< 1 Tawarikh 22 >

1 Maka kata Daud, "Di tempat inilah harus dibangun Rumah TUHAN Allah. Dan di mezbah inilah orang Israel harus mempersembahkan kurban bakaran mereka kepada TUHAN."
Sai Dawuda ya ce, “Gidan Ubangiji Allah zai kasance a nan, haka kuma bagaden hadaya ta ƙonawa don Isra’ila.”
2 Raja Daud menyuruh mengumpulkan semua orang asing yang tinggal di negeri Israel, lalu ia mempekerjakan mereka. Sebagian dari mereka memahat batu untuk membangun Rumah TUHAN.
Dawuda kuwa ya umarta a tattara baƙin da suke zama a Isra’ila, daga cikinsu ya sa masu farfasa duwatsu don su shirya duwatsun da aka sassaƙa saboda ginin gidan Allah.
3 Untuk membuat paku dan engsel bagi pintu-pintu gerbang Rumah TUHAN itu, Daud mengumpulkan banyak sekali besi. Ia juga mengumpulkan begitu banyak perunggu, sehingga tidak dapat ditimbang.
Ya tanada ƙarfe mai yawa don ƙusoshi saboda ƙyamaren hanyoyin shiga da kuma saboda mahaɗai, da ƙarin tagulla fiye da ƙirge.
4 Dari orang Tirus dan Sidon ia memesan sejumlah besar kayu cemara Libanon.
Ya kuma tanada gumaguman al’ul masu yawa fiye da ƙirge, gama Sidoniyawa da mutanen Taya sun kawo su wa Dawuda da yawa.
5 Daud melakukan semuanya itu karena ia berpikir begini: "Aku harus mempersiapkan apa yang diperlukan untuk pembangunan Rumah TUHAN. Sebab Salomo putraku masih muda dan kurang pengalaman, sedangkan Rumah TUHAN yang akan dibangunnya itu harus sangat megah dan termasyhur di seluruh dunia." Maka sebelum Daud meninggal, ia menyediakan banyak sekali bahan bangunan.
Dawuda ya ce, “Ɗana Solomon matashi ne kuma bai gogu ba, kuma gidan da za a gina wa Ubangiji zai zama mai ƙayatarwa ƙwarai, sananne da kuma mai daraja a idon dukan al’ummai. Saboda haka zan yi shirye-shirye saboda shi.” Sai Dawuda ya yi ɗumbun shirye-shirye kafin mutuwarsa.
6 Daud memanggil putranya, Salomo, dan memerintahkan dia untuk mendirikan rumah bagi TUHAN Allah yang disembah oleh umat Israel.
Sa’an nan ya kira ɗansa Solomon ya umarce shi yă gina gida domin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
7 Kata Daud kepada Salomo, "Anakku, sudah lama aku berniat mendirikan sebuah rumah untuk menghormati TUHAN Allahku.
Dawuda ya ce wa Solomon, “Ɗana, na yi niyya a zuciyata in gina gida saboda Sunan Ubangiji Allahna.
8 Tetapi TUHAN berkata bahwa aku terlalu sering bertempur dan telah membunuh banyak orang. Karena itu Ia tidak mengizinkan aku mendirikan rumah untuk Dia.
Amma wannan maganar Ubangiji ta zo mini, ‘Ka zub da jini mai yawa ka kuma yi yaƙe-yaƙe masu yawa. Ba za ka gina gida domin Sunana ba, domin ka zub da jini da yawa a duniya a idona.
9 Meskipun begitu, Ia telah memberikan kepadaku janji ini: 'Engkau akan mendapat seorang putra yang akan memerintah dengan tentram, sebab Aku akan menolong dia sehingga tak ada musuh yang memerangi dia. Ia akan dinamakan Salomo sebab selama ia memerintah, Aku akan memberikan ketentraman dan keamanan di seluruh Israel.
Amma za ka haifi ɗa wanda zai zama mutumin salama da kuma hutu, zan kuma ba shi hutu daga dukan abokan gābansa a kowane gefe. Za a kira shi Solomon, zai kuma kawo wa Isra’ila salama da natsuwa a zamanin mulkinsa.
10 Putramu itulah yang akan mendirikan rumah untuk-Ku. Dia akan menjadi anak-Ku dan Aku menjadi bapaknya. Takhta kerajaan Israel akan tetap pada keturunannya untuk selama-lamanya.'"
