< Yohanna 1 >

1 A cikin farko akwai Kalma, Kalmar kuma tana tare da Allah, wannan Kalma kuwa Allah ne.
Au commencement était la Parole; la Parole était avec Dieu, et la Parole était dieu.
2 Shi kuwa tare da Allah yake tun farko.
Elle était au commencement avec Dieu.
3 Dukan abu ta wurinsa aka yi su, babu abin da aka halitta sai ta wurin sa.
Toutes choses ont été faites par elle, et rien de ce qui a été fait, n'a été fait sans elle.
4 A cikinsa rai ya ke, kuma wannan rai ya zama haske ga dukan mutane.
En elle était la vie, et cette vie était la lumière des hommes:
5 Hasken ya haskaka a cikin duhu, kuma duhun bai rinjaye shi ba.
la lumière brille dans les ténèbres, mais les ténèbres ne l'ont point reçue.
6 Akwai wani mutum wanda Allah ya aiko, mai suna Yahaya.
Un homme parut; il était envoyé de Dieu, son nom était Jean.
7 Ya zo a matsayin mai ba da shaida game da hasken, domin kowa ya ba da gaskiya ta wurinsa.
Il vint pour un témoignage, pour rendre témoignage à la Lumière, afin que tous crussent par lui:
8 Ba Yahaya ne hasken ba, amma ya zo ne domin ya shaida hasken.
il n'était pas la Lumière, mais il devait rendre témoignage à la Lumière.
9 Wannan shine haske na gaskiya mai ba da haske ga dukan mutane, da ke zuwa cikin duniya.
La véritable Lumière, qui éclaire tout homme, était entrée dans le monde;
10 Yana cikin duniya, kuma an halicci duniya ta wurinsa, amma duniya bata san shi ba.
elle était dans le monde, et le monde a été fait par elle, mais le monde ne l'a point connue.
11 Ya zo wurin nasa, amma nasa basu karbe shi ba.
Elle est venue chez les siens, et les siens ne l'ont point reçue;
12 Amma duk iyakar wadanda suka karbe shi, suka kuma ba da gaskiya ga sunansa, ya ba su 'yanci su zama 'ya'yan Allah.
mais à tous ceux qui l'ont reçue, à tous ceux qui croient en son nom, elle a donné la prérogative d'être enfants de Dieu:
13 Wadanda aka haife su ba ta wurin jini ba, ko ta wurin nufin jiki, ko nufin mutum, amma ta wurin Allah.
enfants, qui ne sont pas nés du sang, ni de la volonté de la chair, ni de la volonté de l'homme, mais qui sont nés de Dieu.
14 Kalmar kuma ya zama jiki ya zauna cikin mu. Mun ga daukakarsa, daukaka irin ta makadaici shi kadai wanda ya zo daga Uban, cike da alheri da gaskiya.
Et la Parole a été faite chair; elle a habité au milieu de nous pleine de grâce et de vérité, et nous avons contemplé sa gloire, une gloire comme celle d'un fils unique envoyé par son père.
15 Yahaya ya yi shaida akansa yana kira da karfi, cewa, “Wannan shine wanda na yi magana a kansa cewa, 'Shi wanda ke zuwa bayana, ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'”
Jean lui rend témoignage, quand il dit à haute voix: «Voici celui dont je disais: Celui qui vient après moi. a pris le pas devant moi, parce qu'il est plus grand que moi.»
16 Domin daga cikarsa ne muka karbi alheri akan alheri.
C'est de sa plénitude que nous avons tous reçu grâce sur grâce;
17 Gama shari'a ta zo daga wurin Musa. Alheri da gaskiya sun zo ta wurin Yesu Almasihu.
car la Loi a été donnée par Moïse; mais la Grâce et la Vérité sont venues par Jésus-Christ.
18 Babu lokacin da wani ya taba ganin Allah, shi wanda shi kadai ne Allah, wanda ke jingine da kirjin Uba, shi ya bayyana shi.
Personne n'a jamais vu Dieu; le Fils unique, qui est dans le sein du Père, est celui qui l'a révélé.
19 Wannan ita ce shaidar Yahaya sa'adda Yahudawa suka aika da Firistoci da Lawiyawa zuwa gareshi don su tambaye shi, “Wanene kai?”
Voici le témoignage que rendit Jean, lorsque les Juifs envoyèrent de Jérusalem des sacrificateurs et des lévites pour lui adresser cette question: «Qui es-tu?»
