< Luka 5 >

1 Ya zama sa'adda mutane sun taru a wurin Yesu suna sauraron maganar Allah, yana kuma yana tsaye a bakin tabkin Janisarata.
Ngelinye ilanga uJesu emi eduze kweChibi laseGenezaretha abantu beminyezelana kuye belalela ilizwi likaNkulunkulu,
2 Ya ga jiragen ruwa biyu tsaye a bakin tabkin. Masu kamun kifin kuwa sun fita daga cikin jiragen suna wanke tarunsu.
wabona ekhunjini lechibi izikepe ezimbili zitshiywe khonapho ngabagoli benhlanzi ababegezisa omambule babo.
3 Yesu ya shiga daya daga cikn jiragen wanda shike na Bitrus ne, sai ya umarce shi ya dan zakuda da jirgin daga bakin tabkin kadan zuwa cikin ruwa. Sai ya zauna ya kuma koya wa mutane daga cikin jirgin.
Wangena kwesinye isikepe esasingesikaSimoni, wamcela ukuthi akathi gudlu asuke kancane okhunjini. Wasehlala phansi wafundisa abantu ehlezi esikepeni.
4 Da ya gama magana, ya ce wa Siman, “Zakuda jirgin zuwa wuri mai zurfi sa'annan ka zuba tarunka domin kamu.”
Eseqedile ukukhuluma wathi kuSimoni, “Gwedla ungene enzikini uphosele omambule bakho ukuze ubambe inhlanzi.”
5 Siman ya amsa ya ce, “Ubangiji, mun yi aiki dukan dare bamu kama komai ba, amma bisa ga maganarka, zan jefa tarun.”
USimoni waphendula wathi, “Nkosi, sisebenze gadalala ubusuku bonke, kodwa kasibambanga lutho. Kodwa njengoba usitsho njalo ngizabehlisa omambule.”
6 Da sun yi haka, suka kama kifaye da yawan gaske, har tarunsu suna yagewa.
Kwathi sebenze njalo babamba inhlanzi ezaba zinengi kwaze kwaqalisa ukudabuka omambule.
7 Sai suka roki abokan aikinsu da ke a dayan jirgin su zo su taimake su. Suka zo sun cika jiragen biyu da kifaye, har suka fara nutsewa.
Basebebiza abakhula babo kwesinye isikepe ukuthi bazobelekelela. Beza abakhula babo kwesinye isikepe ukuthi bazobelekelela. Beza bazigcwalisa zombili izikepe zathi phamu zaze zaqalisa ukutshona.
8 Amma Siman Bitrus, da ya ga haka, ya russuna a gaban Yesu, yana cewa, “Ka rabu da ni Ubangiji, gama ni mai zunubi ne.”
Kwathi uSimoni Phethro ekubona lokhu wazilahla phansi phambi kukaJesu wathi, “Suka kimi, Nkosi; ngingumuntu oyisoni!”
9 Domin ya yi mamaki, da dukan wadanda suke tare da shi, sabili da yawan kifaye da suka kama.
Ngoba yena labakhula bakhe babemangele ngenhlanzi ababezibambile,
10 Wannan ya hada da Yakubu da Yahaya 'ya'yan Zabadi abokan aikin Siman. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, domin daga yanzu, za ka kama mutane.”
kwamangalisa njalo uJakhobe loJohane amadodana kaZebhediya, ababe phathisana loSimoni. UJesu wasesithi kuSimoni, “Ungesabi; kusukela manje usuzagola abantu.”
11 Da sun kawo jiragensu waje kan kasa, suka bar komai suka kuma bi shi.
Basebedonsela izikepe zabo okhunjini batshiya konke bamlandela.
12 Sa'adda yana daya daga cikin biranen, wani mutum dauke da kuturta yana nan wurin. Da ya ga Yesu, ya fadi bisa fuskarsa kasa yana rokansa, yana cewa, “Ubangji, idan ka yarda, za ka iya tsarkake ni.”
Kwathi uJesu ekwelinye lamadolobho kweza indoda eyayigcwele ubulephero. Yathi ibona uJesu yathi mbo phansi ngobuso yamncenga yathi, “Nkosi, nxa uthanda ungangihlambulula.”
13 Yesu ya mika hanunsa ya taba shi, yana cewa, “Na yarda. Ka tsarkaka.” Sai nan da nan, kuturtar ta rabu da shi.
UJesu welula isandla sakhe wayithinta indoda leyo. Wathi, “Ngiyathanda. Hlambuluka!” Masinyane nje ubulephero bahle baphela.
