< Luka 18 >

1 Ya kuma ba su wani misali cewa ya kamata kullum su yi addu'a kada kuma su karaya,
And he put forth a similitude vnto the signifyinge that men ought alwayes to praye and not to be wery
2 yace, “A wani gari an yi wani alkali mara tsoron Allah, kuma baya ganin darajan mutane.
sayinge: Ther was a Iudge in a certayne cite which feared not god nether regarded man.
3 Akwai wata mace gwauruwa a wannan garin, wadda ta rika zuwa wurinsa, tana ce masa, 'Ka taimake ni yanda zan sami adalci a kan abokin gaba na.'
And ther was a certayne wedowe in the same cite which came vnto him sayinge: avenge me of myne adversary.
4 An dade bai so ya taimaka mata, amma daga baya sai ya ce a ransa, 'ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma darajanta mutane,
And he wolde not for a whyle. But afterwarde he sayd vnto him selfe: though I feare not God nor care for man
5 duk da haka saboda gwauruwar nan ta dame ni, zan taimake ta domin ta sami adalci, yadda ba za ta gajiyar da ni da zuwanta wurina ba.'”
yet because this wedowe troubleth me I will avenge her lest at the laste she come and hagge on me.
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alkalin nan marar gaskiya ya fada.
And the lorde sayd: heare what the vnrightewes Iudge sayeth.
7 A yanzu Allah ba zai biya wa zababbunsa da suke yi masa kuka dare da rana hakkinsu ba? Zai yi jinkiri a wajen taimakonsu ne?
And shall not god avenge his electe which crye daye and nyght vnto him ye though he differre them?
8 Ina gaya maku, zai biya masu hakkin su da wuri. Amma sa'adda Dan Mutum ya zo, zai tarar da bangaskiya a duniya?”
I tell you he will avenge them and that quickly. Neverthelesse when the sonne of man cometh suppose ye that he shall fynde faithe on the erthe.
9 Ya sake ba da misalin nan ga wadansu masu amincewa da kansu, wai su masu adalci ne, har suna raina sauran mutane,
And he put forthe this similitude vnto certayne which trusted in the selves yt they were perfecte and despysed other.
10 “Wadansu mutane biyu suka shiga haikali domin yin addu'a - daya Bafarise, dayan kuma mai karbar haraji ne.
Two men went vp into ye teple to praye: ye one a pharise and the other a publican.
11 Sai Bafarisen ya mike, ya yi addu'a a kan wadannan abubuwa game da kansa, 'Allah, na gode maka, da cewa ni ba kamar sauran mutane dake mazambata ba, ko marasa adalci, ko mazinata, ko kamar wannan mai karbar harajin.
The pharise stode and prayed thus wt him selfe. God I thanke the yt I am not as other men are extorsioners vniuste advoutrers or as this publican.
12 Duk mako ina azumi sau biyu. Nakan bayar da zakkar dukan abin da na samu.'
I fast twyse in ye weke. I geve tythe of all that I possesse.
13 Amma mai karbar harajin kuwa yana tsaye daga can nesa, bai yarda ya daga kai sama ba, sai dai yana bugun kirjin sa, yana cewa, 'Allah, ka yi mini jinkai, ni mai zunubi.'
And the publican stode afarre of and wolde not lyfte vp his eyes to heven but smote his brest sayinge: God be mercyfull to me a synner.
14 Ina gaya maku, wannan mutum ya koma gidansa baratacce, ba kamar dayan ba, domin dukan wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, amma duk wanda kaskantar da kansa kuwa daukaka shi za a yi.”
I tell you: this ma departed hoe to his housse iustified moore then the other. For every man that exalteth him selfe shalbe brought low: And he yt hubleth him selfe shalbe exalted
15 Sai mutanen suka kawo masa jariransu, domin ya taba su, da almajiransa suka ga haka, sai suka kwabe su.
They brought vnto him also babes yt he shuld touche the. When his disciples sawe that they rebuked the.
16 Amma Yesu ya kira su wurinsa, ya ce, “Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai mulkin Allah na irin su ne.
But Iesus called the vnto him and sayde: Suffre chyldren to come vnto me and forbidde the not. For of soche is ye kyngdome of God.
17 Gaskiya ina gaya maku, duk wanda bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, lallai ba zai shige shi ba.”
Verely I saye vnto you: whosoever receaveth not the kyngdome of God as a chylde: he shall not enter therin.
18 Wani shugaban jama'a ya tambaye shi ya ce “Malam managarci, me zan yi in gaji rai Madawwami?” (aiōnios g166)
And a certayne ruler axed him sayinge: Good Master: what ought I to do to obtayne eternall lyfe? (aiōnios g166)
19 Yesu ya ce masa, “Don me ka kira ni managarci? Babu wani managarci sai Allah kadai.
Iesus sayd vnto him: Why callest thou me good? No man is good save God only.
20 Ka dai san dokokin - kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar karya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.”
