< Yohanna 3 >

1 akwai wani Bafarise da ake kira Nikodimu, shugaba a cikin Yahudawa.
Il y avait, parmi les pharisiens, un homme qui s'appelait Nicodème: c'était un sénateur juif.
2 Wannan mutum ya zo wurin Yesu da dare ya ce masa, “Rabbi, mun sani cewa kai malami ne da kazo daga wurin Allah, gama ba wanda zai iya yin wadannan alamu da kake yi sai idan Allah na tare da shi.”
Il vint de nuit trouver Jésus, et lui dit: «Maître, nous savons que tu es un docteur venu de Dieu, car nul ne peut faire les miracles que tu fais, si Dieu n'est avec lui...»
3 Yesu ya amsa masa, “Hakika, hakika, idan ba a sake haifuwar mutum ba, ba zai iya ganin mulkin Allah ba.”
Jésus répondit et lui dit: «En vérité, en vérité, je te le dis, si l’on ne naît à nouveau, on ne peut voir le royaume de Dieu.»
4 Nikodimu ya ce masa, “Yaya za a sake haifuwar mutum bayan ya tsufa? Ba zai iya sake shiga cikin cikin uwarsa kuma a haife shi ba, zai iya?”
Nicodème lui dit: «Comment un homme qui est vieux, peut-il naître? peut-il rentrer dans le sein de sa mère et naître?»
5 Yesu ya amsa, “Hakika, hakika, idan ba a haifi mutum da ruwa da kuma Ruhu ba, ba zai iya shiga cikin mulkin Allah ba.
Jésus répondit: «En vérité, en vérité, je te dis que si l’on ne naît, d'eau et d'esprit, on ne peut entrer dans le royaume de Dieu:
6 Abin da aka haifa ta wurin jiki, jiki ne, kuma abin da aka haifa ta wurin Ruhu, Ruhu ne.
ce qui est né de la chair est chair, et ce qui est né de l'esprit est esprit...
7 Kada ka yi mamaki don na ce maka, 'dole a maya haifuwar ka.'
Ne t'étonne point de ce que je t'ai dit qu'il vous faut naître à nouveau.
8 Iska takan hura duk inda ta ga dama. Ka kan ji motsin ta, amma ba ka san inda ta fito ko inda za ta tafi ba. Haka duk wanda aka haifa daga Ruhu.”
Le vent souffle où il veut, et tu en entends le bruit; mais tu ne sais d'où il vient ni où il va; ainsi en est-il de tout homme qui est né de l'esprit.»
9 Nikodimu ya amsa yace masa, “Yaya wannan zai yiwu?”
Nicodème lui dit: «Comment cela peut-il se faire?»
10 Yesu ya amsa yace masa, “Kai malami ne a Israila amma ba ka san wadannan al'amura ba?
Jésus lui répondit: «Tu es le docteur d'Israël, et tu ne sais pas ces choses!
11 Hakika, hakika, ina gaya maka, muna fadin abubuwan da muka sani, kuma muna shaida abubuwan da muka gani. Duk da haka ba ku karbi shaidar mu ba.
En vérité, en vérité, je te dis que nous disons ce que nous savons, et que nous rendons témoignage de ce que nous avons vu; mais vous ne recevez pas notre témoignage.
12 Idan na gaya maka abubuwan da ke na duniya amma baka gaskata ba, to yaya zaka gaskata idan na gaya maka abubuwa na sama?
Si, quand je vous parle des choses terrestres, vous ne croyez pas, comment croirez-vous quand je vous parlerai des choses célestes?
13 Babu wanda ya taba hawa zuwa sama sai dai shi wanda ya sauko daga sama: wato Dan Mutum.
Nul n'est monté au ciel, que celui qui est descendu du ciel, le Fils de l'homme qui était dans le ciel;
14 Kamar yadda Musa ya ta da maciji a jeji, haka ma dole a ta da Dan Mutum
et, comme Moïse éleva le serpent dans le désert, il faut de même que le Fils de l’homme soit élevé,
15 domin dukan wadanda suka bada gaskiya gareshi su sami rai na har abada. (aiōnios g166)
afin que quiconque croit en lui ait la vie éternelle.» (aiōnios g166)
16 Gama Allah ya kaunaci duniya sosai, har ya ba da makadaicin Dansa, domin duk wanda ya bada gaskiya gareshi, kada ya mutu, amma ya samu rai madawwami. (aiōnios g166)
En effet, Dieu a tant aimé le monde, qu'il a donné son Fils unique, afin que quiconque croit en lui ne périsse point, mais qu'il ait la vie éternelle. (aiōnios g166)
17 Gama Allah bai aiko da Dansa cikin duniya domin ya kayar da duniya ba, amma domin a ceci duniya ta wurin sa.
Dieu n'a pas envoyé son Fils dans le monde, pour juger le monde, mais afin que le monde soit sauvé par lui.
18 Duk wanda ya bada gaskiya gare shi ba a kayar da shi ba, amma duk wanda bai bada gaskiya gare shi ba an riga an kayar da shi, domin bai bada gaskiya ga sunan wannan da shi kadai ne Dan Allah ba.
