< Markus 1 >

1 Wannan itace farkon bisharar Yesu Almasihu, Dan Allah.
The beginnynge of the Gospell of Iesu Christ the sonne of God
2 kamar yadda aka rubuta cikin littafin annabi Ishaya. Duba, ina aika manzona, a gabanka, wanda zai shirya maka hanya.
as yt is wrytten in the Prophetes: beholde I sende my messenger before thy face which shall prepared thy waye before ye.
3 Akwai murya mai kira a jeji, tana cewa ka shirya hanyar Ubangiji. ka daidaita ta.
The voyce of a cryer in the wildernes: prepare ye the waye of the Lorde make his paches streyght.
4 Yahaya ya zo, yana baptisma acikin jeji yana wa'azin tuba, domin gafarar zunubai.
Iohn dyd baptise in the wyldernes and preche the baptyme of repentauce for the remission of synnes.
5 Dukan kasar Yahudiya da mutanen Urshalima suka zo wurin sa, a ka kuma yi masu baptisma a kogin urdun. suna furta zunubansu.
And all the londe of Iurie and they of Ierusalem went out vnto him and were all baptised of him in the ryver Iordan confessynge their synnes.
6 Yahaya yana saye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma da damara ta fata a kugunsa, abincinsa fara ce da zuma.
Iohn was clothed with cammylles heer and with a gerdyll of a skyn a bout hys loynes. And he dyd eate locustes and wylde hony
7 Yana wa'azi, ya ce “akwai mai zuwa a bayana wanda ya ke da iko fiye da ni. wanda ko maballin takalminsa ban isa in kwance ba.
and preached sayinge: a stronger then I commeth after me whose shue latchet I am not worthy to stoupe doune and vnlose.
8 Ni ina yi maku baptisma da ruwa, amma mai zuwa a bayana zai yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki''.
I have baptised you with water: but he shall baptise you with the holy goost.
9 Sai ya kasance a kwanakin nan Yesu ya zo daga Nazarat ta Galili, sai Yahaya ya yi masa baptisma a kogin urdun.
And yt came to passe in those dayes that Iesus cam from Nazareth a cyte of Galile: and was baptised of Iohn in Iordan.
10 Sa'adda Yesu ya fito daga ruwan, sai sama ta bude, sai Ruhu ya sauko a bisansa da kamanin kurciya.
And assone as he was come out of the water Iohn sawe heaven open and the holy goost descendinge vpon him lyke a dove.
11 Sai wata murya ta zo daga sama, tana cewa, “Kai kaunataccen Dana ne. zuciyata ta na murna da kai kwarai''.
And ther came a voyce from heaven: Thou arte my dere sonne in whom I delyte.
12 Sai Ruhu ya iza shi zuwa jeji.
And immediatly the sprete drave him into wildernes:
13 Yana a jeji kwana arba'in, Shaidan yana jarabtar sa. Yana cikin jeji da dabobi, sai malaiku su ka yi masa hidima.
and he was there in the wildernes xl dayes and was tempted of Satan and was with wilde beestes. And the aungels ministred vnto him.
14 Bayan da aka kama Yahaya, Yesu ya shiga kasar Galili yana wa'azin bisharar Allah.
After Iohn was taken Iesus came in to Galile preachinge the gospell of the kyngdome of God
15 Yana cewa, “Lokaci ya yi, gama mulkin Allah ya kusato. Ku tuba ku bada gaskiya ga bishara”.
and sayinge: the tyme is come and the kyngdome of God is at honde repent and beleve the gospell.
16 Sa'adda ya ke wucewa a gefen takun Galili, sai ya ga Saminu da Andarawus, dan'uwansa suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
As he walked by the see of Galile he sawe Simon and Andrew his brother castinge nettes into ye see for they were fysshers.
17 Yesu ya ce masu ku zo, ku biyo ni, ni kuwa sai in maisheku masuntan mutane”.
And Iesus sayde vnto them: folowe me and I will make you fisshers of men.
18 Nan da nan suka bar tarun su, suka bi shi.
And strayght waye they forsoke their nettes and folowed him.
19 Sa'adda Yesu ya yi tafiya kadan, sai ya ga Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan'uwansa; suna gyaran tarunsu a jirgin ruwa.
And when he had gone a lytell further thence he sawe Iames the sonne of zebede and Ihon his brother even as they were in the shyppe mendinge their nettes.
20 Sai ya kira su, su kuwa suka bar mahaifinsu Zabadi a jirgin ruwan da ma'aikatansu, sai su ka bi shi.
And anone he called them. And they leeft their father zebede in the shippe with his hyred servauntes and went their waye after him.
21 Da su ka shigo cikin kafanahum, a ranar asabar, Yesu ya shiga majami'a ya koya masu.
And they entred into Capernau: and streight waye on ye Saboth dayes he entred in to ye synagoge and taught.
22 Su ka yi mamakin koyarwarsa, domin ya na koya masu da iko ba kamar marubuta ba.
And they merveled at his learninge. For he taught them as one that had power with him and not as the Scribes.
