< Luka 2 >

1 Ananan cikin kwanakin, sai Kaisar Augustas ya yi shela ya umarta a kidaya dukan mutane da ke zaune a cikin duniya.
And it came to pass, that in those days there went out a decree from Caesar Augustus, that the whole world should be enrolled.
2 Wannan itace kidaya ta farko da aka yi lokacin da Kiriniyus yake mulkin Suriya.
This enrolling was first made by Cyrinus, the governor of Syria.
3 Sabili da haka, kowa ya koma garinsa domin a yi masa rijista domin kidayan.
And all went to be enrolled, every one into his own city.
4 Yusufu kuma ya tashi ya bar birnin Nazarat zuwa garin Baitalami da ke Yahudiya, wanda ake kuma kira birnin Dauda, domin shi daga zuriyar iyalin Dauda ne.
And Joseph also went up from Galilee, out of the city of Nazareth into Judea, to the city of David, which is called Bethlehem: because he was of the house and family of David,
5 Ya je can ya yi rijista tare da Maryamu, wadda yake tashi tana kuma da juna biyu.
To be enrolled with Mary his espoused wife, who was with child.
6 Ya zama sa'adda suke can, lokaci ya yi da za ta haifi danta.
And it came to pass, that when they were there, her days were accomplished, that she should be delivered.
7 Ta haifi da, dan farinta kuwa, ta nade shi da kyau da 'yan tsummoki. Ta sa shi cikin wani kwami na dabbobi, gama babu daki dominsu a masaukin.
And she brought forth her firstborn son, and wrapped him up in swaddling clothes, and laid him in a manger; because there was no room for them in the inn.
8 A cikin wannan yankin, akwai makiyaya wadanda suke zama a sarari suna tsaron garken tumakinsu da dare.
And there were in the same country shepherds watching, and keeping the night watches over their flock.
9 Nan da nan, sai mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare su, daukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, sai suka figita kwarai.
And behold an angel of the Lord stood by them, and the brightness of God shone round about them; and they feared with a great fear.
10 Sai mala'ikan ya ce masu, “Kada ku ji tsoro, domin na kawo maku labari mai dadi da zai kawo murna da yawa ga dukan mutane.
And the angel said to them: Fear not; for, behold, I bring you good tidings of great joy, that shall be to all the people:
11 Yau an haifi maku mai ceto a cikin birnin Dauda! Shine Almasihu Ubangiji!
For, this day, is born to you a Saviour, who is Christ the Lord, in the city of David.
12 Wannan itace alama da za a ba ku. Za ku ga dan jariri nade cikin 'yan tsummoki kwance cikin kwamin dabbobi.”
And this shall be a sign unto you. You shall find the infant wrapped in swaddling clothes, and laid in a manger.
13 Nan take, sai ga babban taro daga sama tare da mala'ikan suna yabon Allah, suna cewa,
And suddenly there was with the angel a multitude of the heavenly army, praising God, and saying:
14 “Daukaka ga Allah daga bisa, bari salama ta kasance a duniya tsakanin mutanen da ya ke jin dadinsu.”
Glory to God in the highest; and on earth peace to men of good will.
15 Ya zama sa'adda mala'iku suka bar su zuwa cikin sama, sai makiyayan su ka ce wa junansu, “Bari mu je Baitalami mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya nuna mana.”
And it came to pass, after the angels departed from them into heaven, the shepherds said one to another: Let us go over to Bethlehem, and let us see this word that is come to pass, which the Lord hath shewed to us.
16 Su ka yi hamzari suka tafi can sun iske Maryamu da Yusufu, suka ga jaririn kuwa kwance a cikin kwamin dabbobin.
And they came with haste; and they found Mary and Joseph, and the infant lying in the manger.
17 Bayan da sun ga wannan, suka gaya wa mutane abinda aka gaya masu game da wannan yaro.
And seeing, they understood of the word that had been spoken to them concerning this child.
18 Dukan wadanda su ka ji, su ka yi mamaki kwarai game da abin da makiyayan su ka gaya masu.
And all that heard, wondered; and at those things that were told them by the shepherds.