Shi ne wanda zai gina gida saboda Sunana. Zai zama ɗana, ni kuma zan zama mahaifinsa. Zan kafa kujerar sarautarsa a bisa Isra’ila har abada.’
11 Lalu kata Daud lagi, "Sekarang, anakku, semoga TUHAN Allahmu selalu menolong engkau. Dan semoga engkau berhasil mendirikan rumah untuk TUHAN seperti yang telah dijanjikan-Nya.
“Yanzu, ɗana, Ubangiji ya kasance tare da kai, bari kuma ka yi nasara ka kuma gina gidan Ubangiji Allahnka, kamar yadda ya ce za ka yi.
12 Dan mudah-mudahan TUHAN Allahmu memberikan kepadamu kebijaksanaan dan pengertian untuk memerintah Israel sesuai dengan hukum-hukum-Nya.
Bari Ubangiji ya ba ka basira da fahimi sa’ad da ya sa ka shugaba a bisa Isra’ila, saboda ka kiyaye dokar Ubangiji Allahnka.
13 Kalau engkau mentaati semua hukum yang diberikan TUHAN kepada Musa untuk bangsa Israel, engkau akan berhasil. Engkau harus yakin dan berani. Jangan takut menghadapi apa pun juga.
Ta haka za ka yi nasara in ka mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa saboda Isra’ila. Ka yi ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa. Kada ka ji tsoro ko ka fid da zuciya.
14 Mengenai Rumah TUHAN itu aku sudah berusaha sungguh-sungguh untuk mengumpulkan 3.400 ton emas dan lebih dari 34.000 ton perak. Selain itu ada perunggu dan besi yang tidak terhitung banyaknya. Kayu dan batu pun sudah kusiapkan, tetapi engkau harus menambahkannya lagi.
“Na sha wahala da yawa don in yi tanadi talentin dubu ɗari na zinariya, talenti miliyon na azurfa, ɗumbun tagulla da ƙarfe da suka wuce ƙirge da katako da dutse saboda haikalin Ubangiji. Za ka iya ƙara su.
15 Engkau mempunyai banyak pekerja. Ada yang dapat bekerja di tambang batu, ada tukang kayu, tukang batu dan banyak sekali pengrajin yang pandai mengerjakan
Kana da ma’aikata masu yawa, masu fafarshe duwatsu, masu gini da masu aikin katako, da kuma gwanaye a kowane irin aikin
16 emas, perak, perunggu dan besi. Nah, mulailah segera! Semoga TUHAN menolong engkau."
zinariya da azurfa, tagulla da ƙarfe, masu sana’a waɗanda suka wuce ƙirge. Yanzu ka fara aiki, Ubangiji kuma ya kasance tare da kai.”
17 Lalu Daud menyuruh semua pemimpin Israel membantu Salomo.
Sai Dawuda ya umarta dukan shugabannin Isra’ila su taimake ɗansa Solomon.
18 Katanya, "TUHAN Allahmu sudah menolong kalian, dan memberi damai serta ketentraman di seluruh negeri. Ia sudah memungkinkan aku mengalahkan semua bangsa yang dulu tinggal di negeri ini. Sekarang mereka takluk kepadamu dan kepada TUHAN.
Ya ce musu, “Ba Ubangiji Allahnku yana tare da ku ba? Bai kuma ba ku hutu a kowane gefe ba? Gama ya ba da mazaunan ƙasar gare ni, ƙasar kuma ta Ubangiji ce da mutanensa.
19 Jadi, hendaklah kalian mengabdi kepada TUHAN Allahmu dengan segenap jiwa ragamu. Mulailah membangun rumah untuk TUHAN, supaya Peti Perjanjian-Nya dan semua perkakas lain yang dipakai khusus untuk ibadat dapat ditempatkan di situ."
Yanzu fa sai ku sa zuciyarku da ranku ga neman Ubangiji Allahnku. Ku fara ginin wuri mai tsarki na Ubangiji Allah, don ku kawo akwatin alkawarin Ubangiji da kayayyaki masu tsarki na Allah a cikin haikalin da za a gina saboda Sunan Ubangiji.”

< 1 Tawarikh 22 >