14 Ya umarce shi kada ya gaya wa kowa, amma ya ce ma sa, “Tafi ka nuna kanka ga firist sa'annan ka mika hadaya domin tsarkakewarka, kamar yadda Musa ya umarta, a matsayin shaida a garesu.”
UJesu waseyilaya wathi, “Ungatsheli muntu kodwa hamba uyeziveza kumphristi ubusunikela umhlatshelo wokuhlanjululwa kwakho owamiswa nguMosi ukuze kube yibufakazi kubo.”
15 Amma labarinsa ya bazu nesa, taron mutane da yawa kuma suka zo wurinsa domin su ji shi, su kuma samu warkarwa daga cututtukansu.
Kodwa udumo lwakhe lwanda ngamandla, yikho amaxuku abantu eza ukuzamuzwa lokusiliswa emikhuhlaneni yabo.
16 Amma ya kan janye zuwa wuraren da babu kowa ya yi addu'a.
Kodwa kanengi uJesu wayesithi nyelele ayesithela ezindaweni ezithuleyo ayekhuleka.
17 Ya zama daya a cikin kwanakin da yake koyarwa, akwai Farisawa da malaman attaura da ke zaune a wurin wandanda suka zo daga kauyukan da suke kewaye da Galili da Yahudiya da kuma birnin Urushalima. Ikon Ubangiji yana tare da shi domin warkarwa.
Ngelinye ilanga elokhu efundisa, kwakuhlezi khonapho abaFarisi labafundisi bomthetho ababephuma emizini yonke yaseGalile abanye bevela eJudiya laseJerusalema. Amandla eNkosi ayekhona kuye ukuze asilise abagulayo.
18 A lokacin nan, wasu mutane suka zo dauke da wani mutum shanyayye a kan tabarma, suka kuma nemi yadda za su shigar da shi ciki, su kwantar da shi a gaban Yesu.
Kwafika amanye amadoda ethwele indoda eyayome umhlubulo ngecansi efuna ukungena laye endlini ambeke phambi kukaJesu.
19 Ba su iya samun hanyar da za su shigar da shi ba saboda taron, sai suka hau saman gidan, suka saukar da shi daga rufin, a kan tabarman sa, zuwa tsakiyar mutanen, dai dai a gaban Yesu.
Athi esehlulekile ngenxa yokuminyana kwabantu, akhwela ephahleni, amehlisela phansi ngesikhala amuthi qithi phakathi laphakathi kwabantu phambi kukaJesu.
20 Da ya ga bangaskiyarsu, Yesu ya ce, “Maigida, an gafarta zunubanka.”
Kwathi uJesu ebona ukholo lwawo wathi, “Mngane, izono zakho sezithethelelwe.”
21 Marubuta da Farisawa suka fara sukar wannan, suna cewa, “Wanene wannan da ke sabo? Wa zai iya gafarta zunubi, idan ba Allah kadai ba?”
AbaFarisi labafundisi bomthetho bakhonona bathi, “Ungubani yena lo umuntu okhuluma ehlambaza na? Ngubani ongathethelela izono ngaphandle kukaNkulunkulu kuphela?”
22 Amma da Yesu ya fahimci abin da suke tunani, sai ya amsa ya ce masu, “Don me kuke sukar wannan a zuciyarku?
UJesu wayekwazi abakucabangayo wasebuza wathi, “Kungani linakana izinto ezinje ezinhliziyweni zenu?
23 Wanne ne ya fi sauki a ce, 'An yafe zunubanka' ko kuwa a ce, 'Tashi ka yi tafiya?”
Yikuphi okulula: ukuthi, ‘Izono zakho sezithethelelwe,’ loba ukuthi, ‘Sukuma uhambe’?
24 Amma domin ku sani cewa Dan Mutum yana da yancin gafarta zunubai a duniya, na ce maka, 'Tashi, dauki tabarmanka, ka tafi gidanka.'”
Kodwa ukuze lazi ukuthi iNdodana yoMuntu ilamandla okuthethelela izono emhlabeni.” Wasesithi kuyo indoda eyome umhlubulo, “Sukuma, thatha icansi lakho uhambe uye ekhaya.”
25 Nan take, ya tashi a gabansu ya dauki tabarma da yake kwance; sai ya koma gidansa, yana daukaka Allah.
Masinyane wathi lothu phambi kwabo, wabutha ayekade elele phezu kwakho waya ekhaya edumisa uNkulunkulu.