20 Ya fada dalla dalla, kuma bai musunta ba, yana amsa masu cewa, “ba nine Almasihu ba.”
Il le déclara, et ne le nia point; il déclara qu'il n'était pas le Messie.
21 Sai suka tambaye shi, “To kai wanene? Kai Iliya ne?” Yace, “Ba ni ba ne.” Suka ce, “Kai ne anabin?” Ya amsa, “A'a”.
— «Quoi donc! Es-tu Élie?» lui demandèrent-ils; et il dit: «Je ne le suis point.» - «Es-tu le Prophète?» et il répondit: «Non.»
22 Sai suka ce masa, “Kai wanene, domin mu bada amsa ga wadanda suka aiko mu? Me kake fadi game da kanka?”
Ils lui dirent donc: «Qui es-tu? afin que nous rendions réponse à ceux qui nous ont envoyés. Que dis-tu que tu es?»
23 Yace, “Ni murya ne, da ke kira cikin jeji, 'Ku daidaita hanyar Ubangiji,' kamar yadda annabi Ishaya ya fada.”
— «Moi, dit-il, je suis «une voix qui crie au désert: Redressez le chemin du Seigneur, » comme a dit le prophète Ésaïe.
24 Su wadanda aka aika daga wurin Farisawa suke. Sai suka tambaye shi cewa,
Ceux qu'on avait envoyés étaient des pharisiens.
25 “To don me kake baftisma idan kai ba Almasihu bane, ko Iliya, ko annabin?”.
Ils insistèrent, et lui dirent: «Pourquoi donc baptises-tu, si tu n'es pas le Messie, ni même Elie ou le Prophète?»
26 Yahaya ya amsa masu, cewa, “Ina baftisma ne da ruwa. Amma a cikinku akwai wani tsaye wanda ba ku sani ba,
Jean leur répondit: «Pour moi, je baptise d'eau, mais il y a au milieu de vous quelqu'un que vous ne connaissez pas:
27 shi wanda ke zuwa bayana, wanda ko igiyar takalminsa ban isa in kwance ba.”
c'est celui qui vient après moi; je ne suis pas digne de délier la courroie de ses sandales.»
28 Wadannan abubuwa sun faru ne a Baitanya, a dayan ketaren Urdun, a wurin da Yahaya ke Baftisma.
Ces choses se passèrent à Béthanie, au delà du Jourdain, où Jean baptisait.
29 Washegari, Yahaya ya ga Yesu yana zuwa wurinsa ya ce, “Duba, ga Dan Ragon Allah wanda ke dauke zunubin duniya!
Le lendemain, Jean vit Jésus qui venait vers lui, et il dit: «Voici l'agneau de Dieu qui ôte le péché du monde.»
30 Wannan shine wanda na fada maku cewa, “Shi wanda ke zuwa bayana ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'
C'est de lui que j'ai dit: Il vient après moi un homme qui a pris le pas devant moi, parce qu'il est plus grand que moi.
31 Ban san shi ba, amma saboda a bayyana shi ga Isra'ila ne nazo ina baftisma da ruwa. “
Je ne le connaissais pas; mais je suis venu baptiser d'eau, afin qu'il fût manifesté à Israël»
32 Yahaya ya shaida, cewa, “Na ga Ruhu yana saukowa kamar kurciya daga sama, ya kuma zauna a kansa.
et Jean avait rendu ce témoignage: «J'ai vu l'Esprit descendre du ciel comme une colombe, et demeurer sur lui.»
33 Ban gane shi ba, amma shi wanda ya aiko ni in yi baftisma cikin ruwa ya fada mani cewa, 'duk wanda ka ga Ruhun ya sauka kuma ya zauna a kansa, shine wanda ke yin baftisma cikin Ruhu mai tsarki.'
Je ne le connaissais pas; mais celui-là même qui m'a envoyé baptiser d'eau m'a dit: «Celui sur qui tu verras l'Esprit descendre et demeurer, c'est lui qui baptise d'esprit saint.»
34 Na gani, na kuma shaida cewa wannan shine Dan Allah.”
Je l'ai vu, et j'ai rendu témoignage que c'est lui qui est le Fils de Dieu.»
35 Kuma, washegari, da Yahaya na tsaye da biyu daga cikin almajiransa,
Le lendemain, Jean se trouvait là de nouveau, avec deux de ses disciples;
36 suka ga Yesu na wucewa, sai Yahaya ya ce, “Duba, ga Dan rago na Allah!”
et, ayant considéré Jésus qui passait, il dit: «Voilà l'agneau de Dieu.»
