< Zabura 69 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
For the Chief Musician. To the tune of “Lilies.” By David. Save me, God, for the waters have come up to my neck!
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
I sink in deep mire, where there is no foothold. I have come into deep waters, where the floods overflow me.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
I am weary with my crying. My throat is dry. My eyes fail looking for my God.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
Those who hate me without a cause are more than the hairs of my head. Those who want to cut me off, being my enemies wrongfully, are mighty. I have to restore what I didn’t take away.
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
God, you know my foolishness. My sins aren’t hidden from you.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Don’t let those who wait for you be shamed through me, Lord Yahweh of Armies. Don’t let those who seek you be brought to dishonor through me, God of Israel.
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Because for your sake, I have borne reproach. Shame has covered my face.
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
I have become a stranger to my brothers, an alien to my mother’s children.
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
For the zeal of your house consumes me. The reproaches of those who reproach you have fallen on me.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
When I wept and I fasted, that was to my reproach.
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
When I made sackcloth my clothing, I became a byword to them.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
Those who sit in the gate talk about me. I am the song of the drunkards.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
But as for me, my prayer is to you, Yahweh, in an acceptable time. God, in the abundance of your loving kindness, answer me in the truth of your salvation.
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Deliver me out of the mire, and don’t let me sink. Let me be delivered from those who hate me, and out of the deep waters.
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
Don’t let the flood waters overwhelm me, neither let the deep swallow me up. Don’t let the pit shut its mouth on me.
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Answer me, Yahweh, for your loving kindness is good. According to the multitude of your tender mercies, turn to me.
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
Don’t hide your face from your servant, for I am in distress. Answer me speedily!
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Draw near to my soul and redeem it. Ransom me because of my enemies.
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
You know my reproach, my shame, and my dishonor. My adversaries are all before you.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
Reproach has broken my heart, and I am full of heaviness. I looked for some to take pity, but there was none; for comforters, but I found none.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
They also gave me poison for my food. In my thirst, they gave me vinegar to drink.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
Let their table before them become a snare. May it become a retribution and a trap.
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
Let their eyes be darkened, so that they can’t see. Let their backs be continually bent.
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Pour out your indignation on them. Let the fierceness of your anger overtake them.
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
Let their habitation be desolate. Let no one dwell in their tents.
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
For they persecute him whom you have wounded. They tell of the sorrow of those whom you have hurt.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Charge them with crime upon crime. Don’t let them come into your righteousness.
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Let them be blotted out of the book of life, and not be written with the righteous.
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
But I am in pain and distress. Let your salvation, God, protect me.
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
I will praise the name of God with a song, and will magnify him with thanksgiving.
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
It will please Yahweh better than an ox, or a bull that has horns and hoofs.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
The humble have seen it, and are glad. You who seek after God, let your heart live.
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
For Yahweh hears the needy, and doesn’t despise his captive people.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Let heaven and earth praise him; the seas, and everything that moves therein!
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
For God will save Zion, and build the cities of Judah. They shall settle there, and own it.
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
The children also of his servants shall inherit it. Those who love his name shall dwell therein.

< Zabura 69 >