perjanjian untuk membebaskan budak-budak mereka dan tak akan memperbudaknya lagi, betul-betul melepaskan budak-budak mereka itu.
Saboda haka dukan fadawa da mutane suka yi yarjejjeniyar cewa za su’yantar da bayinsu maza da mata ba za su kuwa ƙara riƙe su bayi ba. Suka yarda, suka kuma sake su.
11 Tapi kemudian mereka berubah pikiran, lalu mengambil kembali budak-budak itu, dan memaksanya menjadi budak lagi.
Amma daga baya suka canja ra’ayoyinsu suka maido bayinsu suka kuma sāke bautar da su.
12 Maka TUHAN, Allah Israel, menyuruh aku berkata begini kepada orang-orang itu, "Ketika Aku membawa leluhurmu keluar dari Mesir dan membebaskan mereka dari perbudakan, Aku telah membuat perjanjian dengan mereka.
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa na yi alkawari da kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga ƙasar bauta. Na ce,
14 Aku berkata bahwa semua budak Ibrani yang telah melayani enam tahun lamanya, harus dibebaskan pada akhir tahun ketujuh. Tapi leluhurmu tidak mau memperhatikan atau mendengarkan apa yang Kukatakan itu.
‘A kowace shekara ta bakwai dole kowannenku yă’yantar da duk wani ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa wanda aka sayar masa. Bayan ya yi muku hidima shekaru shida, dole ku bar shi yă tafi’yantacce.’ Amma kakanninku ba su saurare ni ba, ba su ji ni ba.
15 Beberapa hari yang lalu kamu mengubah kelakuanmu dan melakukan yang menyenangkan hati-Ku. Kamu semua menyetujui untuk membebaskan budak-budak sebangsamu, dan membuat perjanjian dengan Aku di dalam Rumah-Ku.
Bai daɗe ba da kuka tuba, kuka kuma yi abin da yake mai kyau a idona. Kowannenku ya yi shelar’yanci ga ɗan’uwansa. Kun ma yi yarjejjeniya a gabana a gidan da ake kira da Sunana.
16 Pejabat-pejabat pemerintah Yehuda dan Yerusalem bersama para pegawai istana, imam-imam dan semua pengawas tanahmu telah mensahkan perjanjian itu dengan menyembelih sapi, memotongnya menjadi dua, dan berjalan di antara kedua potongan itu. Tapi, kemudian kamu berubah pikiran dan menghina Aku. Budak-budak yang sudah kamu bebaskan sesuai dengan keinginan mereka, kamu ambil kembali dan paksakan untuk menjadi budak lagi. Karena itu, Aku, TUHAN, berkata bahwa kamu telah melanggar perintah-Ku, dan tidak mentaati syarat-syaratnya, sebab kamu tidak membebaskan sesamamu bangsa Israel. Nah, sekarang baiklah Aku memberikan kebebasan kepadamu: kebebasan untuk tewas dalam pertempuran atau oleh wabah penyakit atau oleh kelaparan. Aku akan memperlakukan kamu seperti kamu memperlakukan sapi yang kamu sembelih itu. Aku akan membuat segala bangsa di dunia merasa ngeri melihat apa yang Kulakukan terhadap kamu.
Amma yanzu kun juya kun kuma ɓata sunana; kowannenku ya mayar da bayi maza da matan da kuka’yantar su tafi inda suka ga dama. Kun sāke tilasta su su zama bayinku.
“Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, kun yi mini rashin biyayya; ba ku yi shelar’yanci don’yan’uwanku ba. Saboda haka yanzu na yi muku shelar’yanci in ji Ubangiji,’yanci ga mutuwa ta takobi, annoba da kuma yunwa. Zan sa ku zama abin ƙyama ga sauran mulkokin duniya.
Mutanen da suka keta alkawarina da ba su cika sharuɗan alkawarin da suka yi a gabana ba, zan yi da su kamar ɗan maraƙin da suka yanka biyu suka bi ta tsakiyarsa.
Shugabannin Yahuda da Urushalima, fadawa, firistoci da kuma dukan mutanen ƙasar waɗanda suka bi tsakanin ɗan maraƙin da aka yanka,
20 Aku akan menyerahkan kamu kepada musuh yang ingin membunuh kamu. Mayatmu akan dimakan burung dan binatang buas.
zan ba da su ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namun jeji.
21 Zedekia raja Yehuda dan para pejabat pemerintahnya akan Kuserahkan kepada orang-orang yang ingin membunuh mereka. Aku akan menyerahkan mereka kepada tentara Babel, yang kini telah meninggalkan kamu.
“Zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda da fadawansa ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu, ga sojojin sarkin Babilon, waɗanda suke janye daga gare ku.
22 Aku akan memberi aba-aba supaya mereka kembali ke kota ini, lalu menyerang, merebut, dan membakarnya. Kota-kota Yehuda akan Kujadikan seperti padang gurun yang tidak didiami orang. Aku, TUHAN, telah berbicara."
Zan yi umarni, in ji Ubangiji, zan kuma komo da su wannan birni. Za su kuwa yi yaƙi da ita, su ƙwace ta su kuma ƙone ta. Zan kuma mai da garuruwan Yahuda kufai don kada wani ya zauna a can.”

< Yeremia 34 >