23 A nan cikin majami'a akwai wani mutum mai kazamin ruhu, sai ya yi ihu da karfi.
And there was in their synagoge a ma vexed wt an vnclene spirite yt cried
24 Yana cewa Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo ne domin ka halakar da mu? Na san wanene kai. Kai ne Mai Tsarki na Allah”.
sayinge: let be: what have we to do with the thou Iesus of Nazareth? Arte thou come to destroye vs? I knowe the what thou arte eue that holy of god.
25 Sai Yesu ya tsauta wa kazamin ruhun ya ce, “Ka yi shiru ka fita daga cikinsa”.
And Iesus rebuked him sayinge: hoolde thy peace and come out of him.
26 Bayan da kazamin ruhun ya buga shi kasa, sai kazamin ruhun ya yi ihu sa'annan ya fita daga jikinsa.
And ye vnclene spirite tare him and cryed with a loude voyce and came out of him.
27 Sai dukan mutanen su ka yi mamaki kwarai, suna tambayar junansu menene wannan? wace sabuwar koyarwa ce da iko haka? har yana umartar kazaman ruhohi suna kuwa yi masa biyayya!”
And they were all amased in so moche that they demaunded one of another amoge them selves saying: what thinge is this? what newe doctryne is this? For he comaundeth the foule spirites with power and they obeye him.
28 Nan da nan labarinsa ya bazu ko'ina a dukkan kewayen kasar Galili.
And immediatly his fame spreed abroade throughoute all the region borderinge on Galile.
29 Bayan da suka bar majami'a, sai su ka shiga gidan Saminu da Andarawus, suna kuma tare da Yakubu da Yahaya.
And forth with as sone as they were come out of the synagoge they entred into ye housse of Symon and Andrew with Iames and Ihon.
30 Surikar Saminu tana kwance ba lafiya tana fama da zazzabi. Sai suka gaya wa Yesu game da ita.
And Symons mother in lawe lay sicke of a fever. And anone they tolde him of her.
31 Sai ya zo, ya kama hannunta, ya daga ta, sai zazzabin ya sake ta, ta fara yi masu hidima.
And he came and toke her by the honde and lifte her vp: and the fever forsoke hir by and by: and she ministred vnto them.
32 Da yamman nan, bayan da rana ta fadi, sai su ka kawo masa dukan marasa lafiya da masu fama da aljanu.
And at even when the sunne was downe they brought to him all that were diseased and them that were possessed with devyls.
33 Dukan mutanen garin su ka taru a bakin kofa.
And all the cite gaddred to gedder at the dore
34 ya warkar da masu ciwo da yawa da masu chututtuka iri-iri, ya kuma fitar da bakaken aljanu, amma bai yarda aljanun su yi magana ba domin sun san shi.
and he healed many yt were sicke of divers deseases. And he cast out many devyls and suffred not ye devyls to speake because they knewe him.
35 Ya tashi da sassafe, tun da sauran dare, ya tafi wurin da ba kowa, a can ya yi add'ua.
And in the morninge very erly Iesus arose and went out into a solitary place and there prayed.
36 Saminu da wandanda suke tare da shi suka neme shi.
And Simon and they that were with him folowed after him.
37 Suka sa me shi, sai su ka ce masa, “kowa yana nemanka”.
And when they had founde him they sayde vnto him: all men seke for the.
38 Ya ce, bari mu tafi wani wuri, zuwa wadansu garuruwan da ke kewaye, Saboda in yi wa'azi a can kuma. Wannan shi yasa na zo nan''.
And he sayd vnto them: let vs go into the next tounes that I maye preache there also: for truly I cam out for that purpose.
39 Ya tafi dukan kasar Galili, yana wa'azi a majimi'un su yana kuma fitar da aljanu.
And he preached in their synagoges throughout all Galile and cast the devyls out.
40 Wani kuturu ya zo wurinsa. Yana rokonsa, ya durkusa. Ya ce masa, “in ka yarda kana iya warkar da ni.
And there came a leper to him besechinge him and kneled doune vnto him and sayde to him: yf thou wilt thou canest make me clene.
41 Sai ya yi juyayi, Yesu ya mi ka hannun sa ya ta ba shi ya na ce masa “Na yarda. Ka sarkaka”.
And Iesus had copassion on him and put forth his honde touched him and sayde to him: I will be thou clene.
42 Nan da nan kuturtar ta barshi, ya kuma sa mu tsarkakewa.
And assone as he had spoke immediatly ye leprosy departed fro him and was clensed.
43 Yesu ya yi masa gargadi sosai, ya salame shi.
And he charged him and sent him awaye forthwith
44 Ya ce masa “ka tabbata fa kada ka gayawa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, sai ka je ka yi hadaya domin tsarkakewa kamar yadda Musa ya umurta, domin shaida.
and sayd vnto him: Se thou saye no thinge to any man: but get the hence and shewe thy silfe to ye preste and offer for thy clensinge those thinges which Moses comaunded for a testimoniall vnto them.
45 Amma da ya fita sai ya fara gaya wa kowa, ya baza maganar a ko'ina, har Yesu bai iya tafiya a sake a garin ba. Ya tafi ya tsaya a wuraren da ba kowa, mutane kuwa su ka zo wurinsa daga ko'ina.
But he (assone as he was departed) beganne to tell many thinges and to publyshe the dede: in so moche that Iesus coulde no more opely entre in to the cite but was with out in desert places. And they came to him fro every quarter.

< Markus 1 >