< Zabura 19 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sammai suna shelar ɗaukakar Allah; sararin sama suna furta aikin hannuwansa.
To the chief Musician, A Psalm of David. The heavens declare the glory of God; and the firmament sheweth his handywork.
2 Kowace rana tana yin jawabi; kowane dare yana nuna sani.
Day unto day uttereth speech, and night unto night sheweth knowledge.
3 Ba magana, ba kalmar da aka hurta, ba wani amon da aka ji daga gare su.
[There is] no speech nor language, [where] their voice is not heard.
4 Duk da haka muryarsu tana kaiwa ga dukan duniya, kalmominsu zuwa iyakokin duniya. A sammai Allah ya kafa tenti domin rana,
Their line is gone out through all the earth, and their words to the end of the world. In them hath he set a tabernacle for the sun,
5 wanda yake kamar ango mai fitowa daga rumfarsa, kamar gwani ɗan wasan da yake farin ciki yă yi tsere.
Which [is] as a bridegroom coming out of his chamber, [and] rejoiceth as a strong man to run a race.
6 Takan taso daga ƙarshen sammai ta kewaye zuwa wancan; babu abin da yake ɓuya wa zafinta.
His going forth [is] from the end of the heaven, and his circuit unto the ends of it: and there is nothing hid from the heat thereof.
7 Dokar Ubangiji cikakkiya ce, takan wartsakar da rai. Farillan Ubangiji abin dogara ne, suna mai da hikima da sauƙi.
The law of the LORD [is] perfect, converting the soul: the testimony of the LORD [is] sure, making wise the simple.
8 Ƙa’idodin Ubangiji daidai ne, suna ba da farin ciki ga zuciya. Umarnan Ubangiji haske ne suna ba da haske ga idanu.
The statutes of the LORD [are] right, rejoicing the heart: the commandment of the LORD [is] pure, enlightening the eyes.
9 Tsoron Ubangiji yakan kawo tsabtar zuciya, zai kasance har abada. Farillan Ubangiji tabbatattu ne, kuma gaba ɗaya masu adalci ne.
The fear of the LORD [is] clean, enduring for ever: the judgments of the LORD [are] true [and] righteous altogether.
10 Sun fi zinariya daraja, fiye da zalla zinariya nesa; sun fi zuma zaƙi fiye da zuma daga kaki.
More to be desired [are they] than gold, yea, than much fine gold: sweeter also than honey and the honeycomb.
11 Ta wurinsu ana gargaɗe bawanka; a kiyaye su akwai lada mai girma.
Moreover by them is thy servant warned: [and] in keeping of them [there is] great reward.
12 Wane ne zai iya rabe kurakuransa? Ya gafarta ɓoyayyun laifofinsa.
Who can understand [his] errors? cleanse thou me from secret [faults].
13 Ka kiyaye bawanka daga zunubin ganganci; kada ka bari su yi mulki a kaina. Ta haka zan zama marar laifi; marar laifi na babban tawaye.
Keep back thy servant also from presumptuous [sins; ] let them not have dominion over me: then shall I be upright, and I shall be innocent from the great transgression.
14 Bari kalmomin bakina da tunanin zuciyata su zama abin gamsuwa a gabanka, Ya Ubangiji, Dutsena da Mai fansata.
Let the words of my mouth, and the meditation of my heart, be acceptable in thy sight, O LORD, my strength, and my redeemer.

< Zabura 19 >