19 Amma ita Maryamu ta ci gaba da tunani akan wadanan abubuwa da ta ji, tana tunani mai zurfi a cikin zuciyarta.
But Mary kept all these words, pondering them in her heart.
20 Makiyayan suka koma suna ta daukaka da yabon Allah domin dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, dadai da yadda aka gaya masu.
And the shepherds returned, glorifying and praising God, for all the things they had heard and seen, as it was told unto them.
21 Da ya kai kwana takwas, lokacin da za a yi wa jaririn kaciya, sai aka rada masa suna Yesu, sunan da mala'ikan ya bashi kamin a yi cikinsa.
And after eight days were accomplished, that the child should be circumcised, his name was called JESUS, which was called by the angel, before he was conceived in the womb.
22 Da kwanakin tsarkakewar su ya wuce bisa ga shari'ar Musa, Yusufu da Maryamu suka kawo shi cikin haikali a Urushalima dominsu mika shi ga Ubangiji.
And after the days of her purification, according to the law of Moses, were accomplished, they carried him to Jerusalem, to present him to the Lord:
23 Kamar yadda aka rubuta a dokokin Ubangiji, “Za a kira duk da na fari kebabbe ga Ubangiji.”
As it is written in the law of the Lord: Every male opening the womb shall be called holy to the Lord:
24 Suka kuma zo su mika hadaya bisa ga yadda aka fada a shari'ar Ubangiji, “Kurciyoyi biyu ko 'yan tantabaru biyu.”
And to offer a sacrifice, according as it is written in the law of the Lord, a pair of turtledoves, or two young pigeons:
25 Ga shi akwai wani mutum a Ushalima mai suna Siman. Wannan mutum adali ne kuma mai ibada. Yana jiran mai ta'aziyar Isra'ila, kuma Ruhu Mai-sarki na bisansa.
And behold there was a man in Jerusalem named Simeon, and this man was just and devout, waiting for the consolation of Israel; and the Holy Ghost was in him.
26 An kuma bayyana masa ta wurin Ruhu Mai-tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kristi na Ubangiji.
And he had received an answer from the Holy Ghost, that he should not see death, before he had seen the Christ of the Lord.
27 Wata rana Siman ya zo cikin haikali ta wurin jagorar Ruhu Mai-tsarki. Da iyayen suka kawo yaron ciki, wato Yesu, domin su cika sharudan da shari'ar ke bukata,
And he came by the Spirit into the temple. And when his parents brought in the child Jesus, to do for him according to the custom of the law,
28 sai Siman ya karbe shi cikin hanuwansa, ya yabi Allah ya ce,
He also took him into his arms, and blessed God, and said:
29 “Yanzu bari bawanka ya tafi da salama, Ubangiji, bisa ga kalmarka.
Now thou dost dismiss thy servant, O Lord, according to thy word in peace;
30 Domin idanuna sun ga cetonka,
Because my eyes have seen thy salvation,
31 wanda ka shirya a gaban dukan mutane:
Which thou hast prepared before the face of all peoples:
32 Haske ne na wahayi ga al'ummai, kuma daukakar mutanenka Isra'ila.”
A light to the revelation of the Gentiles, and the glory of thy people Israel.
33 Mahaifin yaron da Mahaifiyarsa, sun yi mamaki kwarai domin abubuwan da aka fada akansa.
And his father and mother were wondering at those things which were spoken concerning him.
34 Sai Siman ya albarkace su ya ce wa uwatasa Maryamu, “Ki ji da kyau, wannan yaro zai zama sanadiyar faduwa da tashin mutane dayawa a Isra'ila, kuma alama wadda ake kushen ta.
And Simeon blessed them, and said to Mary his mother: Behold this child is set for the fall, and for the resurrection of many in Israel, and for a sign which shall be contradicted;
35 Kuma takobi zai tsaga zuciyar ki yadda tunanin mutane za ya bayyana.”
And thy own soul a sword shall pierce, that, out of many hearts, thoughts may be revealed.