26 Kowa yana ta mamaki kuma suka daukaka Allah. Suna cike da tsoro, suna cewa, “Yau mun ga abubuwan al'ajibi.”
Wonke umuntu wamangala, badumisa uNkulunkulu. Bamangala kakhulu bathi, “Lamuhla sibone izimanga.”
27 Bayan wadannan abubuwa sun faru, Yesu ya fito daga can sai ya ga wani mai karban haraji mai suna Lawi yana zama a wurin karban haraji. Ya ce masa, “Ka biyo ni.”
Ngemva kwalokhu uJesu waphuma wasebona umthelisi owayethiwa nguLevi ehlezi endaweni yakhe yokuthelisa. UJesu wathi kuye, “Ngilandela,”
28 Sai Lawi ya bar komai, ya tashi, ya bi shi.
uLevi wasukuma watshiya konke wamlandela.
29 Lawi kuma ya shirya gagarumar liyafa a gidansa, kuma akwai masu karban haraji da yawa a nan, da wasu mutane da ke zama a gaban teburin liyafar suna cin abinci tare da su.
ULevi wasesenzela uJesu idili elikhulu endlini yakhe kukhona ixuku labathelisi labanye besidla labo.
30 Amma Farisawa da Marubuta suka fara korafi ga almajiransa, suna cewa, “Don menene kuna ci da sha tare da masu karban haraji da mutane masu zunubi?”
Kodwa abaFarisi labafundisi bomthetho abeqembu labo basola kubafundi bakhe bathi, “Lenzelani ukudla linathe labathelisi kanye lezoni na?”
31 Yesu ya amsa masu, “Masu lafiya basu bukatar likita, wadanda ke marasa lafiya kadai ke bukatar likita.
UJesu wabaphendula wathi, “Kakusibo abaphilayo abaswela umelaphi, kodwa ngabagulayo.
32 Ban zo domin kiran masu adalci ba, amma na zo ne domin kiran masu zunubi zuwa ga tuba.”
Kangilandanga ukubiza abulungileyo, kodwa ukubiza izoni ukuba ziphenduke.”
33 Sun ce masa, “Almajiran Yahaya sukan yi azumi da addu'a, kuma almajiran Farisawa ma sukan yi haka. Amma almajiranka suna ci suna sha?”
Bathi kuye, “Abafundi bakaJohane bazila kanengi bekhuleka njalo labafundi babaFarisi labo benza njalo, kodwa abakho bahlala besidla, benatha.”
34 Yesu ya ce masu, “Akwai wanda zai sa abokan ango su yi azumi, a lokacin da shi ango yana tare da su?
UJesu waphendula wathi, “Kungenzeka yini ukuzilisa izethekeli zomyeni emthimbeni umyeni eseselazo na?
35 Amma kwanaki na zuwa wadanda za a dauke ango daga wurinsu, a kwanakin za su yi azumi.”
Kodwa sizafika isikhathi lapho umyeni ezasuswa kuzo; zizazila ngalezonsuku.”
36 Sai Yesu ya sake fada masu wani misali. “Babu wanda zai yage kyalle daga sabuwar tufa, ya kuma yi amfani da ita ya dinka tsohuwar tufa. Idan ya yi hakannan, zai yage sabuwar tufar, kuma kyallen daga sabuwar tufar ba zai dace da kyallen tsohuwar tufar ba.
Wabatshela umzekeliso lo: “Kakho odabula isichibi esigqokweni esitsha asithungele esigqokweni esidala. Angenzenjalo, uzakuba esesidabule isigqoko esitsha, ikanti isichibi sesitsha kasiyikufanela esidala.
37 Kuma, babu mutum da zai sa sabon ruwan inabi a cikin tsofafin salkuna. Idan ya yi haka, sabon ruwan inabin zai fasa salkunan, kuma ruwan inabin din zai zube, salkunan kuma za su lallace.
Njalo kakho othela iwayini elitsha emigodleni yezikhumba emidala. Angenza njalo iwayini elitsha lizaziqhekeza izikhumba iwayini livuze kuthi lemigodla yezikhumba leyo ihle yonakale.
38 Amma dole ne a sa sabon ruwan inabi a sabobin salkuna.
Hatshi, iwayini elitsha lithelwa emigodleni yezikhumba emitsha.
39 Babu wanda zai yi marmarin sabon ruwan inabi bayan da ya sha tsohon, gama zai ce, “Tsohon ya fi sabon.”
Njalo kakho othi eseqale wanatha iwayini elidala afune elitsha, ngoba uthi, ‘Elidala lingcono.’”

< Luka 5 >