< Zabura 68 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
For the Chief Musician. A Psalm by David. A song. Let God arise! Let his enemies be scattered! Let them who hate him also flee before him.
2 Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
As smoke is driven away, so drive them away. As wax melts before the fire, so let the wicked perish at the presence of God.
3 Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
But let the righteous be glad. Let them rejoice before God. Yes, let them rejoice with gladness.
4 Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
Sing to God! Sing praises to his name! Extol him who rides on the clouds: to Yah, his name! Rejoice before him!
5 Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
A father of the fatherless, and a defender of the widows, is God in his holy habitation.
6 Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
God sets the lonely in families. He brings out the prisoners with singing, but the rebellious dwell in a sun-scorched land.
7 Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
God, when you went out before your people, when you marched through the wilderness... (Selah)
8 duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
The earth trembled. The sky also poured down rain at the presence of the God of Sinai— at the presence of God, the God of Israel.
9 Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
You, God, sent a plentiful rain. You confirmed your inheritance when it was weary.
10 Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
Your congregation lived therein. You, God, prepared your goodness for the poor.
11 Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
The Lord announced the word. The ones who proclaim it are a great company.
12 “Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
“Kings of armies flee! They flee!” She who waits at home divides the plunder,
13 Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
while you sleep among the camp fires, the wings of a dove sheathed with silver, her feathers with shining gold.
14 Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
When the Almighty scattered kings in her, it snowed on Zalmon.
15 Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
The mountains of Bashan are majestic mountains. The mountains of Bashan are rugged.
16 Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
Why do you look in envy, you rugged mountains, at the mountain where God chooses to reign? Yes, Yahweh will dwell there forever.
17 Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
The chariots of God are tens of thousands and thousands of thousands. The Lord is among them, from Sinai, into the sanctuary.
18 Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
You have ascended on high. You have led away captives. You have received gifts among people, yes, among the rebellious also, that Yah God might dwell there.
19 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
Blessed be the Lord, who daily bears our burdens, even the God who is our salvation. (Selah)
20 Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
God is to us a God of deliverance. To Yahweh, the Lord, belongs escape from death.
21 Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
But God will strike through the head of his enemies, the hairy scalp of such a one as still continues in his guiltiness.
22 Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
The Lord said, “I will bring you again from Bashan, I will bring you again from the depths of the sea,
23 don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
that you may crush them, dipping your foot in blood, that the tongues of your dogs may have their portion from your enemies.”
24 Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
They have seen your processions, God, even the processions of my God, my King, into the sanctuary.
25 A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
The singers went before, the minstrels followed after, among the ladies playing with tambourines,
26 Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
“Bless God in the congregations, even the Lord in the assembly of Israel!”
27 Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
There is little Benjamin, their ruler, the princes of Judah, their council, the princes of Zebulun, and the princes of Naphtali.
28 Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
Your God has commanded your strength. Strengthen, God, that which you have done for us.
29 Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
Because of your temple at Jerusalem, kings shall bring presents to you.
30 Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
Rebuke the wild animal of the reeds, the multitude of the bulls with the calves of the peoples. Trample under foot the bars of silver. Scatter the nations who delight in war.
31 Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
Princes shall come out of Egypt. Ethiopia shall hurry to stretch out her hands to God.
32 Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
Sing to God, you kingdoms of the earth! Sing praises to the Lord— (Selah)
33 gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
to him who rides on the heaven of heavens, which are of old; behold, he utters his voice, a mighty voice.
34 Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
Ascribe strength to God! His excellency is over Israel, his strength is in the skies.
35 Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!
You are awesome, God, in your sanctuaries. The God of Israel gives strength and power to his people. Praise be to God!

< Zabura 68 >