36 Wata annabiya mai suna Annatu ta na nan wurin. Ita diyar Fanuyila ce daga kabilar Ashiru. Ta riga ta manyanta a shekaru sosai. Ta kasance da maigidanta shekaru bakwai bayan auren ta,
And there was one Anna, a prophetess, the daughter of Phanuel, of the tribe of Aser; she was far advanced in years, and had lived with her husband seven years from her virginity.
37 sannan ta yi zama gwambranci na shekaru tamanin da hudu. Ba ta taba barin haikali ba, tana ci gaba da yi wa Ubangiji sujada, dare da rana.
And she was a widow until fourscore and four years; who departed not from the temple, by fastings and prayers serving night and day.
38 A dadai lokacin nan, ta hau zuwa wurinsu ta fara yi wa Allah godiya. Ta gaya wa dukan wadanda ke jiran fansar Urushalima.
Now she, at the same hour, coming in, confessed to the Lord; and spoke of him to all that looked for the redemption of Israel.
39 Da su ka gama komai da aka bukace su suyi bisa ga tafarkin shari'ar Ubangiji, sai suka koma Galili, zuwa birninsu, Nazarat.
And after they had performed all things according to the law of the Lord, they returned into Galilee, to their city Nazareth.
40 Yaron kuma ya yi girma ya zama da karfi, yana karuwa da hikima, alherin Ubangiji kuma yana kansa.
And the child grew, and waxed strong, full of wisdom; and the grace of God was in him.
41 Iyayensa sukan tafi Urushalima kowacce shekara domin idin ketarewa.
And his parents went every year to Jerusalem, at the solemn day of the pasch,
42 Da yana shekara goma sha biyu, suka sake haurawa daidai lokacin idin a al'adance.
And when he was twelve years old, they going up into Jerusalem, according to the custom of the feast,
43 Bayan da sun cika dukan kwanakin idin, sun fara dawowa gida. Amma dan yaron Yesu ya jinkirta ya zauna a Urushalima, kuma iyayensa basu sani ba.
And having fulfilled the days, when they returned, the child Jesus remained in Jerusalem; and his parents knew it not.
44 Suna tsammani yana tare da sauran mutane da suke tafiya tare, sai suka yi tafiya na kwana daya. Suka fara neman sa a cikin danginsu da abokansu.
And thinking that he was in the company, they came a day’s journey, and sought him among their kinsfolks and acquaintance.
45 Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima suna cigiyar sa a can.
And not finding him, they returned into Jerusalem, seeking him.
46 Ya zama bayan kwanaki uku, su ka same shi a cikin haikali, yana zama a tsakiyar malamai, yana sauraron su yana kuma yi masu tambayoyi.
And it came to pass, that, after three days, they found him in the temple, sitting in the midst of the doctors, hearing them, and asking them questions.
47 Dukan wadanda suka ji shi suna ta mamakin fahimtar sa da amsoshin sa.
And all that heard him were astonished at his wisdom and his answers.
48 Da suka gan shi, suka yi mamaki kwarai. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Da na, don me ka yi mana haka? Ka ji, mahaifinka da ni muna ta neman ka rai a bace.”
And seeing him, they wondered. And his mother said to him: Son, why hast thou done so to us? behold thy father and I have sought thee sorrowing.
49 Ya ce masu, “Don me kuke nema na? Ba ku sani cewa dole in kasance a gidan Ubana ba?”
And he said to them: How is it that you sought me? did you not know, that I must be about my father’s business?
50 Amma ba su gane abin da yake nufi da kalmomin nan ba.
And they understood not the word that he spoke unto them.
51 Sa'annan ya koma gida tare da su zuwa Nazarat yana kuma masu biyayya. Mahaifiayarsa kuma ta ajiye dukan wadannan abubuwa a zuciyarta tana yin tunani akansu.
And he went down with them, and came to Nazareth, and was subject to them. And his mother kept all these words in her heart.
52 Amma Yesu ya ci gaba da hikima da girma, ya kuma karu da tagomashi wurin Allah da mutane.
And Jesus advanced in wisdom, and age, and grace with God and men.

< Luka 2 >