Celui qui croit en lui n'est point jugé, mais celui qui ne croit pas en lui est déjà jugé, parce qu'il n'a pas cru au nom du Fils unique de Dieu;
19 Wannan shi ne dalilin shari'ar, domin haske ya zo duniya, amma mutane suka kaunaci duhu fiye da hasken, sabili da ayyukan su na mugunta ne.
et voici ce jugement: la lumière est venue dans le monde, mais les hommes ont mieux aimé les ténèbres que la lumière, parce que leurs oeuvres étaient mauvaises.
20 Domin duk wanda ke mugayen ayyuka ya ki haske, kuma baya zuwa wurin hasken domin kada ayyukansa su bayyanu.
Car tout homme qui fait le mal, hait la lumière, et il ne s'approche point de la lumière, de peur que la méchanceté de ses oeuvres ne soit mise en évidence;
21 Sai dai duk wanda yake aikata gaskiya kan zo wurin hasken domin ayyukansa, da ake aiwatarwa ga Allah, su bayyanu.
mais celui qui pratique la vérité, s'approche de la lumière, afin que ses oeuvres soient manifestées, parce qu'elles sont faites en Dieu.
22 Bayan wannan, Yesu da almajiransa suka tafi kasar Yahudiya. A can ya dan zauna tare da su ya kuma yi Baftisma.
Après cela, Jésus se rendit dans les campagnes de la Judée avec ses disciples; il y séjourna avec eux, et il baptisait.
23 Yahaya ma yana Baftisma a Ainon kusa da Salim domin akwai ruwa da yawa a can. Mutane na zuwa wurin sa yana masu Baftisma,
Jean baptisait aussi à Énon, près de Salim, parce qu'il y avait là beaucoup d'eau; et l’on venait s'y faire baptiser,
24 domin a lokacin ba a jefa Yahaya a kurkuku ba tukuna.
car Jean n'avait pas encore été mis en prison.
25 Sai gardama ta taso tsakanin almajiran Yahaya da wani Bayahude akan al'adun tsarkakewa.
Il s'éleva donc une dispute entre les disciples de Jean et un Juif au sujet du baptême.
26 Suka je wurin Yahaya suka ce, “Rabbi, wanda yake tare da kai a dayan ketaren kogin Urdun, kuma ka shaida shi, duba, yana baftisma, kuma mutane duka suna zuwa wurin sa.”
Les disciples vinrent vers Jean, et lui dirent: «Maître, celui qui était avec toi au delà du Jourdain, et à qui tu as rendu témoignage, le voilà qui baptise; et tout le monde va vers lui.»
27 Yahaya ya amsa, “Mutum ba zai iya samun wani abu ba sai an ba shi daga sama.
Jean répondit et dit: «Un homme ne peut rien recevoir, s'il ne lui a été donné du ciel.
28 Ku da kanku zaku shaida na ce, 'Ba ni ne Almasihu ba' amma amaimakon haka, 'an aiko ni kafin shi.'
Vous m'êtes vous-mêmes témoins, que j'ai dit: «Je ne suis pas le Messie, mais j'ai été envoyé devant lui.»
29 Amaryar ta angon ce. Yanzu abokin angon, wanda ke tsaye yana saurarensa, yana murna sosai saboda muryan angon. Murnata ta cika domin wannan.
Celui qui a l'épouse est l'époux; mais l'ami de l'époux, qui se tient là et qui l'écoute, est ravi de joie d'entendre la voix de l'époux: cette joie donc est la mienne, et elle est parfaite.
30 Dole shi ya karu, ni kuma in ragu.
Il faut qu'il croisse et que je diminue.»
31 Shi wanda ya fito daga sama ya fi kowa. Shi Wanda ya zo daga duniya, na duniya ne, kuma game da duniya yake magana. Shi wanda ya fito daga sama yana saman kowa.
Celui qui vient d'en haut est au-dessus de tous. Celui qui vient de la terre est de la terre, et il parle comme étant de la terre; celui qui vient du ciel est au-dessus de tous,
32 Ya shaida abubuwan da ya ji ya kuma gani, amma babu wanda ya karbi shaidarsa.
et il rend témoignage de ce qu'il a vu et entendu; mais nul ne reçoit son témoignage.
33 Duk wanda ya karbi shaidarsa ya tabbatar Allah gaskiya ne.
Celui qui reçoit son témoignage certifie que Dieu est vrai;
34 Domin duk wanda Allah ya aika kan yi magana da kalmomin Allah. Domin bai bada Ruhun da ma'auni ba.
car celui que Dieu a envoyé profère les paroles de Dieu, parce que Dieu ne lui donne pas son Esprit par mesure.
35 Uban ya kaunaci Dan, ya kuma ba da dukan komai a hanunsa.
Le Père aime le Fils et a remis toutes choses entre ses mains.
36 Shi wanda ya bada gaskiya ga Dan ya na da rai madawwami, amma wanda ya ki yiwa Dan biyayya ba zai ga rai ba, amma fushin Allah na kansa. (aiōnios g166)
Celui qui croit au Fils a la vie éternelle; celui qui ne croit point au Fils ne verra point la vie, mais la colère de Dieu demeure sur lui. (aiōnios g166)

< Yohanna 3 >