Thou knowest ye comaundmentes: Thou shalt not commit advoutry: thou shalt not kyll: thou shalt not steale: thou shalt not beare false witnes: Honoure thy father and thy mother.
21 Sai shugaban ya ce, “Dukan wadannan abubuwa na kiyaye su tun a kuruciya ta.”
And he sayde: all these have I kept from my youthe.
22 Da Yesu ya ji haka, ya ce masa, “Abu daya ne kadai ya rage maka. Dole ne ka sayar da dukan mallakarka, ka rarraba wa gajiyayyu, za ka kuma sami wadata a sama - sa'annan ka zo ka biyoni.”
When Iesus hearde that he sayde vnto him: Yet lackest thou one thinge. Sell all that thou hast and distribute it vnto the poore and thou shalt have treasure in heven and come and folowe me.
23 Amma da mai arzikin ya ji wadannan abubuwa, sai yayi bakin ciki kwarai, don shi mai arziki ne sosai.
When he heard that he was hevy: for he was very ryche.
24 Yesu kuwa, da ya ga ransa ya baci, sai ya ce, “Yana da wuya masu dukiya su shiga mulkin Allah!
When Iesus sawe him morne he sayde: with what difficulte shall they that have ryches enter into the kyngdome of God:
25 Zai zama da sauki rakumi ya shiga kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
it is easyer for a camell to goo thorow a nedles eye then for a ryche man to enter into the kyngdome of God.
26 Wadanda suka ji wannan magana suka ce, “Idan hakane wa zai sami ceto kenan?”
Then sayde they that hearde that: And who shall then be saved?
27 Yesu ya amsa, “Abin da ya fi karfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah.”
And he sayde: Thinges which are vnpossible with men are possible with God.
28 Sai Bitrus ya ce, “To, ga shi mun bar mallakarmu, mun bi ka.”
Then Peter sayde: Loo we have lefte all and have folowed the.
29 Yesu ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda mulkin Allah,
And he sayde vnto them: Verely I saye vnto you ther is noo man that leaveth housse other father and mother other brethren or wyfe or chyldren for the kyngdome of Goddes sake
30 sa'annan ya kasa samun ninkin ba ninkin a duniyan nan, da rai na har abada a duniya mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
which same shall not receave moche moore in this worlde: and in the worlde to come lyfe everlastinge. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Bayan da ya tara su goma sha biyun nan, ya ce masu, “Ga shi, muna tafiya zuwa Urushalima, duk abubuwan da aka rubuta game da Dan Mutum ta hannun annabawa zasu tabbata.
He toke vnto him twelve and sayde vnto them. Beholde we go vp to Ierusalem and all shalbe fulfilled that are written by ye Prophetes of the sonne of man.
32 Gama za a bashe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa miyau.
He shalbe delivered vnto the gentils and shalbe mocked and shalbe despytfully entreated and shalbe spetted on:
33 Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma zai tashi.”
and when they have scourged him they will put him to deeth and the thyrde daye he shall aryse agayne.
34 Amma ba su fahimci ko daya daga cikin wadannan abubuwa ba, domin zancen nan a boye yake daga garesu, ba su ma gane abin da aka fada ba.
But they vnderstode none of these thinges. And this sayinge was hid fro them. And they perceaved not the thinges which were spoken.
35 Da ya kusato Yariko, ga wani makaho zaune a gefen hanya, yana bara,
And it came to passe as he was come nye vnto Hierico a certayne blynde man sate by the waye syde begginge.
36 da ya ji taro na wucewa, sai ya tambaya ko menene.
And when he hearde the people passe by he axed what it meant.
37 Suka ce masa Yesu Banazarat ne yake wucewa.
And they sayde vnto him yt Iesus of Nazareth passed by.
38 Sai makahon ya ta da murya mai karfi, ya ce, “Yesu, Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
And he cryed sayinge: Iesus ye sonne of David have thou mercy on me.
39 Sai wadanda suke gaba suka kwabe shi, suna gaya masa ya yi shiru. Amma ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, “Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
And they which went before rebuked him that he shuld holde his peace. But he cryed so moche the moare thou sonne of David have mercy on me.
40 Sai Yesu ya tsaya, ya umarta a kawo shi wurinsa. Da makahon ya zo kusa, sai Yesu ya tambaye shi,
And Iesus stode styll and commaunded him to be brought vnto him. And when he was come neare he axed him
41 “Me kake so in yi maka?” Ya ce, “Ubangiji, ina so in samu gani.”
sayinge: What wilt thou that I do vnto the? And he sayde: Lorde yt I maye receave my sight.
42 Yesu ya ce masa, “Karbi ganin gari, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
Iesus sayde vnto him: receave thy sight: thy faith hath saved the.
43 Nan take ya samu gani, ya bi Yesu, yana daukaka Allah. Ganin haka, sai duk jama'a suka yabi Allah.
And immediatly he sawe and folowed him praysinge God. And all the people when they sawe it gave laude to God.

< Luka 18 >