37 Sai almajiransa biyu suka ji ya fadi haka, suka kuwa bi Yesu.
Ces deux disciples l'ayant entendu parler de la sorte, suivirent Jésus.
38 Da Yesu ya waiwaya ya gan su suna bin sa, sai ya ce masu, “Me kuke so?” Suka amsa, “Rabbi (wato 'Mallam'), ina kake da zama?”
Jésus s'étant retourné, et voyant qu'ils le suivaient, leur dit. «Que cherchez- vous?» Ils lui dirent: «Rabbi, »(ce qui signifie Maître) «où demeures-tu?»
39 Yace masu, “Zo ku gani.” Sai suka zo suka ga inda yake zama; suka zauna da shi ranan nan, gama wajen sa'a ta goma ne.
— «Venez, leur dit-il, et vous verrez. Ils allèrent, et ils virent où il demeurait, et ils restèrent auprès de lui ce jour-là. C'était environ la dixième heure du jour.
40 Daya daga cikin wadanda suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu shine Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus.
André, frère de Simon-Pierre, était l'un des deux disciples qui avaient entendu la parole de Jean, et qui avaient suivi Jésus.
41 Ya fara neman dan'uwansa Siman yace masa, “Mun sami Almasihu” (wanda ake kira 'Kristi').
Il rencontra, le premier, son frère Simon, et il lui dit: «Nous avons trouvé le Messie» (ce qui signifie Christ);
42 Ya kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi yace, “Kai ne Siman dan Yahaya. Za a kira ka Kefas,” (ma'ana, 'Bitrus').
et il le mena vers Jésus. Celui-ci, l'ayant considéré, lui dit: «Tu es Simon, fils de Jona; on t'appellera Céphas» (ce qui signifie Pierre).
43 Washegari, da Yesu yana shirin tafiya zuwa Galili, sai ya sami Filibus, ya ce masa, “ka biyo ni.”
Le lendemain, Jésus résolut de partir pour la Galilée. Il rencontra Philippe, et lui dit: «Suis-moi.»
44 Filibus dan asalin Baitsaida ne, garin Andarawus da Bitrus.
Philippe était de la ville de Bethsaïde, d'où étaient aussi André et Pierre.
45 Filibus ya sami Natana'ilu yace masa, “Mun same shi, shi wanda Musa ya rubuta shi a cikin attaura, da annabawa: Yesu Dan Yusufu, Ba-Nazarat.”
Philippe rencontra Nathanaël, et lui dit: «Nous avons trouvé celui dont Moïse a parlé dans la Loi, et que les prophètes ont annoncé; c'est Jésus, fils de Joseph, de Nazareth.»
46 Natana'ilu ya ce masa, “za a iya samun wani abu nagari a Nazarat?” Filibus yace masa, “Zo ka gani.”
Nathanaël lui dit: «Peut-il sortir de Nazareth quelque chose de bon?» Philippe lui répondit: «Viens et vois.»
47 Yesu ya ga Natana'ilu yana zuwa wurinsa sai yayi magana game da shi, “Duba, Ba-Isra'ile na hakika wanda babu yaudara a cikinsa.”
Jésus voyant venir Nathanaël, dit en parlant de lui: «Voici un vrai Israélite, un homme sans détour.»
48 Natana'ilu yace masa, “Ta yaya ka san ni?” Sai Yesu ya amsa masa yace, “Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'adda kake a gindin baure, na gan ka.”
— «D'où me connais-tu?» lui dit Nathanaël. Jésus lui répondit: «Avant que Philippe t'appelât, je t'ai vu sous le figuier.»
49 Natana'ilu ya amsa, “Rabbi, Kai Dan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!”
— «Maître, lui repartit Nathanaël, tu es le Fils de Dieu, tu es le roi d'Israël.»
50 Yesu ya amsa masa yace, “Don na ce maka, 'Na gan ka a gindin Baure', ka gaskanta? Za ka ga abubuwa da suka fi wannan girma.”
Jésus répondit et lui dit: «Parce que je t'ai dit que je t'ai vu sous le figuier, tu crois! Tu verras de plus grandes choses que celles-là.»
51 Sai yace, 'Hakika, hakika ina gaya maka, zaka ga sammai a bude, mala'ikun Allah kuma suna hawa suna sauka akan Dan Mutum.”
Et il ajouta: «En vérité, en vérité, je vous le dis, vous verrez désormais le ciel ouvert, et les anges de Dieu monter et descendre sur le Fils de l'homme.

< Yohanna 1 >